Sashe 18
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai tace "bana son ku tsaya dashi a waje, bana son kuma ku zauna a cikin motarsa, gashi kuma bamu da soro ballantana ya zauna. Abinda za'a yi bara in sallami yaran nan sai ayi masa shimfida a tsakar gida ku zauna ku gaisa, dake da Sumayya zaku je. Ni kuma zan zauna a daki. Ki kiyaye ni Ruqayyah, in kika nuna masa halinki wallahi xan saka baban ku ya gaya masa kar ya sake zuwa gidan nan" Ruqayyah tayi saurin gyada kanta, ta yarda, ta yarda da ko wanne sharadi in dai za'a bata wannan chance din. Wannan chance ne one in a million ta samu kuma ba zata yi wasa da shi ba.
Tana cikin shirya wa Sumayya ta shigo itama ta wanko fuskarta, duk basu yi kwalliya ba sai mai da suka shafa suka saka kaya da dogayen hijabs dinsu. Sannan Sumayya ta shimfida tabarmi guda biyu a kasan bishiya sannan ta shimfida sallaya a saman tabarma daya. Ruqayyah kuma ta dauko sabon kwanon shan ruwan Inna Ade ta debo ruwa ta ajiye sannan ta dora kofi akai.
Sumayya ce ta fita kiransa. Yana motar dai a zaune suna hira shi da drivern, lokaci zuwa lokaci yana kallon kofar shiga gidan zuciyarsa tana son ganin fitowarta. Sai ga Sumayya ta fito, idonta ya sauka kan motar amma da yake tinted glass ne bata hango na ciki ba amma shi ya hango ta, yaji bugun zuciyarsa ya karu, ya dakata da hirar da yake yana samun damar kare mata kallo tare da tunowa da waccan fuskar da ya gani ranar nan. Abinda ya fara fahimta a tare da ita shine yadda take tafiya cikin nutsuwa. Ta tsaya a gaban motar cikin yanayin rasa abinyi. Sai kuma tayi sallama tare da knocking window din. Yaji dadin sallamar da yaji tayi. Ya sauke glass din window din a hankali sannan ya sauke idonsa cikin nata. Tayi murmushi mai fadi, ko ba'a gaya mata ba ta san shine wannan duk da cewa ranar nan bata wani ga fuskarsa sosai ba.
Ta dan durkusa kadan tace "ina yini, sannu da zuwa" ya jefa mata best smile dinsa yace "lafiya lau....." Sai ta katse shi "ammmm an ce ka shigo ciki, Ruqayyah Hassana tana ciki" ya kankance idonsa yana kallonta cikin mamaki, sai ta danyi yar dariya tace "ni sunana Sumayya...." Yace "Hussaina?" Ta daga masa kai ya bude kofar motar ya fito ya na kallon ta yace "gwara in gane ki sosai kar aje ayi min chanje"
ta sake dariya, ya fahimci tana da fara'a sosai tace "baza ayi maka bama, ka kwantar da hankalinka" suka jera yana cewa "amma kuna kama sosai fa" tace "haka ake cewa, amma if you get to know us zaka gane banbancin mu" ita ta fara shiga sannan shi, abinda ya fara lura dashi shine tsaftar gidan da kuma alluna alamar ana koyar da karatu a gidan. Sai kuma yaga shimfidar da akayi masa sannan yaji kamshin tuwon da yake kan wuta. Ya zauna akan shimfidar sannan Sumayya ta durkusa ta sake gaishe shi, ya amsa mata cikin kulawa sannan ta tambaye shi mutan gida.
A lokacin Ruqayyah ta fito daga dakin su, kanta akasa, hannayenta a boye a cikin hijab dinta, fuskarta cike da wani yana yi mai wahalar fassara. Tun da tayi taku na farko taji idonsa ya saukaa kanta, sai taji wani irin yanayi ya lullube ta taji abin duk ba yadda tayi tsammani bane ba, taji ta kasa dago kai ta kalle shi, taji kuma tana son ta kalle shi din.
