Sashe 24
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Inna Ade tace "amma Baban biyu bana jin irin mutanen da zasu yi mana haka ne, in sun fasa ma bana jin zasu ce a biya su kayan su, kuma ma ai ba rokonsa suka yi ba" yace "to kaddara ma ba zasu ce a biya su ba. Yanzun in kika bawa wannan yarinyar" ya fada yana nuna Ruqayyah data rungume kwalin waya a kirjinta idonta ya kada yayi jawur "wannan wayar, kika kuma bata sannan leshin ta saka, idan ba'a yi auren ba ta yaya zata cigaba da girmama wannan" ya nuna wayar hannunsa "da kuma wannan" ya nuna kodaddiyar atamfar jikin Inna.
Ruqayyah ta maimaita "ba zai ce ya fasa ba" yayo kanta "in kika kara Magana sai na kakkarya ki a gurin nan na zubar da kasusuwanki" Inna Ade ta shiga tsakani tana bashi hakuri "dan Allah kar ka taba ta Baban biyu, dan girman Allah kar ka dake ta" ya juyo kanta "ki tattara kayan nan ki nemi gidan wata kawarki ki kai a ajiye, duk ranar da akayi auren sai a dauko su a basu"
Ruqayyah ta durkusa "Baba dan girman Allah kar ka karbe kayan nan, dan Allah ka bar mana abin mu, na tuba Baba wallahi na daina duk abinda baka so, dan Allah ka bar min kayana Baba" Inna Ade ta taya ta roko "ko ba zaka bar musu wayar ba ka bar musu kayan suma su samu suyi kwalliya, ba rokon su suka yi ba kyauta ce suka basu kuma shima Hassan din ai zai so ya ganta fes fes, gashi yan'uwansa suna zuwa, dan Allah Baban biyu kayi hakuri ka bar musu" yace "wato da saka hannunki kenan ko? Shikenan, su rike kaya amma babu ruwana"
Ya juya ya saka takalmi ya fita, Inna Ade tasan fushi yayi amma kuma bata son abinda zai kara hargitsa tsakanin sa da Ruqayyah, kuma ita tana ganin babu laifi in an karbi kayan.
Bayan ya tafi suka zauna suna dudduba kayan duk da dai duk jikinsu a sanyaye yake da fadan da Baba yayi, banda Ruqayyah da take ta lissafin wanne tailor ne yafi kowa iya dinki a kaduna? Gurinsa zata kai dinki. Ta dora wata doguwar riga kenan a cinyarta sai wata envelope ta fado daga cikinta, ta duba ta lura babu wanda ya gani sai ta zare ta ta saka a rigar ta. Tasan kudi ne a ciki, maybe kudin dinki, Bata so Inna Ade ta gani dan in ta gani karba zata yi kuma ba zata bata wani abin kirki ba kamar yadda wancan dubu ashirin din da Hassan ya ajiye musu duk Baba aka bawa ya siyo musu kayan abinci.
Bayan sun gama suka tattara kayan suka mayar ,inna tace sai da safe sai su dauki wanda zasuyi amfani dashi su kai gurin dinki "sai dai kuma sai an nemo kudin dinkin" inji Inna.
A daki bayan sun kwanta ita da Sumayya ne tace "Sumayya, kina ganin Hassan zai iya cewa ya fasa aure na?" Sumayya ta juyo tana kallonta tace "me yasa kike tambaya?" Tace "kawai dai. Baba baya son auren nan. Bansan me zai faru ba, ina jin tsoro" Sumayya tace "ki ji tsoron Allah. Kiyi ta addu'a" suka yi shiru kowa yana tunanin sa, har bacci ya fara daukan Sumayya sai Ruqayyah ta kuma cewa "Sumayya? Ya kika ga Hussain dazu?
