Sashe 87
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai dai ba wai rashin son a kure shine ya hana shi zuwa a duba gender din abinda yake cikin Fatima ba, damuwarsa shine yadda rabon gadonsa zai kasance idan ya mutu, dan haka ya yanke wani hukunci kuma ya gama tsara duk plans dinsa gabadaya sannan yaje ya samu Hassan a office dinsa ya ajiye masa takardu a gabansa yace "I need to sign these" Hassan ya dauki takardar yana jujjuya ta yana karantawa briefly, ya dago kai yana kankance idonsa yace "what is this? Me kake yi haka?" Hussain ya daga kafada yace "I am giving you half of h and h and all it's assets. Dama sunan sa H and H ma'ana Hassan da Hussain, it is yours as much as it mine, ka sani kuma" Hassan ya girgiza kansa yana dawo masa da takardun gabansa yace "bazan karba ba kuma kaima ka sani, ba tun yau ba ka nuna kana son bani nace bana so saboda ni nafi son inyi working in kuma yi earning kudi na da kaina. Wannan naka ne, H and H naka ne ba namu bane ba kuma kai ma kasan wannan" Hussain yace "shikenan, in baka karba ba ya zama na lawyers dina dan already na riga na fitar dashi kuma sun saka hannu, yanzu saka hannun ka kawai ya rage" suka yi shiru suna kallon juna. Hussain yace "look Hassan, ba wai na baka bane dan baka dashi ko dan in taimaka maka ba a'a na baka ne as security for our family, ban san abinda Fatima zata haifa ba, in ta haifi namiji yayi muku katanga da duk wani abu dana mallaka ni kuma ba zan so haka ba, zanso ace kun gaje ni kai da kannen mu saboda dama dan in kula damu na fara business din nan. Gidan mu da wannan kamfanonin aka dogara gabaki daya, idan Fatima da danta suka karbe komai kai da Aunty da sauran yan'uwa zaku koma a karkashin ta kenan, you will be working under my son and wife abinda ni kuma ba zai min dadi ba duk da nasan Fatima kuma ina saka ran abinda zata haifa zai samu tarbiyya mai kyau daga gurinta da kuma gurinka. But zan so ace kun zama partners ne. Yadda ko ma me ta haifa you still have your share, wadda nasan zaka yi amfani da ita ne gurin kula da kanka da Aunty da yan uwan mu da yayan mu, all of them".
Hassan yace "stop talking as if mutuwa zaka yi Please, idan da kasan yadda maganganunka suke taba zuciyata da ka daina yin irin su Hussain. You are getting well, ba ka ganin yadda jikin ka yayi kyau?" Hussain ya mike yanakara tura masa takardun gabansa yace "sign this please, and try to get some sleep dan ka rame da yawa".
Daga nan ya fice ya barshi a zaune, ya jawo takardun yana duba signature din Hussain baro baro a jiki cewa ya bashi rabin duk abinda ya mallaka a duniya. Sai ya jawo drawer ya saka takardun sannan ya mayar ya rufe. Ya koma ya kife kansa akan table din gabansa yana jin kansa yana sarawa sosai. Shi kansa yasan ya rame ya kara baki ya bushe, mutane da yawa suna tambayarsa "lafiyar ka kalau kuwa?" Yakan amsa da eh amma shi kansa ya san bashi da lafiya, ciwon nan na Hussain yana damunsa sosai kullum hankalinsa ba a kwance yake ba, ko magana yaji anyi da karfi ko kuma yaji hayaniya sai gabansa ya fadi, sai ya dauka za'a ce masa wani abu ya samu Hussain din sa.
Ga kuma problem din Ruqayyah. Duk da wani bangare na zuciyarsa wanda yake cike da sonta kullum yana yi mata uzuri amma kaso mafi yawa na tunanin sa yafi karkatuwa ga karbar gaskiyar magana. Gaskiyar magana kuma shine bai yi dace da mace ta gari ba. Lokuta da dama yakan samu kansa da tambayar kansa shin ina wannan Hassanar daya aura take? Anya ba'a chanja masa da wata ba kuwa? Ina wannan karamar yarinyar nan data dora rayuwarsa a saman tata ta ceto shi daga bakin bindiga take, ina yarinyar nan yar gidan malamai mai cike da tarbiyya, kunya da ilimin addini? Ina yarinyar da bata saba da kyale kyalen duniya ba? Dan yasan ba ita bace wannan wadda last week ta hana masa sakat a gidan sa da mitar Hussain ya sake wa Fatima mota ita banda ita ba, dan waccan yarinyar babanta ko keke bashi dashi.