Kan daya tabarmar taje kusa da Sumayya ta zauna tare da gaishe shi murya can kasa " ya jikin? Allah ya kara lafiya" ya dan kalli dakunan d aduke gefe, ya san akwai mutum a cikin dakin dan haka dole yayi ajjiyar kalamansa sai wani jikon kuma. Amma shi kam yasan zuciyarsata tafi ga wannan yar karamar yarinyar da take kokarin gaisheshi. "Ya naki jikin? Ina fatan ranar nan baki ji ciwo ba" ta girgiza kanta tace "babu ciwo, Nagode" ya sunkuyo yana kokarin kallon fuskarta sai ta kara jawo hijab dinta ta kara rufe fuskar, ya danyi murmushi mai sauti yace "kin gode da me?" Tace "da ka damu dani har ka tambayi lafiya ta" yace "lallai ke ɗin ta daban ce tunda har zaki yi min godiya bayan nine ya kamata inyi miki godiya. Ki sani Hassana, bana jin akwai abinda zanyi miki wanda zai nuna irin godiya ta gare ki, duk abinda zanyi kwatanta wa ne kawai amma ninba zan iya biyan ki ba, Allah ne kadai zai biya ki. Ina kuma fatan ya biya ki da aljannar firdausi"
Sumayya tace "ameen, tare da mu baki daya" ya sake kallon dakin yana feeling uncomfortable, akwai maganganu daya ta tsarawa tun a India amma duk ba zai iya fadin su ba a wannan setting din, dole ya bar wannan ziyarar a matsayin ta godiya kadai in yaso in ya kuma xuwa ya fara kafa gwamnatin sa. Amma duk da haka zai gwada ko dan kadan ne, at least dan asan inda ya dosa.
Ya kalli Sumayya yace "kinga har na gano banbancin ku da Hassana ta" Sumayya ta bude ido tace "menene banbancin?" Yace "Hassana ta ta fiki nutsuwa, ta fiki kunya tunda gashi nan ta kasa kallona har yanzu kuma ta kasa bari in kalli fuskarta. Ki roka min ita ta kalle ni ko da sau daya ne kar ta saka yau in manta hanyar gidan mu in dawo nan in kwana"
Sumayya tayi dariya tace "in kai ka manta drivern ka aishi ba zai manta ba" ya dafe kai yace "haka ne fa. To amma ai na kasa bacci ko? In banyi bacci ba kuma kinga ba zan samu karfin da zan dawo gobe in tambayi Baba ya bani izinin fara zuwa zance gurinta ba" Sumayya ta sake dariya, Ruqayyah ma ta danyi dariya a cikin hijabin ta, tana kallon saitin fuskarta ta cikin hijab din yace "kuma na sake gano wani banbancin naku, ta fiki kyau, dan na hango dogon hancinta ta jikin hijab" Ruqayyah tayi sauri ta kuma jan hijab din gaba yadda fuskarta ba zata fito ba.
Yayi gyaran murya yace "abinda duk nake nema zan iya cewa na same su gabaki daya a gurin ki Hassana. Addini, tarbiyya, kunya, nutsuwa, kyau duk kina dasu. Ni na riga na samu mata Ruqayyah in dai kin amince kina sona ni da gaske nake aurenki zanyi in dai har iyayenki zasu bani ke" ya sake rage murya yace "amma ai ba zaki amince ba in nayi miki, ba zaki gane nayi miki ba kuma sai kin kalle ni" Sumayya ta kuma yin dariya, sai yaga tana tuna masa da Hussain ta bangaren fara'a. Sai ya samu kansa da fara yi mata hirar Hussain.
Ruqayyah ta dan bude fuskarta kadan ta mike ta zuba masa ruws a kofi tace "ga ruwa, ka sha" ya karba yana cewa "nagode sosai" sannan ya kalli Sumayya yace "kinga inda aka damu dani an fahimci ban sha ruwa ba, ke kuwa sai magana kuke saka ni" Sumayya tace "to bara in tashi in tafi in ya so sai kuyi hirar kurame tunda na fahimci ba magana zata yi maka ba" ya shanye ruwan ya ajiye cup din yace "kiyi zamanki, nine dai zan tafi. Ki mika min gaisuwata a gurin Mama sannan ki yi kokari gurin kafa min gwamnati na, ki fara da Foundation mai kyau dan ginin da nake so inyi na har abada ne"
ya mike sannan yace "in Baba ya dawo ki gaishe min dashi sannan ki gaya masa in babu damuwa gobe da kamar wannan lokacin zan dawo ina son magana dashi" ta amsa masa da insha Allah, sai ya dauko daurin kudi ya ajiye akan shimfidar yace "gashi ki sayi sweet, dan naga alamar kina da kwadayi"
Ranar Ruqayyah bata iya bacci ba. Tana ta sakawa da warwarewa.