Sumayya tace "ya kuwa na ganshi? He is okay" Ruqayyah tace "ba haka nake nufi ba, ina nufin yafi Hassan haduwa ko?" Sumayya ta mike zaune tana kallon ta tace "no......bai fishi haduwa ba, kar ma ki sake wannan tunanin dan Allah" Ruqayyah ta mike itama zaunen tace "ba wani abun nace ba ai, kawai dai kamar ya fishi....." Sumayya tace "gayu? Ko kuma bagu da mota da kaya masu kyau da sababbin kudi" Ruqayyah ta fadi abinda yake ranta "ya fishi kyau" Sumayya ta runtse idonta tana jin zafin abinda yar uwarta take neman yiwa Hassan tace "bai fishi kyau ba. Ya dai fishi fari" Ruqayyah tace "ya fishi fari ko kuma dai kice shi fari ne shi kuma baƙi?" Sumayya tace "fari da baƙi duk halittar Allah ce, amma ni personally ma nafi son bakin mutum akan farin. Sannan ni bayan kalar fata banga wani banbancin halitta a tsakanin su ba dan kamannin su har abin mamaki ne dashi, hanci, baki, ido, shape din fuska, tsaho kirar jikinsu duk iri daya. Kuma Hassan yafi kama da matured kamilallen mutum shi kuma Hussain yafi kama da ladies man, ni in nice da zabi zan zabi Hassan sau goma kafin in zabi Hussain sau daya" ta koma ta kwanta tare da juya wa Ruqayyah baya cikin jin zafin maganar ta. Tana jin Ruqayyah tayi addu'a sannan ta kwanta, sai kuma tace "har dimple ne dashi"
Sumayya ta kuma juyowa cikin fushi tace "gaya min gaskiya Ruqayyah, zaki juyawa Hassan baya ne ki ce hussainin sa kike so kuma? Kina ganin hakan mai yiyuwa ne?" Ruqayyah tace "Ni haka kika ji nace miki? Dan Hussain ya fishi kyau ai ba wai ya fishi komai ba ne ba, Hassan shine babba, sannan shine mai kudin," Sumayya tace "wrong. Wannan ba shine dalilin da ya kamata ki fada ba na zaben Hassan, ya kamata ki zabi Hassan ne saboda Hassan shi yake sonki ba Hussain ba, Hassan shi ya kamata ki so ba Hussain ba" Ruqayyah tace "shi nake so ɗin ai. Amma dai ai ba haka aka so ba kanin miji yafi miji kyau".
Sumayya ta runtse idonta tana hana zuciyarta rinjayar ta gurin juyowa ta rufe Ruqayyah da duka. Sai taji cewa ta fahimci menene problem din Ruqayyah, ba wai bakar zuciya ko fada, ko son abin duniya ne da ita ba. A'a rashin godiyar Allah ne da ita. In taga abu zata kwallafa ranta akan tana sonsa amma da zarar ta samu to kuwa ya zama banza abinda ya fishi kuma take hari. And now she have her eyes on Hussain, and Sumayya knows that abinda yasa kawai ba zata rabu da Hassan ta makale wa Hussain ba shine saboda kuɗi, saboda tana son kudin Hassan din. Sai Sumayya taji tana tausayin Hassan. Tana kuma tausayin Ruqayyah saboda karin maganar hausawa da suke cewa "duk wanda bai gode Allah ba to kuwa tabbas zai gode wa azabar Allah".
Washegari da sassafe Baba ya fita yace musu ya tafi gurin interview, suka yi masa fatan alkhairi ya tafi.
A bangaren su Hassan kuwa suma da sassafe suka fita. Hassan ya kai Hussain airport ya tafi China zai siyo injinan da wancan karon bai samu damar siyowa ba, dama kudin su ne ya hada da kudin da yake account dinsa ya bayar kudin ransom din Hassan, yanzu kuwa tunda alhamdulillah kuɗin sun dawo shine zai koma ya siyo duk da cewa yasan ba zai same su a wadancan price din ba.
Daga airport shi kuma Hassan gurin interview ya zarce, dan yasan cewa yanzu mutane suna nan sun taru suna jiransa shi kuma baya son ya bar mutane suna jiran sa.
Baba yana zaune akan layi tare da sauran mutane, wani ya fara mita "haka kawai bayan mun riga munzo munyi interview din nan, sai da akayi wata guda kuma sannan sai a dawo a sake cewa muzo mu kuma yin wata? Shikenan yanzu a duniya masu kudi basa tausayin talakawa? Wannan ai zalunci ne, gashi kuma mum zo din sannan an shanya mu a waje kamar wasu kayan wanki".
