Sashe 4
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan sun gama sun shiga mota ne yace "bayan wannan kuma sai na fulawa ne zai biyo baya. Shine abinda zai kaini Beijing gobe saboda injinan da nake son siyowa na harkar noma da gyaran alkama har zuwa na sarrafa ta zuwa fulawa duk anyo su sabon design, munyi magana dasu sun turo min hotunan su na gani shine nake so in je ayi launching dinsu a gaba na, injinan suna zuwa *H & H Flour Mills* zai tashi. Kasan Sawun dangote nake takawa" ya karasa cikin sigar tsokana, Hassan ya dauke kansa gefe yana driving dinsa hankali a kwance, amma idanunsa sun nuna cewa tunani yake da yawa a zuciyar sa, ba tare da Hussain ya lura ba ya dauko wata magazine yana bubbudewa da sauri sauri har yazo inda yake so sannan ya nuno wa Hassan "there! Ya kaga wannan babyn?" Hassan yayi wa motar da take cikin page din magazine din kallo daya ya dauke kai gefe yace "ita ce sabuwar da za'a chanza?" Hussain ya ajiye magazine din yace "noooo, ni da akwai wadda nake jira, har yanzu basu sake ta ba, wannan Gimbiya ta nake so inyi wa kyautar ta ranar birthday dinta" Hassan yayi saurin jefa masa wani kallo yace "kyauta? Hussain me yake damunka ne? Anya kuwa ka duba kudin motar nan?" Hussain yayi dariya yace "na gani mana mr tsimilmila. Fatima fa zan bawa, wannan ba komai bane ba indai a kanta ne"
Hassan ya girgiza kansa yace "Hussain. Naga alamar yarinyar nan ta kwace min gurina tun kafin ta shigo a zuciyar ka. Ina jin in akayi auren nan in ina son ganin ka sai na sayi form a gurin ta na cike" Hussain ya sake dariya yana kara kwanciya a kan kujerar sa, ya lumshe ido sannan yace "ba a haife ta ba ba kuma za'a haife ta ba. Yarinyar da zata raba ni da kai bata zo duniya ba ba kuma zata zo ba." Hassan yace "kana raina power ta mata Hussain. Shaidan da kansa ya ce yana tsoron kaidin mata ballantana mu da bamu san ma me duniyar take ciki ba. Mace tana iya raba tsakanin uwa da danta, ko tsakanin uba da yayansa, ballantana mu da muke brothers" Hussain yana taping hannunsa a kan cinyarsa yace "yanzu so kake in rabu da ita kenan?" Hassan yace "no, ba haka nake nufi ba, just be careful, be very careful akan mata" Hussain yayi murmushi yace "mr be careful. I am being careful ai, I have always been. Yarinyar nan fa shekarun mu uku, almost hudu tare da ita, duk wani abu nata daya kamata in sani na riga na sani, wanda ban sani ba kuma in an yi bikin mun shiga daga ciki zan sani" ya karashe maganar da dariya a muryar sa, Hassan ya bata rai yace "kasan problem dinka? Babban problem dinka a rayuwa shine komai a gurin ka abin wasa ne, komai a gurin ka is not serious, ita kuma rayiwa ba haka take ba"
Hussain ya dago kai yana kallon sa yace "ka san wani abu Hassan? Ita rayuwa nan guda daya ce, shi ran nan nan guda daya ne. In ya kare babu refilling. So ko dai kayi enjoying rayuwarka kafin ta tafi ta barka ko kuma kayi spending your entire life being careful ba tare daka mori all the goodies of the life ba, sai kawai rana daya kaga time ya kare maka a lokacin da kake tsakiya da tsara abubuwan da zaka yi nan gaba. What we have is today, what we are sure of is now, ba ayi mana alkawarin gobe ba. Zata iya kasancewa ina bude kofar motar nan zan fita mota tazo tabi ta kaina in mutu and that will be the end of me, babu abinda zai rage nawa sai memories na abinda na aikata, abinda na aikata ba wai abinda na zauna ina ta tunani ina planning cewa zan aikata