Sashe 116
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Kamar dag asama taji ance "in kina yawan zurfafa tunani.....kina zama ke kadai kiyi kuka.....zaki tsufa da wuri" ya fada da sigar tsokana. Ta dago kai tana kallon Hassan, fuskar sa babu yabo babu fallasa. Ta fahimci tsokanar ta yake yi but she is in no mood for wasa dan haka ta mike tana gyara hijab din jikinta tace "kun gama?" Yace "mun kusa dai, kar mosquitoes su cinye ki naga kin zauna kusa da flowers shi yasa nayi miki magana ko zaki koma daga can" ya fada yana nuna inda aka saka kujeru "saura few mutane mu gama" taji babu dadi, tana so tace masa zata yi tafiyar ta kawai in yaso in taje gida ta karbi kudi ta biya, amma kuma bata so yaga hakan a matsayin rashin kyautata wa. Sai ta tafi inda yace mata ta zauna tana cigaba da daddanna phone dinta har taga ya kuma tahowa shida wasu maza su biyu, suna ta hirar su sai ya dago mata hannu yace "let's go" ta mike tabi bayansu, amma ta bar dan space a tsakanin ta dasu. Suka je gurin mota sai taga ya zagaya ya bude mata kofar gefen driver, yayi mata alamar ta shiga da hannunsa. Zata shiga kenan taji wani a gurin yace "Madam babu magana? Ya gida ya yaran?" Ta juyo tana kallon sa, daga yadda yayi maganar ta fahimci ya dauka Ruqayyah ce, sau ta kalli Hassan sai taga ya bude baki ya rufe ya kasa yin magana, sai tayi sauri tace "lafiya lau. Yara sun bi Aunty" sai dayan yace "ohh anyi musu wayo an kora su dan asha soyayya a hanya ko? To ayi a hankali dai kar a soye" suka yi dariya su biyun. Da sauri Sumayya ta shiga ta rufe kofar, tana kallon suka yi sallama da Hassan sannan suka fara tafiya kafin shima yazo ya shiga kusa da ita ya zauna ya tayar da motar, sai taji a ranta ina ma a baya ta zauna ba'a gaba ba? Duk kuwa da cewa ba wai yau ne karo na farko da suka zauna kamar haka ba ita da Hassan amma da yana a matsayin mijin twin sister dinta ne amma yanzu babu wancan link din, sai taga kamar zaman nasu bai dace ba.
Bai ce mata komai ba har yayi magana da mai gadin gurin sannan suka fita. Sai da suka dauki hanya sannan yace "sorry about that. Da yawa daga friends dina basu san mun rabu da Ruqayyah ba, and you guys look alike, sun dauka ita ce" ta gyada kai tace "babu komai,na fahimta ai" suka sake yin shiru sannan ya kuma yin gyaran murya yace "to ya kikaga gurin? Yayi? Huh?" Tace "yayi kyau sosai, Allah ya sanya alkhairi" yace "ameen, yayi kyau fa, ko Hussain in da zai gani sai yace yayi kyau. Kinsan shi ba komai ne yake burge shi ba" ya danyi dariya, "but it took a lot out of me, sai da aikin nan yayi min tas, in nace tas ina nufin tas, account dina sai da yayi reading 0.00" yadda ya jera zeros din yasa ta danyi murmushi, tace "tunda an gama ai shikenan" yace "shikenan fa, sai da family suka saka min hannu sannan na samu na kammala, gashi already yanzu har an karbi wasu daga ciki" tace "Masha Allah. Allah yasa musu albarka baki daya".
Ji take yi a ranta kamar ta tura motar dan suyi sauri amma shi ta fahimci wani taking time dinsa yake yi. Ta dan kunna wayar ta tana kallon time, ya kalle ta yace "expecting a call?" Ta girgiza kai, ira waye zai kirata a wannan lokacin in ba Inna ba? Inna ce kawai zata iya kiranta tace ya akayi bata dawo gida ba har yanzu, ita ma kuma bata kira ba dan tana tunanin she is in safe hands.