Baba yace "haba bawan Allah, ba ka san abinda ya samu mutumin nan bane ba? Masu garkuwa da mutane ne fa suka sace shi da kyar ya tsira da ransa" wasu a gurin suka fara jajanta abin wasu kuma suka ce "ina ruwan mu to mu, mu muka sace shi ko kuma mu aka bawa kudin diyyar? Ai irin wannan abin da masu kudi suke yi wa talakawa yana daya daga cikin abinda yake jawo musu irin wancan balain"
Sai Baba yayi shiru kawai ya barsu, dan wadansu mutanen ko yaya ka kai da bayani ba zasu bude kwakwalwar su ba ballantana su fahimce ka. A lokacin ne Hassan ya shigo gurin da saurinsa, Baba ya lura da yadda yake amsa gaisuwar mutane cike da kulawa sannan ya dan bada hakurin jiransa da akayi sai kuma ya shige ciki. Sai Baba yaji dadi a ransa, yaji yana alfahari da shi yana kuma kara saka ran ya zamo surikin sa dan ya yarda dashi, sai dai ita yar tasa ce bai yarda da ita ba.
Akayi ta kira ana shiga ana fitowa har aka zo kan Baba. Ya shiga da sallamar sa. Hassan ya amsa tare da dago kai, suna hada ido da Baba sai ya mike. "A'a, Baba, sannu da zuwa." Ya fada yana shafa kai, Baba ya zauna sannan shima ya zauna yana gaisheshi sannan yace "Baba ai da an kira ni ni sai inzo gida ba sai anzo nan ba" Baba yace "a'a, ai ba wani abin bane ba, maganar aikin nan ce ta kawo ni an kira mu ance mu sake dawowa za'a sake gwada mu" Hassan ya danyi shiru yana tunani sannan yace "wai wannan aikin dama kaima kazo wancan watan?"
Baba yayi murmushi yace "nazo mana, ai ba zaka gane ba tunda mutanen da yawa" Hassan yayi shiru yana tunani, shi dai ba zai iya hana Baba aikin nan ba ba kuma zai iya bashi ba. Aiyukan na labourers, messengers da kuma na masu gadi ne, ba zai iya saka Baba aiki ba, ba zai iya aikensa ba ba kuma zai iya kullum yana bude masa kofa in zai shigo ba. A matsayin sa na surukinsa hakan bai dace ba.
Ya gyara zama yace "Baba, yanzu misali in aka samu wani kasuwanci haka aka baka, zaka iya hakura da aikin nan?" Baba yace "to Hassan, ni dai ban taba yin kasuwanci ba, ni abinda na sani shine aikin karfi shi nake yi nake ciyar da iyali na har yanzu. Dan haka ba lallai ne in na fara kasuwancin ya dore ba tunda ban san kan abun ba, aikin dai shine, nasan abinda kake tunani kuma ina so ka cire komai daga zuciyarka ka gwada ni idan naci ka bani, wannan shine taimako mafi girman da zaka yi min".
Ruqayyah ta maimaita "ba zai ce ya fasa ba" yayo kanta "in kika kara Magana sai na kakkarya ki a gurin nan na zubar da kasusuwanki" Inna Ade ta shiga tsakani tana bashi hakuri "dan Allah kar ka taba ta Baban biyu, dan girman Allah kar ka dake ta" ya juyo kanta "ki tattara kayan nan ki nemi gidan wata kawarki ki kai a ajiye, duk ranar da akayi auren sai a dauko su a basu"
Ruqayyah ta durkusa "Baba dan girman Allah kar ka karbe kayan nan, dan Allah ka bar mana abin mu, na tuba Baba wallahi na daina duk abinda baka so, dan Allah ka bar min kayana Baba" Inna Ade ta taya ta roko "ko ba zaka bar musu wayar ba ka bar musu kayan suma su samu suyi kwalliya, ba rokon su suka yi ba kyauta ce suka basu kuma shima Hassan din ai zai so ya ganta fes fes, gashi yan'uwansa suna zuwa, dan Allah Baban biyu kayi hakuri ka bar musu" yace "wato da saka hannunki kenan ko? Shikenan, su rike kaya amma babu ruwana"
Ya juya ya saka takalmi ya fita, Inna Ade tasan fushi yayi amma kuma bata son abinda zai kara hargitsa tsakanin sa da Ruqayyah, kuma ita tana ganin babu laifi in an karbi kayan.
Bayan ya tafi suka zauna suna dudduba kayan duk da dai duk jikinsu a sanyaye yake da fadan da Baba yayi, banda Ruqayyah da take ta lissafin wanne tailor ne yafi kowa iya dinki a kaduna? Gurinsa zata kai dinki. Ta dora wata doguwar riga kenan a cinyarta sai wata envelope ta fado daga cikinta, ta duba ta lura babu wanda ya gani sai ta zare ta ta saka a rigar ta. Tasan kudi ne a ciki, maybe kudin dinki, Bata so Inna Ade ta gani dan in ta gani karba zata yi kuma ba zata bata wani abin kirki ba kamar yadda wancan dubu ashirin din da Hassan ya ajiye musu duk Baba aka bawa ya siyo musu kayan abinci.