Yanzu gidan sa ya koma abin gudu a gurinsa, wannan yasa kullum yana office, har weekend zuwa yake yi yayi ta aiki shi kadai musamman tunda yanzu Hussain ya tattara harkar kamfanin yayi watsi da ita. Shi kuma sai ya dauki aikin yake tayi da iya kacin karfinsa dan yana so ya rage wa kansa tunani kuma ya nesanta kansa da fada da kuma mitar Ruqayyah. Yau ma kafin ya fito sai data saka shi a gaba da zancen tana son ya bata kudi ta tafi Dubai siyayyar haihuwa.
Hussain yana komawa gida yayi wa Fatima alkawarin ta lissafa masa dream countries din da take son zuwa a rayuwarta shi kuma zai kaita. Ta bude baki cikin murna "lah! Na dauka yanzu baka son fita" yace "yanzu ina so, so nake mu fita mu samu good quality time daga ni sai ke sai baby" ai kuwa nan take ta fara lissafa masa duk inda take son zuwa, shi kuma ya ware wasu kudade masu kyau daga cikin personal kudinsa ya fara shirya musu tafiyar. Kafin wani lokaci komai ya kammala, suka shirya suka tafi and they spent the best days of their lives together. A lokacin ne ciwon Hussain yafi karfin drugs din da ya ke sha har Fatima ta fara fahimtar bashi da lafiya, amma sai ya gaya mata cewa ulcer ce take damunsa, ta nemi suje asibiti sai ya shiga drug store kawai ya siyi magani ba tare da ya bari an wani do ba shi sosai ba. A lokacin ne labarin haihuwar Ruqayyah ya same su, ta haifi danta namiji kuma kowa ya kira sai ya gaya musu irin tsananin kamar da yaron yake yi da Hussain. Kuma Hassan ya rada masa suna Hussain duk da cewa bashi da abokin tagwaitaka. Wannan yasa hankalinsu kuma yayo gida dan itama Fatima nata cikin ya kai wata bakwai kenan, tace "naga alama dai gidan nan sai maza ake ta haifa, ni kam nafi son mace dan ta zama kawata amma ko namijin nema ina sonsa shima".
Hussain shima ba wai ya damu da lallai sai namiji ba, kawai dai yana ganin kamar namijin zai fi jan nasabarsa sosai akan mace, tunda ita mace in tayi aure ta haihu yayanta da gidan baban su zasu yi tutiya ba da shi ba, amma a yanzu yadda yake jin ya matsu yaga abinda zai haifa ko macen cema yana so sosai. Sai suka shirya dawowa Nigeria dan ayi sunan takwaran Hussain dasu, kafin su taho sai Hussain ya dauke ta zuwa asibiti inda ya nemi ayi musu 4d scan na babyn cikinta. Tayi ta mamakin dalilinsa nayin hakan bayan da yace ko gender baya son sani, ta tambayeshi dalili sai yace "I changed my mind, ina tsananin son ganin abinda yake cikin ki ko da a hoto ne" ita bata taba sanin cewa 4d pregnancy scan is possible ba sai yau, lallai technology babu abinda ya bari rai ne kawai Allah bai bawa turawa ikon hurawa jiki ba, babyn da yake kwance a cikinta sai gashi suna ganinsa clearly a jikin screen a kwance a cikin amniotic fluid yana ta tsotsar hannunsa, idanuwan sa tar a bude. Ba sai Doctor ya gaya musu ba su da kansu suka gani cewa namiji ne, ta juyo da sauri ta kalli Hussain sai taga hankalinsa yana kan screen din yana kallon babyn, and she saw a tear in his eyes but sai yayi sauri ya mayar da ita a hankali yace "bai yi miki kara ba, kamar mu daya" ta turo baki "ai dama hada baki kuke yi kullum in kana yi masa hira, a lokacin kukayi meeting kuka ware ni" ya danyi dariya, tace "amma ai kalar fata ta ce dashi, bai kai ka haske ba" yace "waya gaya miki? ai hoton black and white ne kuma yayi duhu ba zaki gane kalar fata ba".