Suka sake yin shiru sannan yace "ya labarin friend dinku kuwa? Any development? Da muna waya da mijinta kuma daga baya da abubuwa suka dan sha kaina sai na manta da maganar" tace "Minal? Har yanzu babu labari fa, har an fitar da rai kuma. Iyayenta sunyi kuka sun gama, yan uwanta ma haka. Ni har bana so in je gidan su wallahi saboda Maman su tausayi take bani sosai" yace "dole ta baki tausayi, batan mutum akwai tashin hankali ai ballantana a yanayin da take ciki" ta gyada kai da sauri hawaye yana cika idonta, ya lura da sanda ta goge hawayen sai yace "yana gidan su, kin sani" ta girgiza kanta "bamu tabbatar ba. We don't know for sure" yace "Ruqayyah ta aikawa iyayensa labarin inda yake, dama sun dade suna nemanshi, babansa yayi tafiya a dai dai lokacin da shi kuma ya bata, ko motar da yake ciki ba'a dauka ba, ko waya ta da take cikin motar ba'a dauka ba. It adds up to me. Yana tare da iyayensa" ta juyo tana kallon sa ta cikin hawayen ta tace "da zai kira ni ai, a zaiyi making effort na ganin ya dawo gare ni ai. Ba zai manta dani gaka lokaci daya ba, except...." Yace "except what?" Tace "ta gyara zamanta tace "except ko iyayen sunyi masa asiri ko something" ya danyi murmushi yace "mu kuma sai muyi masa addu'a. Duk a inda yake zata same shi am sure watarana zai zo gare ki da kansa"
Tace "ina so ya dawo gare ni tabbas, but ba wannan ne babban abinda nake bukata ba, I just want to know cewa he is fine. In na samu wannan assurance din hankali na zai kwanta sosai" ya gyada kai yace "na fahimce ki. Me kike so ayi?" Ta girgiza kai tace "abinda nake son yi ba zai yiwu ba, ba za'a barni ba" yace "menene kike so?" Tace "inje nemansa" ya danyi dariya yace "imo? Zaki tafi neman Adam? To in kinje ta ina zaki fara? Ta wanne local government din ta wanne unguwa?" Tayi shiru tana wasa da hannunta, itama bata sani ba, basu taba wannan maganar da Adam ba. Sai yace "Baba ba zai barki ba, nima ba zan barki ba" ta dago kai tana kallonsa tan mamakin yadda ya dauki responsibility din barinta ya dora a kansa.
Sai yace "abu daya zan iya barin ki kiyi, ko kuma ince zanyi miki, zamu saka rana mu koma Kano tare, mu sake gwada bribing mai gadin nan mu gani ko zai kara bamu wani info din. Daga nan zamu gani idan family din sun dawo gida sai mu gani ko suma zamu iya samun wani abu daga gare su" ta gyada kai da sauri. "Yaushe zamu tafi?" Yayi dariya yana jinjina soyayyar da Sumayya take yiwa adam yace "zan saka rana, sai in gaya miki. Sai dai ni yanzu kamar ma bani da phone number din ki" ya fada yana mika mata wayarsa, da sauri ta saka masa number din tayi saving ta mika masa. Ya karba yana packing a kofar gidan su, tayi masa godiya sannan ta fita, ya bita da kallo har ta bude kofar gidan su ta shiga sannan ya ja motar, a ransa yana tunawa da ranar daya fara zuwa zance gurin Ruqayyah, lokacin da Sumayya ta fara fitowa yayi tunanin Ruqayyah ce.
Bai ce mata komai ba har yayi magana da mai gadin gurin sannan suka fita. Sai da suka dauki hanya sannan yace "sorry about that. Da yawa daga friends dina basu san mun rabu da Ruqayyah ba, and you guys look alike, sun dauka ita ce" ta gyada kai tace "babu komai,na fahimta ai" suka sake yin shiru sannan ya kuma yin gyaran murya yace "to ya kikaga gurin? Yayi? Huh?" Tace "yayi kyau sosai, Allah ya sanya alkhairi" yace "ameen, yayi kyau fa, ko Hussain in da zai gani sai yace yayi kyau. Kinsan shi ba komai ne yake burge shi ba" ya danyi dariya, "but it took a lot out of me, sai da aikin nan yayi min tas, in nace tas ina nufin tas, account dina sai da yayi reading 0.00" yadda ya jera zeros din yasa ta danyi murmushi, tace "tunda an gama ai shikenan" yace "shikenan fa, sai da family suka saka min hannu sannan na samu na kammala, gashi already yanzu har an karbi wasu daga ciki" tace "Masha Allah. Allah yasa musu albarka baki daya".