Washegari ya dawo kamar yadda yayi alkawari. Baba kuma already yana zaune yana zamn jiransa kuma ya yanke shawarar abinda zai gaya masa, danda aka aiko ya zo sai Baba ya saka Sulaiman ya shimfida musu tabarma a waje daga gefe inda mutane ba zasu dame su ba, sannan ya fita gurinsa.
Ganin haka yasa Ruqayyah ta kira Zunnur ta tambaye shi a inda suke, ita kuma ta tafi dai inda suke daga cikin gida tayi shimfida ta zauna tana yanke farcenta. Kawai haka nan taji zuciyarta tana son taji maganar da zasu yi.
A waje Hassan ne tare da Jabir, yaso Hussain yazo du taho tare amma sai ya kirkiri wani excuse ya kawo amma Hassan ya fahimci zuwa ne baya son yi kuma yaji babu dadi. Bayan sun gaisa cikin mutunci da girmama juna, sun kuma yo doguwar godiya a bisa taimakon da aka yiwa Hassan a gidan sai Jabir ya shigar da maganar kudirin Hassan na neman izinin fara neman auren Ruqayyah.
Baba ya masu kudurin su cikin nuna jin dadin wannan karramawar amma kuma sai yace "amma wani hanzari ba gudu ba, ni ba zan boye maka ba tun ranar dana fara ganinka naji zuciya ta tana sonka, naji a raina ina ma dai kai dana ne, kuma yanzu zanji dadi sosai idan ka zamo dan nawa wato in ka auri yata, sai dai, in har ka amince ina son ka chanza daga Ruqayyah ka nemi Sumayya"
Ruqayyah ta dago kai daga yankan farcen ta, ba tare da ta ce komai ba ta mike ta tafi daki tana jin zuciyarta ta zama tamkar dunkulallen garwashin wuta.
Wannan littafin na kudi ne, duk mai son siya tayi wa wannan number din magana 08067081020
08067081020Episode thirteen: The Strategy
Tana cikin shirya wa Sumayya ta shigo itama ta wanko fuskarta, duk basu yi kwalliya ba sai mai da suka shafa suka saka kaya da dogayen hijabs dinsu. Sannan Sumayya ta shimfida tabarmi guda biyu a kasan bishiya sannan ta shimfida sallaya a saman tabarma daya. Ruqayyah kuma ta dauko sabon kwanon shan ruwan Inna Ade ta debo ruwa ta ajiye sannan ta dora kofi akai.
Sumayya ce ta fita kiransa. Yana motar dai a zaune suna hira shi da drivern, lokaci zuwa lokaci yana kallon kofar shiga gidan zuciyarsa tana son ganin fitowarta. Sai ga Sumayya ta fito, idonta ya sauka kan motar amma da yake tinted glass ne bata hango na ciki ba amma shi ya hango ta, yaji bugun zuciyarsa ya karu, ya dakata da hirar da yake yana samun damar kare mata kallo tare da tunowa da waccan fuskar da ya gani ranar nan. Abinda ya fara fahimta a tare da ita shine yadda take tafiya cikin nutsuwa. Ta tsaya a gaban motar cikin yanayin rasa abinyi. Sai kuma tayi sallama tare da knocking window din. Yaji dadin sallamar da yaji tayi. Ya sauke glass din window din a hankali sannan ya sauke idonsa cikin nata. Tayi murmushi mai fadi, ko ba'a gaya mata ba ta san shine wannan duk da cewa ranar nan bata wani ga fuskarsa sosai ba.