Sun jima suma kallon babyn su for 30 minutes wanda shine medically advisable sannan aka kashe, Hussain yaji kamar an kashe wani part na zuciyarsa ya daina amfani, sai dai kawai jin dadin sa shine an musu record na scan din a CD aka basu. At least ya samu abin gani kafin babyn yazo, that's in babyn zai zo ya tarar da shi.
Kwana biyu bayan nan suka dauki hanyar Nigeria. Suna sauka suka je suka ga jaririn Ruqayyah, Fatima tana jin kamar ta sace shi saboda kamannin da taga yana yi da Hussain.
Bayan an kammala suna ne Hussain ya koma Abuja gurin Doctor din da yake dubashi yayi requesting ya bashi wasu magungunan da suka fi wadancan karfi, amma sai Doctor din ya nuna masa cewa babu sama da wadannan, from kallon da Doctor din yake yi masa yasan cewa lokacin da ya rage masa bashi da yawa, amma sai yaji har cikin zuciyarsa baya jin tsoro kawai dai yana bakin cikin rabuwa da masoyansa ne. A ranar bayan ya koma gida ya dauko diary dinsa wanda har ya kusa cika shi da rubutu ya rubuta..
Dear baby
Hassan yace "stop talking as if mutuwa zaka yi Please, idan da kasan yadda maganganunka suke taba zuciyata da ka daina yin irin su Hussain. You are getting well, ba ka ganin yadda jikin ka yayi kyau?" Hussain ya mike yanakara tura masa takardun gabansa yace "sign this please, and try to get some sleep dan ka rame da yawa".
Daga nan ya fice ya barshi a zaune, ya jawo takardun yana duba signature din Hussain baro baro a jiki cewa ya bashi rabin duk abinda ya mallaka a duniya. Sai ya jawo drawer ya saka takardun sannan ya mayar ya rufe. Ya koma ya kife kansa akan table din gabansa yana jin kansa yana sarawa sosai. Shi kansa yasan ya rame ya kara baki ya bushe, mutane da yawa suna tambayarsa "lafiyar ka kalau kuwa?" Yakan amsa da eh amma shi kansa ya san bashi da lafiya, ciwon nan na Hussain yana damunsa sosai kullum hankalinsa ba a kwance yake ba, ko magana yaji anyi da karfi ko kuma yaji hayaniya sai gabansa ya fadi, sai ya dauka za'a ce masa wani abu ya samu Hussain din sa.
Ga kuma problem din Ruqayyah. Duk da wani bangare na zuciyarsa wanda yake cike da sonta kullum yana yi mata uzuri amma kaso mafi yawa na tunanin sa yafi karkatuwa ga karbar gaskiyar magana. Gaskiyar magana kuma shine bai yi dace da mace ta gari ba. Lokuta da dama yakan samu kansa da tambayar kansa shin ina wannan Hassanar daya aura take? Anya ba'a chanja masa da wata ba kuwa? Ina wannan karamar yarinyar nan data dora rayuwarsa a saman tata ta ceto shi daga bakin bindiga take, ina yarinyar nan yar gidan malamai mai cike da tarbiyya, kunya da ilimin addini? Ina yarinyar da bata saba da kyale kyalen duniya ba? Dan yasan ba ita bace wannan wadda last week ta hana masa sakat a gidan sa da mitar Hussain ya sake wa Fatima mota ita banda ita ba, dan waccan yarinyar babanta ko keke bashi dashi.
Yanzu gidan sa ya koma abin gudu a gurinsa, wannan yasa kullum yana office, har weekend zuwa yake yi yayi ta aiki shi kadai musamman tunda yanzu Hussain ya tattara harkar kamfanin yayi watsi da ita. Shi kuma sai ya dauki aikin yake tayi da iya kacin karfinsa dan yana so ya rage wa kansa tunani kuma ya nesanta kansa da fada da kuma mitar Ruqayyah. Yau ma kafin ya fito sai data saka shi a gaba da zancen tana son ya bata kudi ta tafi Dubai siyayyar haihuwa.