Ji take yi a ranta kamar ta tura motar dan suyi sauri amma shi ta fahimci wani taking time dinsa yake yi. Ta dan kunna wayar ta tana kallon time, ya kalle ta yace "expecting a call?" Ta girgiza kai, ira waye zai kirata a wannan lokacin in ba Inna ba? Inna ce kawai zata iya kiranta tace ya akayi bata dawo gida ba har yanzu, ita ma kuma bata kira ba dan tana tunanin she is in safe hands.
Suka sake yin shiru sannan yace "ya labarin friend dinku kuwa? Any development? Da muna waya da mijinta kuma daga baya da abubuwa suka dan sha kaina sai na manta da maganar" tace "Minal? Har yanzu babu labari fa, har an fitar da rai kuma. Iyayenta sunyi kuka sun gama, yan uwanta ma haka. Ni har bana so in je gidan su wallahi saboda Maman su tausayi take bani sosai" yace "dole ta baki tausayi, batan mutum akwai tashin hankali ai ballantana a yanayin da take ciki" ta gyada kai da sauri hawaye yana cika idonta, ya lura da sanda ta goge hawayen sai yace "yana gidan su, kin sani" ta girgiza kanta "bamu tabbatar ba. We don't know for sure" yace "Ruqayyah ta aikawa iyayensa labarin inda yake, dama sun dade suna nemanshi, babansa yayi tafiya a dai dai lokacin da shi kuma ya bata, ko motar da yake ciki ba'a dauka ba, ko waya ta da take cikin motar ba'a dauka ba. It adds up to me. Yana tare da iyayensa" ta juyo tana kallon sa ta cikin hawayen ta tace "da zai kira ni ai, a zaiyi making effort na ganin ya dawo gare ni ai. Ba zai manta dani gaka lokaci daya ba, except...." Yace "except what?" Tace "ta gyara zamanta tace "except ko iyayen sunyi masa asiri ko something" ya danyi murmushi yace "mu kuma sai muyi masa addu'a. Duk a inda yake zata same shi am sure watarana zai zo gare ki da kansa"
Tace "ina so ya dawo gare ni tabbas, but ba wannan ne babban abinda nake bukata ba, I just want to know cewa he is fine. In na samu wannan assurance din hankali na zai kwanta sosai" ya gyada kai yace "na fahimce ki. Me kike so ayi?" Ta girgiza kai tace "abinda nake son yi ba zai yiwu ba, ba za'a barni ba" yace "menene kike so?" Tace "inje nemansa" ya danyi dariya yace "imo? Zaki tafi neman Adam? To in kinje ta ina zaki fara? Ta wanne local government din ta wanne unguwa?" Tayi shiru tana wasa da hannunta, itama bata sani ba, basu taba wannan maganar da Adam ba. Sai yace "Baba ba zai barki ba, nima ba zan barki ba" ta dago kai tana kallonsa tan mamakin yadda ya dauki responsibility din barinta ya dora a kansa.
Sai yace "abu daya zan iya barin ki kiyi, ko kuma ince zanyi miki, zamu saka rana mu koma Kano tare, mu sake gwada bribing mai gadin nan mu gani ko zai kara bamu wani info din. Daga nan zamu gani idan family din sun dawo gida sai mu gani ko suma zamu iya samun wani abu daga gare su" ta gyada kai da sauri. "Yaushe zamu tafi?" Yayi dariya yana jinjina soyayyar da Sumayya take yiwa adam yace "zan saka rana, sai in gaya miki. Sai dai ni yanzu kamar ma bani da phone number din ki" ya fada yana mika mata wayarsa, da sauri ta saka masa number din tayi saving ta mika masa. Ya karba yana packing a kofar gidan su, tayi masa godiya sannan ta fita, ya bita da kallo har ta bude kofar gidan su ta shiga sannan ya ja motar, a ransa yana tunawa da ranar daya fara zuwa zance gurin Ruqayyah, lokacin da Sumayya ta fara fitowa yayi tunanin Ruqayyah ce.