sati mai zuwa ko wata mai zuwa ko kuma shekara mai xuwa ba. Bani da tabbas din zan kai wannan lokacin. Kuma ba zan iya chanza komai na daga kaddarar rayuwata ba so why worry? In na tafi bayan aiyukana da zanje in tarar a can abinda zan bari a duniya bayan memory na a zuciyoyin masoyana sai kuma sunana. And that's what am working on. Ina so in kafa H &H irin kafuwar da zai jima kafin sunansa ya goge a garin nan, ina so kuma inyi aure, auren nan daga zuriya mai karfi irin zuriyar masarautar kano, in hada jini dasu in samu yaya yadda zan bar bayana. Wannan shine burina, wannan kawai shine burina"
Hassan yayi packing motar a compound din gidan su sannan ya juyo yana kallon Hussain yace "nima duk ina da wadannan burikan Hussain, musamman burin aure da samun zuri'a kafin barin duniya, amma ni ban damu da familyn da zan hada zuri'a da su ba, ni dai fatana kawai shine in samu mace ta gari, mai kyawawan halayya, mai addini, wacce duniya sam bata gabanta balle abinda yake cikinta, reserved, wacce ba zata damu da abinda nake dashi ba balle abinda zan bata. Mai zurfin tunani, mai ilimin addini dana boko, Wacce......" Hussain ya daga hannunsa yace "in short, kafi son ka samu mace mai irin halayen ka.....boring.....to bara kaji, Gimbiya ta ma tana da duk wadannan characters din daka lissafa. But wait a second...." Ya matso da fuskar sa kusa da tashi yana kare masa kallo yace "wannan dogon lissafin da kake yi gaya min? Ta samu ne?" Hassan ya dungure masa goshi yace "tukunna dai, still searching..." Hussain yayi tagumi dramatically da hannu daya yace "still thinking about it... Planning... thinking and re planning.... Malam if you want to do something, do it now" Hassan ya fito daga motar yana cewa "sai kayi tayi yanzu din ai, gobe kuma kazo kana nadama" Hussain ya fito shima yana cewa "gwara inyi yanzun tunda bani da tabbas din zan kai gobe. In ma nayi nadamar a goben sai in sake yin wani".
A palo suka tarar da Aunty da yammatan ta ana ta hira, mostly hirar jami'a da Zulaihat take shirye shiryen tafiya, Nafisa tana ta bata tsoro akan irin wahalar da ake sha ita kuma tana korafin bata son zuwa, nan suma suka shiga cikin hirar Hassan ya shiga team din tsokanar Zulaihat Hussain kuma ya jawo ta jikinsa yana lallashinta. "Kinga autar Aunty, kije kiyi semester daya, in kika ji bata yi miki ba kina dawowa ki gaya min shikenan kin daina ta, sai ki zabi duk makarantar da kike so koda kasar waje ne zan kaiki. Ita rayuwar nan mai sauki ce, babu wani takura a cikin ta".
Washegari da sassafe Hussain ya tafi kano zance gurin Gimbiya. A jirgi ya tafi, dan haka cikin yan mintina ya isa kuma ya zarce direct zuwa fada ina Gimbiya Fatima ta aiko aka tarye shi aka kai shi masaukin da ake saukar baki irinsa sannan aka cika masa gabansa da kayayyakin abincin karin kumallo tunda tasan bai karya ba kuma tasan sauri yake yi dan tasan da tafiyar da zaiyi a yau. Kusan komai na Hussain Gimbiya Fatima ta sani.
Sai dai a bangaren Hussain din shi ba wai abincin ne a gabansa ba duk kuwa da cewa kamshin abincin ya gama cika masa ciki ya kuma tayar masa da yunwar da take kwakular hanjinsa, amma shi abinda yake gabansa shine ganin fuskar gimbiyar tasa, dan haka ya dora idanuwansa a kofar da yasan tanan zata fito, a haka har sai da ta fito din, sai ya samu knsa da mikewa tsaye yana yarfar da hannayensa, fiskarsa dauke da madaukakin murmushi wanda ya samu tarya da makamancinsa daga fuskarta.