Ta dan durkusa kadan tace "ina yini, sannu da zuwa" ya jefa mata best smile dinsa yace "lafiya lau....." Sai ta katse shi "ammmm an ce ka shigo ciki, Ruqayyah Hassana tana ciki" ya kankance idonsa yana kallonta cikin mamaki, sai ta danyi yar dariya tace "ni sunana Sumayya...." Yace "Hussaina?" Ta daga masa kai ya bude kofar motar ya fito ya na kallon ta yace "gwara in gane ki sosai kar aje ayi min chanje"
ta sake dariya, ya fahimci tana da fara'a sosai tace "baza ayi maka bama, ka kwantar da hankalinka" suka jera yana cewa "amma kuna kama sosai fa" tace "haka ake cewa, amma if you get to know us zaka gane banbancin mu" ita ta fara shiga sannan shi, abinda ya fara lura dashi shine tsaftar gidan da kuma alluna alamar ana koyar da karatu a gidan. Sai kuma yaga shimfidar da akayi masa sannan yaji kamshin tuwon da yake kan wuta. Ya zauna akan shimfidar sannan Sumayya ta durkusa ta sake gaishe shi, ya amsa mata cikin kulawa sannan ta tambaye shi mutan gida.
A lokacin Ruqayyah ta fito daga dakin su, kanta akasa, hannayenta a boye a cikin hijab dinta, fuskarta cike da wani yana yi mai wahalar fassara. Tun da tayi taku na farko taji idonsa ya saukaa kanta, sai taji wani irin yanayi ya lullube ta taji abin duk ba yadda tayi tsammani bane ba, taji ta kasa dago kai ta kalle shi, taji kuma tana son ta kalle shi din.
Kan daya tabarmar taje kusa da Sumayya ta zauna tare da gaishe shi murya can kasa " ya jikin? Allah ya kara lafiya" ya dan kalli dakunan d aduke gefe, ya san akwai mutum a cikin dakin dan haka dole yayi ajjiyar kalamansa sai wani jikon kuma. Amma shi kam yasan zuciyarsata tafi ga wannan yar karamar yarinyar da take kokarin gaisheshi. "Ya naki jikin? Ina fatan ranar nan baki ji ciwo ba" ta girgiza kanta tace "babu ciwo, Nagode" ya sunkuyo yana kokarin kallon fuskarta sai ta kara jawo hijab dinta ta kara rufe fuskar, ya danyi murmushi mai sauti yace "kin gode da me?" Tace "da ka damu dani har ka tambayi lafiya ta" yace "lallai ke ɗin ta daban ce tunda har zaki yi min godiya bayan nine ya kamata inyi miki godiya. Ki sani Hassana, bana jin akwai abinda zanyi miki wanda zai nuna irin godiya ta gare ki, duk abinda zanyi kwatanta wa ne kawai amma ninba zan iya biyan ki ba, Allah ne kadai zai biya ki. Ina kuma fatan ya biya ki da aljannar firdausi"
Sumayya tace "ameen, tare da mu baki daya" ya sake kallon dakin yana feeling uncomfortable, akwai maganganu daya ta tsarawa tun a India amma duk ba zai iya fadin su ba a wannan setting din, dole ya bar wannan ziyarar a matsayin ta godiya kadai in yaso in ya kuma xuwa ya fara kafa gwamnatin sa. Amma duk da haka zai gwada ko dan kadan ne, at least dan asan inda ya dosa.
Ya kalli Sumayya yace "kinga har na gano banbancin ku da Hassana ta" Sumayya ta bude ido tace "menene banbancin?" Yace "Hassana ta ta fiki nutsuwa, ta fiki kunya tunda gashi nan ta kasa kallona har yanzu kuma ta kasa bari in kalli fuskarta. Ki roka min ita ta kalle ni ko da sau daya ne kar ta saka yau in manta hanyar gidan mu in dawo nan in kwana"
Sumayya tayi dariya tace "in kai ka manta drivern ka aishi ba zai manta ba" ya dafe kai yace "haka ne fa. To amma ai na kasa bacci ko? In banyi bacci ba kuma kinga ba zan samu karfin da zan dawo gobe in tambayi Baba ya bani izinin fara zuwa zance gurinta ba" Sumayya ta sake dariya, Ruqayyah ma ta danyi dariya a cikin hijabin ta, tana kallon saitin fuskarta ta cikin hijab din yace "kuma na sake gano wani banbancin naku, ta fiki kyau, dan na hango dogon hancinta ta jikin hijab" Ruqayyah tayi sauri ta kuma jan hijab din gaba yadda fuskarta ba zata fito ba.
