Sashe 134
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ta goge hawayen idanunta, duk da cewa tana goge su wadansu suka yi replacing dinsu. Tun sanda ta dawo hayyacin ta, tun sanda ta fara tuna ko wacece ita tare da taimakon Adam, babban abinda take kokarin tunawa shine yadda akayi ta haihu, saboda tana so ta tuno koda fuskar danta ne, ta tuna feeling din nakuda da fitowarsa daga jikinta, ta tuna muryar sa sanda yayi kukan sa na farko amma ta kasa tunawa. Abu na biyu da take kokarin tunawa shine accident din da Adam yace sunyi, menene ya faru, amma abinda kawai take tunawa shine Hussain ya mutu, bata san ya akayi ta sani ba amma ta san ta san Hussain ya mutu kuna shine last abinda ta sani.
"Kiyi kokari ki tuna Fatima" Asma'u ta fada tana shafa kafadar ta, ki tuna a ranar tunda safe me kikayi har zuwa tafiyar ku Abuja, ke da waye a cikin motar? Me ya faru a cikin motar" tayi shiru tana kallon Asma'u, daga alama tunani take yi, sai ta runtse idanunwanta ta yare da dafe kanta da hannunta, ta jima a haka sannan tace "Hussain........ Hussain ya tafi Abuja shi da Hassan da Adam a mota, ni kuma bana son ya tafi, hankali na ya tashi da tafiyar sa. Bayan na lissafa lokacin daya kamata su sauka sai na kira wayarsa amma baya dauka, nayi ta kira amma baya dauka dai hankali na ya tashi, na kira driver nace yazo ya kaini Abuja gurin Hussain, sai muka tafi tare da ........tare da ........matar Hassan, Ruqayyah, tace ita ma tana son taje taga Hassan. Sai muka tafi, mun kusa shiga Abuja sai Hassan ya kira ta yace mata mu koma gasu nan sun gama abinda suke yi zasu taho, muna juya mota sai aka ce min Hussain ya mutu ......" Sai ta rufe fuskarta tana kuka "shikenan abinda na sani"
Umar yace "waye ya gaya miki Hussain ya mutu?" Ta bude idonta da suka juye saboda kuka tace "ban sani ba Yaya Umar, ba zan iya tunawa ba" ya matso kusa da ita "okay, just close your eyes ki tuna sanda kuke zaune a motar, a ina kika zauna?" Ta rufe idonta a tana tunani sannan tace "a baya nake, a side din driver"
Suka kalli juna suna tunawa cewa gawar da aka samu a gaban mota take, yace "good. Ruqayyah fa? A ina take?" Ta kara tunani Tace "a baya itama, tare muke da ita a baya" yace "waye a gaba, akwai mutum a gaba" tayi shiru, her eyes squeezing, tana jinta kamar a cikin motar take, tana jin tension din son taji halin da Hussain yake ciki, tana tuno maganganun su da Ruqayyah da kuma maganar da Ruqayyah suka yi da Hassan a waya da kuma umarnin da Hassan ya bayar, she remembered the driver, da yadda yake kokarin juya motar, and then.....then she remembered her face sanda ta juyo daga seat din gaba tana kallon su da budaddun idanu, she remembered her voice, kamar yanzu take mata maganar tace "Ruqayyah? Ba Hussain dinku ne Hussain Aminu Abdullahi ba? Ya mutu! Yanzu ake fada a twitter wai ya mutu a wani asibiti a abuja!" Fatima ta tuna yadda dan cikinta ya harba da karfi a lokacin. Ta dafe cikin ta tana tsananin missing dinsa.
Ta bude idonta tana kallon Umar, ta gyada kai da sauri tace "na tuna ta, na tuna kamannin ta da komai, kawar Ruqayyah ce tare suka shigo gida sanda zan fita, ita ce a gaba, ita ce ta gaya min Hussain ya mutu" Abubakar yace "zaki iya tunawa ko da akwai ciki a jikin ta?" Ta gyada kanta ba tare da tayi wani tunani ba tace "tsoho ma kuwa".
*************. ************** *****
A yau, bayan shekara hudu da bude estate dinsa na farko, Hassan ya samu nasarar bude na biyu wanda kamar na farkon ya saka masa suna "Hussain Aminu Abdullahi memorial estate phase 2". Kamar na farkon, shima wannan block shida ne sai dai wannan hawa uku ne ba biyu ba, dan haka wannan gidaje goma sha takwas ne a ciki ba sha biyu ba.