Gimbiya Fatima diya ce a gurin maimartaba Sarkin Kano na wancan lokacin, kyakkyawa ce, mai kyakkyawan jiki wanda yaji komaida ake bukata a jikin mace. Hutu, gata, ilimi, mulki sun gama ratsa duk wata gaba ta jikinta. Kallo daya zaka yi mata zaka fahimci cewa yar sarauta ce ba wai sai an gaya maka ba kamar yadda magana day azata fada maka zaka fahimci cewa mai ilimi ce ita ba sai anyi maka bayani ba. Hanklain ta da nutsuwarta ya saka babanta yayi burin had ta aure da wani sarkin ko kuma wani dan sarkin dan ya karfafa karfin masarautar sa amma Fatima already idanuwanta suna kan Hussain. Dole mahaifinta ya bawa Hussain dama, tare kuma da fatan cewa ba zai bashi kunya ba.
Sun hadu ne a airport, Hussain ya dawo daga daya daga cikin tafiye tafiyen sa ita kuma zata kaiwa yaruwarta da take aure a Egypt ziyara. Yana cikin waya da Hassan bai gani ba suka yi karo, wayarsa ta fadi ita kuma jakar hannunta ta fadi tarkace ciki suka zube kasancewar jakar ba'a rufe take ba. Da sauri ya sunkuya ya tattaro mata kayayyakin ta ya zuba mata a jakar shima ya dauki wayarsa,a ransa yana saka rn zata sunkuyo su debe tare tunda ba laifinsa bane shi kaɗai, amma bata yi haka ba. Sai da ya gama ya mike zai mika mata sannan ya kalli fuskarta kuma a lokaci daya yasan cewa she is the one. Kuma kallo daya yayi mata yasan cewa ba zata kula shi ba, ko sunan ta ba zata gaya mishi ba ballantana phone number dan haka sai yayi dabara ya dauke wayarta ita kuma ya saka mata tasaa cikin jakarta. Ya mika mata tare da cewa "am sorry" sai data jima kafin ta motsa bakinta tace "it's okay" sannan without a second look ta juya tayi tafiyar ta.
Shi kam zuciyarsa fal murna ya fito daga airport din, sai daya fito sannan ya tuna cewa bai gaya wa abokin sa da yazo kano gurinsa cewa gashi nan yazo ba kuma gashi yayi musayar wayarsa, a dolensa ya nemi taxi.
Tunda ya koma kaduna yake kiran layin wayarsa amma shiru, sai tunani yazo masa cewa maybe kasar ta bari dan haka babu network. Option daya da yake dashi shine ya jira a kira ta ko kuma ita tayi amfani da wani layin ta kira layinta, amma shima shiru. Gashi kuma wayar tata da pin ballantana ya bude shi yayi kira da number dinta.
Hassan ya girgiza kansa yace "Hussain. Naga alamar yarinyar nan ta kwace min gurina tun kafin ta shigo a zuciyar ka. Ina jin in akayi auren nan in ina son ganin ka sai na sayi form a gurin ta na cike" Hussain ya sake dariya yana kara kwanciya a kan kujerar sa, ya lumshe ido sannan yace "ba a haife ta ba ba kuma za'a haife ta ba. Yarinyar da zata raba ni da kai bata zo duniya ba ba kuma zata zo ba." Hassan yace "kana raina power ta mata Hussain. Shaidan da kansa ya ce yana tsoron kaidin mata ballantana mu da bamu san ma me duniyar take ciki ba. Mace tana iya raba tsakanin uwa da danta, ko tsakanin uba da yayansa, ballantana mu da muke brothers" Hussain yana taping hannunsa a kan cinyarsa yace "yanzu so kake in rabu da ita kenan?" Hassan yace "no, ba haka nake nufi ba, just be careful, be very careful akan mata" Hussain yayi murmushi yace "mr be careful. I am being careful ai, I have always been. Yarinyar nan fa shekarun mu uku, almost hudu tare da ita, duk wani abu nata daya kamata in sani na riga na sani, wanda ban sani ba kuma in an yi bikin mun shiga daga ciki zan sani" ya karashe maganar da dariya a muryar sa, Hassan ya bata rai yace "kasan problem dinka? Babban problem dinka a rayuwa shine komai a gurin ka abin wasa ne, komai a gurin ka is not serious, ita kuma rayiwa ba haka take ba"