Yayi gyaran murya yace "abinda duk nake nema zan iya cewa na same su gabaki daya a gurin ki Hassana. Addini, tarbiyya, kunya, nutsuwa, kyau duk kina dasu. Ni na riga na samu mata Ruqayyah in dai kin amince kina sona ni da gaske nake aurenki zanyi in dai har iyayenki zasu bani ke" ya sake rage murya yace "amma ai ba zaki amince ba in nayi miki, ba zaki gane nayi miki ba kuma sai kin kalle ni" Sumayya ta kuma yin dariya, sai yaga tana tuna masa da Hussain ta bangaren fara'a. Sai ya samu kansa da fara yi mata hirar Hussain.
Ruqayyah ta dan bude fuskarta kadan ta mike ta zuba masa ruws a kofi tace "ga ruwa, ka sha" ya karba yana cewa "nagode sosai" sannan ya kalli Sumayya yace "kinga inda aka damu dani an fahimci ban sha ruwa ba, ke kuwa sai magana kuke saka ni" Sumayya tace "to bara in tashi in tafi in ya so sai kuyi hirar kurame tunda na fahimci ba magana zata yi maka ba" ya shanye ruwan ya ajiye cup din yace "kiyi zamanki, nine dai zan tafi. Ki mika min gaisuwata a gurin Mama sannan ki yi kokari gurin kafa min gwamnati na, ki fara da Foundation mai kyau dan ginin da nake so inyi na har abada ne"
ya mike sannan yace "in Baba ya dawo ki gaishe min dashi sannan ki gaya masa in babu damuwa gobe da kamar wannan lokacin zan dawo ina son magana dashi" ta amsa masa da insha Allah, sai ya dauko daurin kudi ya ajiye akan shimfidar yace "gashi ki sayi sweet, dan naga alamar kina da kwadayi"
Ranar Ruqayyah bata iya bacci ba. Tana ta sakawa da warwarewa.
Washegari ya dawo kamar yadda yayi alkawari. Baba kuma already yana zaune yana zamn jiransa kuma ya yanke shawarar abinda zai gaya masa, danda aka aiko ya zo sai Baba ya saka Sulaiman ya shimfida musu tabarma a waje daga gefe inda mutane ba zasu dame su ba, sannan ya fita gurinsa.
Ganin haka yasa Ruqayyah ta kira Zunnur ta tambaye shi a inda suke, ita kuma ta tafi dai inda suke daga cikin gida tayi shimfida ta zauna tana yanke farcenta. Kawai haka nan taji zuciyarta tana son taji maganar da zasu yi.
A waje Hassan ne tare da Jabir, yaso Hussain yazo du taho tare amma sai ya kirkiri wani excuse ya kawo amma Hassan ya fahimci zuwa ne baya son yi kuma yaji babu dadi. Bayan sun gaisa cikin mutunci da girmama juna, sun kuma yo doguwar godiya a bisa taimakon da aka yiwa Hassan a gidan sai Jabir ya shigar da maganar kudirin Hassan na neman izinin fara neman auren Ruqayyah.
Baba ya masu kudurin su cikin nuna jin dadin wannan karramawar amma kuma sai yace "amma wani hanzari ba gudu ba, ni ba zan boye maka ba tun ranar dana fara ganinka naji zuciya ta tana sonka, naji a raina ina ma dai kai dana ne, kuma yanzu zanji dadi sosai idan ka zamo dan nawa wato in ka auri yata, sai dai, in har ka amince ina son ka chanza daga Ruqayyah ka nemi Sumayya"
Ruqayyah ta dago kai daga yankan farcen ta, ba tare da ta ce komai ba ta mike ta tafi daki tana jin zuciyarta ta zama tamkar dunkulallen garwashin wuta.
Wannan littafin na kudi ne, duk mai son siya tayi wa wannan number din magana 08067081020
08067081020Episode thirteen: The Strategy