Kamar wancan karon, yan uwa da abokan arziki sun taru sosai dan taya shi murnar wannan abin farin cikin. Aunty da family dinta, yaya da jikoki, dan yanzu Hassana da na uku take goyo, Safiyya daya, Khadijah tsohon ciki, Nafisa karami, Sumayya da one year old Abdullahin ta sai Zulaihat da take ta cin yammatancin ta har yanzu. Hassana ta kira Zulaihat "zo ki dauki Ilham ki tafi da ita gurin samarin, in sun baki kin kasa karba ita sai ta karbo ta kawo min mu raba" ta fada tana miƙa mata ikram da take ta tsalala kuka. Zulaihat ta bata rai "kai yaya Hassana! Ni ya zanyi da ita?" Sumayya ta miko mata abdullahi "hada da Abdul, sai ya taya ki renon ta" Abdul ya mika wa Zulaihat hannu yana murna za'a dauke shi. Zulaihat ta bata rai tana dungure masa kai sannan tace "Aunty kin gan su ko?" Aunty tace "ina ruwan Amina? In da kinyi aure ai da ba zasu ke hada ki da rainon yayan su ba. Ki dauki yaran, maybe in samarin ki suka ganki dasu suka fahimci cewa kin iya raino zasu fahimci cewa kin isa aure". Duk suka kwashe da dariya banda Zulaihat, ita ta gaji da wannan sa idon da suke mata suna cewa taki aure, ga Aunty tana tare mata amma tun da taga Sumayya ta haihu sai ta fara matsanta mata itama akan ta fitar da miji ayi mata aure.
Ta tura baki, "babu dan da zan dauka, ai duk kuna da yan aiki ku basu yaran mana su rike muku" ta tashi tana kokarin barin gurin wayar Aunty tayi kara. Ta fito da ita daga jaka tana duba sunan sai ta dafe kanta "innalillahi" Khadijah tace "waye?" Aunty tace "Hajiya Umma ce, wallahi shaf na manta ban aika musu maganar taron nan ba, yanzu haka labari suka ji zata kira tace min ban kyauta ba" Hassana tace "kash, walllahi an manta kuwa, amma kinga wancan ai an aika musu har suka zo ma" Aunty ta dauki wayar da kiran har ya riga ya katse tace "bara in kira in basu hakuri, ban kyauta ba wallahi"
Kafin ta kira sai wani kiran ya sake shigowa, ta tashi tsaye ta dauka yana matsawa inda babu hayaniya ta fara wayarta, bata jima da tashi ba sai sai Hassan yazo, yan samarin sa guda uku suna binsa kamar jela, ya saka hannu ya dauki Abdullahi da tun daya hango shi ya fara tsalle a cinyar maman sa, ya daga shi yana kissing forehead dinsa sannan yace "shine kika zo kika yi zamanki kika barni da mutane ko?" Ta mike tana murmushi tare da pretending hamma, ya harare ta, tayi murmushi "ba laifi na bane Habibi, laifin wannan katon yaron na hannunka ne" sai shima ya ja kujera ya zauna "nima zama zanyi, duk wanda yazo yanzu ke zaki zagaya dashi" ya zauna Sumayya ta fara zuba masa drink sannan ta zubawa boys din suma. Suna ta hada baki gurin bata labarin abubuwan da suka faru a gurin.