Hussain ya dago kai yana kallon sa yace "ka san wani abu Hassan? Ita rayuwa nan guda daya ce, shi ran nan nan guda daya ne. In ya kare babu refilling. So ko dai kayi enjoying rayuwarka kafin ta tafi ta barka ko kuma kayi spending your entire life being careful ba tare daka mori all the goodies of the life ba, sai kawai rana daya kaga time ya kare maka a lokacin da kake tsakiya da tsara abubuwan da zaka yi nan gaba. What we have is today, what we are sure of is now, ba ayi mana alkawarin gobe ba. Zata iya kasancewa ina bude kofar motar nan zan fita mota tazo tabi ta kaina in mutu and that will be the end of me, babu abinda zai rage nawa sai memories na abinda na aikata, abinda na aikata ba wai abinda na zauna ina ta tunani ina planning cewa zan aikata sati mai zuwa ko wata mai zuwa ko kuma shekara mai xuwa ba. Bani da tabbas din zan kai wannan lokacin. Kuma ba zan iya chanza komai na daga kaddarar rayuwata ba so why worry? In na tafi bayan aiyukana da zanje in tarar a can abinda zan bari a duniya bayan memory na a zuciyoyin masoyana sai kuma sunana. And that's what am working on. Ina so in kafa H &H irin kafuwar da zai jima kafin sunansa ya goge a garin nan, ina so kuma inyi aure, auren nan daga zuriya mai karfi irin zuriyar masarautar kano, in hada jini dasu in samu yaya yadda zan bar bayana. Wannan shine burina, wannan kawai shine burina"
Hassan yayi packing motar a compound din gidan su sannan ya juyo yana kallon Hussain yace "nima duk ina da wadannan burikan Hussain, musamman burin aure da samun zuri'a kafin barin duniya, amma ni ban damu da familyn da zan hada zuri'a da su ba, ni dai fatana kawai shine in samu mace ta gari, mai kyawawan halayya, mai addini, wacce duniya sam bata gabanta balle abinda yake cikinta, reserved, wacce ba zata damu da abinda nake dashi ba balle abinda zan bata. Mai zurfin tunani, mai ilimin addini dana boko, Wacce......" Hussain ya daga hannunsa yace "in short, kafi son ka samu mace mai irin halayen ka.....boring.....to bara kaji, Gimbiya ta ma tana da duk wadannan characters din daka lissafa. But wait a second...." Ya matso da fuskar sa kusa da tashi yana kare masa kallo yace "wannan dogon lissafin da kake yi gaya min? Ta samu ne?" Hassan ya dungure masa goshi yace "tukunna dai, still searching..." Hussain yayi tagumi dramatically da hannu daya yace "still thinking about it... Planning... thinking and re planning.... Malam if you want to do something, do it now" Hassan ya fito daga motar yana cewa "sai kayi tayi yanzu din ai, gobe kuma kazo kana nadama" Hussain ya fito shima yana cewa "gwara inyi yanzun tunda bani da tabbas din zan kai gobe. In ma nayi nadamar a goben sai in sake yin wani".
A palo suka tarar da Aunty da yammatan ta ana ta hira, mostly hirar jami'a da Zulaihat take shirye shiryen tafiya, Nafisa tana ta bata tsoro akan irin wahalar da ake sha ita kuma tana korafin bata son zuwa, nan suma suka shiga cikin hirar Hassan ya shiga team din tsokanar Zulaihat Hussain kuma ya jawo ta jikinsa yana lallashinta. "Kinga autar Aunty, kije kiyi semester daya, in kika ji bata yi miki ba kina dawowa ki gaya min shikenan kin daina ta, sai ki zabi duk makarantar da kike so koda kasar waje ne zan kaiki. Ita rayuwar nan mai sauki ce, babu wani takura a cikin ta".