Hussain yana komawa gida yayi wa Fatima alkawarin ta lissafa masa dream countries din da take son zuwa a rayuwarta shi kuma zai kaita. Ta bude baki cikin murna "lah! Na dauka yanzu baka son fita" yace "yanzu ina so, so nake mu fita mu samu good quality time daga ni sai ke sai baby" ai kuwa nan take ta fara lissafa masa duk inda take son zuwa, shi kuma ya ware wasu kudade masu kyau daga cikin personal kudinsa ya fara shirya musu tafiyar. Kafin wani lokaci komai ya kammala, suka shirya suka tafi and they spent the best days of their lives together. A lokacin ne ciwon Hussain yafi karfin drugs din da ya ke sha har Fatima ta fara fahimtar bashi da lafiya, amma sai ya gaya mata cewa ulcer ce take damunsa, ta nemi suje asibiti sai ya shiga drug store kawai ya siyi magani ba tare da ya bari an wani do ba shi sosai ba. A lokacin ne labarin haihuwar Ruqayyah ya same su, ta haifi danta namiji kuma kowa ya kira sai ya gaya musu irin tsananin kamar da yaron yake yi da Hussain. Kuma Hassan ya rada masa suna Hussain duk da cewa bashi da abokin tagwaitaka. Wannan yasa hankalinsu kuma yayo gida dan itama Fatima nata cikin ya kai wata bakwai kenan, tace "naga alama dai gidan nan sai maza ake ta haifa, ni kam nafi son mace dan ta zama kawata amma ko namijin nema ina sonsa shima".
Hussain shima ba wai ya damu da lallai sai namiji ba, kawai dai yana ganin kamar namijin zai fi jan nasabarsa sosai akan mace, tunda ita mace in tayi aure ta haihu yayanta da gidan baban su zasu yi tutiya ba da shi ba, amma a yanzu yadda yake jin ya matsu yaga abinda zai haifa ko macen cema yana so sosai. Sai suka shirya dawowa Nigeria dan ayi sunan takwaran Hussain dasu, kafin su taho sai Hussain ya dauke ta zuwa asibiti inda ya nemi ayi musu 4d scan na babyn cikinta. Tayi ta mamakin dalilinsa nayin hakan bayan da yace ko gender baya son sani, ta tambayeshi dalili sai yace "I changed my mind, ina tsananin son ganin abinda yake cikin ki ko da a hoto ne" ita bata taba sanin cewa 4d pregnancy scan is possible ba sai yau, lallai technology babu abinda ya bari rai ne kawai Allah bai bawa turawa ikon hurawa jiki ba, babyn da yake kwance a cikinta sai gashi suna ganinsa clearly a jikin screen a kwance a cikin amniotic fluid yana ta tsotsar hannunsa, idanuwan sa tar a bude. Ba sai Doctor ya gaya musu ba su da kansu suka gani cewa namiji ne, ta juyo da sauri ta kalli Hussain sai taga hankalinsa yana kan screen din yana kallon babyn, and she saw a tear in his eyes but sai yayi sauri ya mayar da ita a hankali yace "bai yi miki kara ba, kamar mu daya" ta turo baki "ai dama hada baki kuke yi kullum in kana yi masa hira, a lokacin kukayi meeting kuka ware ni" ya danyi dariya, tace "amma ai kalar fata ta ce dashi, bai kai ka haske ba" yace "waya gaya miki? ai hoton black and white ne kuma yayi duhu ba zaki gane kalar fata ba".
Sun jima suma kallon babyn su for 30 minutes wanda shine medically advisable sannan aka kashe, Hussain yaji kamar an kashe wani part na zuciyarsa ya daina amfani, sai dai kawai jin dadin sa shine an musu record na scan din a CD aka basu. At least ya samu abin gani kafin babyn yazo, that's in babyn zai zo ya tarar da shi.
Kwana biyu bayan nan suka dauki hanyar Nigeria. Suna sauka suka je suka ga jaririn Ruqayyah, Fatima tana jin kamar ta sace shi saboda kamannin da taga yana yi da Hussain.
Bayan an kammala suna ne Hussain ya koma Abuja gurin Doctor din da yake dubashi yayi requesting ya bashi wasu magungunan da suka fi wadancan karfi, amma sai Doctor din ya nuna masa cewa babu sama da wadannan, from kallon da Doctor din yake yi masa yasan cewa lokacin da ya rage masa bashi da yawa, amma sai yaji har cikin zuciyarsa baya jin tsoro kawai dai yana bakin cikin rabuwa da masoyansa ne. A ranar bayan ya koma gida ya dauko diary dinsa wanda har ya kusa cika shi da rubutu ya rubuta..
Dear baby