Sun jima a haka sannan Aunty ta dawo daga wayar da taje yi. Yanayin fuskarta ya saka kusan gaba ki dayansu suka mike tsaye, Nafisa tace "Aunty mutuwa akayi? Waye ya mutu kuma?" Aunty ta bisu da kallo daya bayan daya sannan tace "ba mutuwa akayi ba, the most strangest thing has happened, Fatima ta dawo gida, bata mutu ba"
Wannan littafin na siyarwa ne idan kika ganshi a wani guri na sata ne, in kina son ki sayi halaliyar ki ki yi min magana ta wannan number din through WhatsApp 08067081020
*Ina masu bukatar hadadu kuma ingantatun turarukan wuta da khumra masu dadin kamshi kuma a farashi me sauki to ga dama tazo muku Awwaba scent nada turarukan wuta humra burners kasko shisa coal dorot stool dilka body milk dadai sauransu masu bukatar na iya nemansu a whats app ko kuma kira ta wannan lambar 08034236800*
*bugu da kari duk wanda ya sayi humra ko turaren wuta a cikin wannan watan akwai kyautar dilka me kyau tafiyaya daga kasar chad wadda zata gyara jiki tay expoliating skin acikin minti 20 kawai ku garzayo dan kwasar garabasa*
*Adress kundila zoo road kano muna tura sako ko ina da iznin Allah*
"Kiyi kokari ki tuna Fatima" Asma'u ta fada tana shafa kafadar ta, ki tuna a ranar tunda safe me kikayi har zuwa tafiyar ku Abuja, ke da waye a cikin motar? Me ya faru a cikin motar" tayi shiru tana kallon Asma'u, daga alama tunani take yi, sai ta runtse idanunwanta ta yare da dafe kanta da hannunta, ta jima a haka sannan tace "Hussain........ Hussain ya tafi Abuja shi da Hassan da Adam a mota, ni kuma bana son ya tafi, hankali na ya tashi da tafiyar sa. Bayan na lissafa lokacin daya kamata su sauka sai na kira wayarsa amma baya dauka, nayi ta kira amma baya dauka dai hankali na ya tashi, na kira driver nace yazo ya kaini Abuja gurin Hussain, sai muka tafi tare da ........tare da ........matar Hassan, Ruqayyah, tace ita ma tana son taje taga Hassan. Sai muka tafi, mun kusa shiga Abuja sai Hassan ya kira ta yace mata mu koma gasu nan sun gama abinda suke yi zasu taho, muna juya mota sai aka ce min Hussain ya mutu ......" Sai ta rufe fuskarta tana kuka "shikenan abinda na sani"
Umar yace "waye ya gaya miki Hussain ya mutu?" Ta bude idonta da suka juye saboda kuka tace "ban sani ba Yaya Umar, ba zan iya tunawa ba" ya matso kusa da ita "okay, just close your eyes ki tuna sanda kuke zaune a motar, a ina kika zauna?" Ta rufe idonta a tana tunani sannan tace "a baya nake, a side din driver"
Suka kalli juna suna tunawa cewa gawar da aka samu a gaban mota take, yace "good. Ruqayyah fa? A ina take?" Ta kara tunani Tace "a baya itama, tare muke da ita a baya" yace "waye a gaba, akwai mutum a gaba" tayi shiru, her eyes squeezing, tana jinta kamar a cikin motar take, tana jin tension din son taji halin da Hussain yake ciki, tana tuno maganganun su da Ruqayyah da kuma maganar da Ruqayyah suka yi da Hassan a waya da kuma umarnin da Hassan ya bayar, she remembered the driver, da yadda yake kokarin juya motar, and then.....then she remembered her face sanda ta juyo daga seat din gaba tana kallon su da budaddun idanu, she remembered her voice, kamar yanzu take mata maganar tace "Ruqayyah? Ba Hussain dinku ne Hussain Aminu Abdullahi ba? Ya mutu! Yanzu ake fada a twitter wai ya mutu a wani asibiti a abuja!" Fatima ta tuna yadda dan cikinta ya harba da karfi a lokacin. Ta dafe cikin ta tana tsananin missing dinsa.
Ta bude idonta tana kallon Umar, ta gyada kai da sauri tace "na tuna ta, na tuna kamannin ta da komai, kawar Ruqayyah ce tare suka shigo gida sanda zan fita, ita ce a gaba, ita ce ta gaya min Hussain ya mutu" Abubakar yace "zaki iya tunawa ko da akwai ciki a jikin ta?" Ta gyada kanta ba tare da tayi wani tunani ba tace "tsoho ma kuwa".
*************. ************** *****
A yau, bayan shekara hudu da bude estate dinsa na farko, Hassan ya samu nasarar bude na biyu wanda kamar na farkon ya saka masa suna "Hussain Aminu Abdullahi memorial estate phase 2". Kamar na farkon, shima wannan block shida ne sai dai wannan hawa uku ne ba biyu ba, dan haka wannan gidaje goma sha takwas ne a ciki ba sha biyu ba.