Washegari da sassafe Hussain ya tafi kano zance gurin Gimbiya. A jirgi ya tafi, dan haka cikin yan mintina ya isa kuma ya zarce direct zuwa fada ina Gimbiya Fatima ta aiko aka tarye shi aka kai shi masaukin da ake saukar baki irinsa sannan aka cika masa gabansa da kayayyakin abincin karin kumallo tunda tasan bai karya ba kuma tasan sauri yake yi dan tasan da tafiyar da zaiyi a yau. Kusan komai na Hussain Gimbiya Fatima ta sani.
Sai dai a bangaren Hussain din shi ba wai abincin ne a gabansa ba duk kuwa da cewa kamshin abincin ya gama cika masa ciki ya kuma tayar masa da yunwar da take kwakular hanjinsa, amma shi abinda yake gabansa shine ganin fuskar gimbiyar tasa, dan haka ya dora idanuwansa a kofar da yasan tanan zata fito, a haka har sai da ta fito din, sai ya samu knsa da mikewa tsaye yana yarfar da hannayensa, fiskarsa dauke da madaukakin murmushi wanda ya samu tarya da makamancinsa daga fuskarta.
Gimbiya Fatima diya ce a gurin maimartaba Sarkin Kano na wancan lokacin, kyakkyawa ce, mai kyakkyawan jiki wanda yaji komaida ake bukata a jikin mace. Hutu, gata, ilimi, mulki sun gama ratsa duk wata gaba ta jikinta. Kallo daya zaka yi mata zaka fahimci cewa yar sarauta ce ba wai sai an gaya maka ba kamar yadda magana day azata fada maka zaka fahimci cewa mai ilimi ce ita ba sai anyi maka bayani ba. Hanklain ta da nutsuwarta ya saka babanta yayi burin had ta aure da wani sarkin ko kuma wani dan sarkin dan ya karfafa karfin masarautar sa amma Fatima already idanuwanta suna kan Hussain. Dole mahaifinta ya bawa Hussain dama, tare kuma da fatan cewa ba zai bashi kunya ba.
Sun hadu ne a airport, Hussain ya dawo daga daya daga cikin tafiye tafiyen sa ita kuma zata kaiwa yaruwarta da take aure a Egypt ziyara. Yana cikin waya da Hassan bai gani ba suka yi karo, wayarsa ta fadi ita kuma jakar hannunta ta fadi tarkace ciki suka zube kasancewar jakar ba'a rufe take ba. Da sauri ya sunkuya ya tattaro mata kayayyakin ta ya zuba mata a jakar shima ya dauki wayarsa,a ransa yana saka rn zata sunkuyo su debe tare tunda ba laifinsa bane shi kaɗai, amma bata yi haka ba. Sai da ya gama ya mike zai mika mata sannan ya kalli fuskarta kuma a lokaci daya yasan cewa she is the one. Kuma kallo daya yayi mata yasan cewa ba zata kula shi ba, ko sunan ta ba zata gaya mishi ba ballantana phone number dan haka sai yayi dabara ya dauke wayarta ita kuma ya saka mata tasaa cikin jakarta. Ya mika mata tare da cewa "am sorry" sai data jima kafin ta motsa bakinta tace "it's okay" sannan without a second look ta juya tayi tafiyar ta.
Shi kam zuciyarsa fal murna ya fito daga airport din, sai daya fito sannan ya tuna cewa bai gaya wa abokin sa da yazo kano gurinsa cewa gashi nan yazo ba kuma gashi yayi musayar wayarsa, a dolensa ya nemi taxi.
Tunda ya koma kaduna yake kiran layin wayarsa amma shiru, sai tunani yazo masa cewa maybe kasar ta bari dan haka babu network. Option daya da yake dashi shine ya jira a kira ta ko kuma ita tayi amfani da wani layin ta kira layinta, amma shima shiru. Gashi kuma wayar tata da pin ballantana ya bude shi yayi kira da number dinta.