Bayan sun gama suka tattara kayan suka mayar ,inna tace sai da safe sai su dauki wanda zasuyi amfani dashi su kai gurin dinki "sai dai kuma sai an nemo kudin dinkin" inji Inna.
A daki bayan sun kwanta ita da Sumayya ne tace "Sumayya, kina ganin Hassan zai iya cewa ya fasa aure na?" Sumayya ta juyo tana kallonta tace "me yasa kike tambaya?" Tace "kawai dai. Baba baya son auren nan. Bansan me zai faru ba, ina jin tsoro" Sumayya tace "ki ji tsoron Allah. Kiyi ta addu'a" suka yi shiru kowa yana tunanin sa, har bacci ya fara daukan Sumayya sai Ruqayyah ta kuma cewa "Sumayya? Ya kika ga Hussain dazu?
Sumayya tace "ya kuwa na ganshi? He is okay" Ruqayyah tace "ba haka nake nufi ba, ina nufin yafi Hassan haduwa ko?" Sumayya ta mike zaune tana kallon ta tace "no......bai fishi haduwa ba, kar ma ki sake wannan tunanin dan Allah" Ruqayyah ta mike itama zaunen tace "ba wani abun nace ba ai, kawai dai kamar ya fishi....." Sumayya tace "gayu? Ko kuma bagu da mota da kaya masu kyau da sababbin kudi" Ruqayyah ta fadi abinda yake ranta "ya fishi kyau" Sumayya ta runtse idonta tana jin zafin abinda yar uwarta take neman yiwa Hassan tace "bai fishi kyau ba. Ya dai fishi fari" Ruqayyah tace "ya fishi fari ko kuma dai kice shi fari ne shi kuma baƙi?" Sumayya tace "fari da baƙi duk halittar Allah ce, amma ni personally ma nafi son bakin mutum akan farin. Sannan ni bayan kalar fata banga wani banbancin halitta a tsakanin su ba dan kamannin su har abin mamaki ne dashi, hanci, baki, ido, shape din fuska, tsaho kirar jikinsu duk iri daya. Kuma Hassan yafi kama da matured kamilallen mutum shi kuma Hussain yafi kama da ladies man, ni in nice da zabi zan zabi Hassan sau goma kafin in zabi Hussain sau daya" ta koma ta kwanta tare da juya wa Ruqayyah baya cikin jin zafin maganar ta. Tana jin Ruqayyah tayi addu'a sannan ta kwanta, sai kuma tace "har dimple ne dashi"
Sumayya ta kuma juyowa cikin fushi tace "gaya min gaskiya Ruqayyah, zaki juyawa Hassan baya ne ki ce hussainin sa kike so kuma? Kina ganin hakan mai yiyuwa ne?" Ruqayyah tace "Ni haka kika ji nace miki? Dan Hussain ya fishi kyau ai ba wai ya fishi komai ba ne ba, Hassan shine babba, sannan shine mai kudin," Sumayya tace "wrong. Wannan ba shine dalilin da ya kamata ki fada ba na zaben Hassan, ya kamata ki zabi Hassan ne saboda Hassan shi yake sonki ba Hussain ba, Hassan shi ya kamata ki so ba Hussain ba" Ruqayyah tace "shi nake so ɗin ai. Amma dai ai ba haka aka so ba kanin miji yafi miji kyau".
Sumayya ta runtse idonta tana hana zuciyarta rinjayar ta gurin juyowa ta rufe Ruqayyah da duka. Sai taji cewa ta fahimci menene problem din Ruqayyah, ba wai bakar zuciya ko fada, ko son abin duniya ne da ita ba. A'a rashin godiyar Allah ne da ita. In taga abu zata kwallafa ranta akan tana sonsa amma da zarar ta samu to kuwa ya zama banza abinda ya fishi kuma take hari. And now she have her eyes on Hussain, and Sumayya knows that abinda yasa kawai ba zata rabu da Hassan ta makale wa Hussain ba shine saboda kuɗi, saboda tana son kudin Hassan din. Sai Sumayya taji tana tausayin Hassan. Tana kuma tausayin Ruqayyah saboda karin maganar hausawa da suke cewa "duk wanda bai gode Allah ba to kuwa tabbas zai gode wa azabar Allah".