Kamar wancan karon, yan uwa da abokan arziki sun taru sosai dan taya shi murnar wannan abin farin cikin. Aunty da family dinta, yaya da jikoki, dan yanzu Hassana da na uku take goyo, Safiyya daya, Khadijah tsohon ciki, Nafisa karami, Sumayya da one year old Abdullahin ta sai Zulaihat da take ta cin yammatancin ta har yanzu. Hassana ta kira Zulaihat "zo ki dauki Ilham ki tafi da ita gurin samarin, in sun baki kin kasa karba ita sai ta karbo ta kawo min mu raba" ta fada tana miƙa mata ikram da take ta tsalala kuka. Zulaihat ta bata rai "kai yaya Hassana! Ni ya zanyi da ita?" Sumayya ta miko mata abdullahi "hada da Abdul, sai ya taya ki renon ta" Abdul ya mika wa Zulaihat hannu yana murna za'a dauke shi. Zulaihat ta bata rai tana dungure masa kai sannan tace "Aunty kin gan su ko?" Aunty tace "ina ruwan Amina? In da kinyi aure ai da ba zasu ke hada ki da rainon yayan su ba. Ki dauki yaran, maybe in samarin ki suka ganki dasu suka fahimci cewa kin iya raino zasu fahimci cewa kin isa aure". Duk suka kwashe da dariya banda Zulaihat, ita ta gaji da wannan sa idon da suke mata suna cewa taki aure, ga Aunty tana tare mata amma tun da taga Sumayya ta haihu sai ta fara matsanta mata itama akan ta fitar da miji ayi mata aure.
Ta tura baki, "babu dan da zan dauka, ai duk kuna da yan aiki ku basu yaran mana su rike muku" ta tashi tana kokarin barin gurin wayar Aunty tayi kara. Ta fito da ita daga jaka tana duba sunan sai ta dafe kanta "innalillahi" Khadijah tace "waye?" Aunty tace "Hajiya Umma ce, wallahi shaf na manta ban aika musu maganar taron nan ba, yanzu haka labari suka ji zata kira tace min ban kyauta ba" Hassana tace "kash, walllahi an manta kuwa, amma kinga wancan ai an aika musu har suka zo ma" Aunty ta dauki wayar da kiran har ya riga ya katse tace "bara in kira in basu hakuri, ban kyauta ba wallahi"
Kafin ta kira sai wani kiran ya sake shigowa, ta tashi tsaye ta dauka yana matsawa inda babu hayaniya ta fara wayarta, bata jima da tashi ba sai sai Hassan yazo, yan samarin sa guda uku suna binsa kamar jela, ya saka hannu ya dauki Abdullahi da tun daya hango shi ya fara tsalle a cinyar maman sa, ya daga shi yana kissing forehead dinsa sannan yace "shine kika zo kika yi zamanki kika barni da mutane ko?" Ta mike tana murmushi tare da pretending hamma, ya harare ta, tayi murmushi "ba laifi na bane Habibi, laifin wannan katon yaron na hannunka ne" sai shima ya ja kujera ya zauna "nima zama zanyi, duk wanda yazo yanzu ke zaki zagaya dashi" ya zauna Sumayya ta fara zuba masa drink sannan ta zubawa boys din suma. Suna ta hada baki gurin bata labarin abubuwan da suka faru a gurin.
Sun jima a haka sannan Aunty ta dawo daga wayar da taje yi. Yanayin fuskarta ya saka kusan gaba ki dayansu suka mike tsaye, Nafisa tace "Aunty mutuwa akayi? Waye ya mutu kuma?" Aunty ta bisu da kallo daya bayan daya sannan tace "ba mutuwa akayi ba, the most strangest thing has happened, Fatima ta dawo gida, bata mutu ba"
Wannan littafin na siyarwa ne idan kika ganshi a wani guri na sata ne, in kina son ki sayi halaliyar ki ki yi min magana ta wannan number din through WhatsApp 08067081020
*Ina masu bukatar hadadu kuma ingantatun turarukan wuta da khumra masu dadin kamshi kuma a farashi me sauki to ga dama tazo muku Awwaba scent nada turarukan wuta humra burners kasko shisa coal dorot stool dilka body milk dadai sauransu masu bukatar na iya nemansu a whats app ko kuma kira ta wannan lambar 08034236800*
*bugu da kari duk wanda ya sayi humra ko turaren wuta a cikin wannan watan akwai kyautar dilka me kyau tafiyaya daga kasar chad wadda zata gyara jiki tay expoliating skin acikin minti 20 kawai ku garzayo dan kwasar garabasa*
*Adress kundila zoo road kano muna tura sako ko ina da iznin Allah*