Washegari da sassafe Baba ya fita yace musu ya tafi gurin interview, suka yi masa fatan alkhairi ya tafi.
A bangaren su Hassan kuwa suma da sassafe suka fita. Hassan ya kai Hussain airport ya tafi China zai siyo injinan da wancan karon bai samu damar siyowa ba, dama kudin su ne ya hada da kudin da yake account dinsa ya bayar kudin ransom din Hassan, yanzu kuwa tunda alhamdulillah kuɗin sun dawo shine zai koma ya siyo duk da cewa yasan ba zai same su a wadancan price din ba.
Daga airport shi kuma Hassan gurin interview ya zarce, dan yasan cewa yanzu mutane suna nan sun taru suna jiransa shi kuma baya son ya bar mutane suna jiran sa.
Baba yana zaune akan layi tare da sauran mutane, wani ya fara mita "haka kawai bayan mun riga munzo munyi interview din nan, sai da akayi wata guda kuma sannan sai a dawo a sake cewa muzo mu kuma yin wata? Shikenan yanzu a duniya masu kudi basa tausayin talakawa? Wannan ai zalunci ne, gashi kuma mum zo din sannan an shanya mu a waje kamar wasu kayan wanki".
Baba yace "haba bawan Allah, ba ka san abinda ya samu mutumin nan bane ba? Masu garkuwa da mutane ne fa suka sace shi da kyar ya tsira da ransa" wasu a gurin suka fara jajanta abin wasu kuma suka ce "ina ruwan mu to mu, mu muka sace shi ko kuma mu aka bawa kudin diyyar? Ai irin wannan abin da masu kudi suke yi wa talakawa yana daya daga cikin abinda yake jawo musu irin wancan balain"
Sai Baba yayi shiru kawai ya barsu, dan wadansu mutanen ko yaya ka kai da bayani ba zasu bude kwakwalwar su ba ballantana su fahimce ka. A lokacin ne Hassan ya shigo gurin da saurinsa, Baba ya lura da yadda yake amsa gaisuwar mutane cike da kulawa sannan ya dan bada hakurin jiransa da akayi sai kuma ya shige ciki. Sai Baba yaji dadi a ransa, yaji yana alfahari da shi yana kuma kara saka ran ya zamo surikin sa dan ya yarda dashi, sai dai ita yar tasa ce bai yarda da ita ba.
Akayi ta kira ana shiga ana fitowa har aka zo kan Baba. Ya shiga da sallamar sa. Hassan ya amsa tare da dago kai, suna hada ido da Baba sai ya mike. "A'a, Baba, sannu da zuwa." Ya fada yana shafa kai, Baba ya zauna sannan shima ya zauna yana gaisheshi sannan yace "Baba ai da an kira ni ni sai inzo gida ba sai anzo nan ba" Baba yace "a'a, ai ba wani abin bane ba, maganar aikin nan ce ta kawo ni an kira mu ance mu sake dawowa za'a sake gwada mu" Hassan ya danyi shiru yana tunani sannan yace "wai wannan aikin dama kaima kazo wancan watan?"
Baba yayi murmushi yace "nazo mana, ai ba zaka gane ba tunda mutanen da yawa" Hassan yayi shiru yana tunani, shi dai ba zai iya hana Baba aikin nan ba ba kuma zai iya bashi ba. Aiyukan na labourers, messengers da kuma na masu gadi ne, ba zai iya saka Baba aiki ba, ba zai iya aikensa ba ba kuma zai iya kullum yana bude masa kofa in zai shigo ba. A matsayin sa na surukinsa hakan bai dace ba.
Ya gyara zama yace "Baba, yanzu misali in aka samu wani kasuwanci haka aka baka, zaka iya hakura da aikin nan?" Baba yace "to Hassan, ni dai ban taba yin kasuwanci ba, ni abinda na sani shine aikin karfi shi nake yi nake ciyar da iyali na har yanzu. Dan haka ba lallai ne in na fara kasuwancin ya dore ba tunda ban san kan abun ba, aikin dai shine, nasan abinda kake tunani kuma ina so ka cire komai daga zuciyarka ka gwada ni idan naci ka bani, wannan shine taimako mafi girman da zaka yi min".