Sashe 37
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Amma sai me, sai taga an wuce katon an tafi ga an karamin, sai a lokacin ta lura cewa kofofin katon a rufe suke fitulun sa a kashe karamin kum komai a bude yake tana iya hango mutane a ciki ma. Ta juya side din Aunty, zuciyarta tan agaya mata t tunawa Aunty cewa anyi mistake ba nan ne gidan Hassan ba nan gidan Hussain ne. Amma sai taji aunty tana cewa "alhamdulillah Ruqayyah Allah y kawo ki gidan ki lafiya, sai kiyi masa godiya sannan ki fito da kafar dama tare da bismillah" sai wata zuciyar ta gaya mata to ko nan part din Aunty da yara ne aka kawo ta ayi mata fada sannan a kaita part dinta? Yes, that must be it.
Ta fito da bismillah kamar yadda Aunty tace, sannan Hajiyan Kano ta kama hannayenta tana tafiya da ita yan uwanta ta suka rako ta suna take musu baya. A palo ne taga hoton su ita da Hassan wanda suka dauka last week yace enlargement za'a yi musu a kafe musu a palon su. Kafafuwanta taji sun kasa daukan ta, jikinta yayi sanyi kwakwalwar ta tana neman toshewa. Ta tafi kamar zata fadi, Aunty tayi saurin riketa "subhanallah. Ruqayyah lafiya? Sai ta taba wuyanta, wuyan da lokaci daya da dauki mugun zafi ta ce "ya salam, jikinta zafi, dama bata jin dadi?" Goggo Habibah yayar Inna Ade tace "anya kuwa, kamar lafiyar ta kalau" Ruqayyah ta fara kuka a hankali irin wanda sheshsheka ce kawai take fitowa, tana jin tamkar duniya ce gabaki daya take ruguzo mata aka, tana jin kamar duk mafarkanta suna tarwatsewa a gaban idonta. Zuciyarta tana rada mata wata magana, wata mummunar magana.
Hussain shine CEO na H and H ba Hassan ba.
And that explains alot of things. Tayi saurin tana girgiza kanta kamar mai fada fa zuciyar tata. No, no, no. Ta ringa maimaitawa
She felt her dreams shattering. Ta sake girgiza kanta trying to comport herself, wani barin na zuciyarta yana gaya mata "ba haka bane ba, kinsan Hassan da makale aljihu, shine zai zabi gina karamin gida ba wai dan ba shine mai Company ba" sai daya barin yace "kuma sai yabar kaninsa ya gina babban gidan da ya fi nashi?" Nan take sautin kukanta ya karu
Kuka take yi kamar ranta zai fita, Hassan ya yaudareta yaci amanar ta, yayi mata karya dan ya aureta. Zuciyarta zafi take mata, zuciyarta ciwo take yi mata, anya kuwa ba ciwon zuciya ne zai kama ta ba?
Tana jin maganganun mutane a kusa da ita, yawancin su hakuri suke bata, sama sama kuma tana jin dariyar wasu. Sai ta fahimci sun dauka kukan barin gida take yi. "Kaji yarinyar nan, har muna yabonta muna cewa yarinya karama amma bata yi kuka ba ashe kukan zuci take yi sai yanzu zata yi na fili" "kiyi hakuri Ruqayyah, muma duk da haka muka sossoma wai kuturu yaga mai kyasbi" suka kwashe da dariya wasu daga ciki suka yi guda, "ni sanda za'a kaini gidan nawa mijin ma guduwa nayi, sai da akayi ta nema na aka rasa har aka hakura sannan na dawo, ina dawowa kuwa aka kama ni aka kaini" aka sake wata dariyar.
Ruqayyah taji tamkar ta samu bindiga Ak47 duk ta bi su da bullet goma goma. Dan dai tasan sun fi ta karfi ne da babu Abinda zai hana ta tashi ta rufe duk mutanen gurin da duka. But bata son ta bata rawar ta da tsalle, zargi ne ai kawai take yi, bata tabbatar ba lokacin taji muryar Nafisa a kusa da ita, "kiyi hakuri kiyi shiru kinji yayata kar kanki yazo yana yi miki ciwo, kinga duk su Aunty tsokanar ki suke yi" sai itama tayi dariyar sannan kuma ta juya tana waigen neman Sumayya tace "ina Sumayya? Wata kila ita zata iya rarrashinta"
"Kaga Adam kazo ka mayar dani inda ka dauko ni ko kuma ka kaini inda zaka kaini, ka daina yawo dani a titi" yace "sai kinyi dariya tukunna. Haka kawai dan Ruqayyah tayi aure sai ki zauna kiyi ta kuka har idonki yayi wannan kumburin? Kinga fuskarki kuwa?" ta kuma hade rai "ni bana cikin mood din dariya, dan Allah ka rabu dani" yace "in rabu dake fa kika ce? Kamar fa kina nufin in rabu da wani sashe na jikina in daina amfani dashi kenan fa? Kina ganin haka zai yiwu?" Ta kara hade rai "kaga fa za'a neme ni a can, in aka fahimci yawo na tafi kuma za'a yi min fada. Dan Allah ka kaini, ni jikina bani yake yi kamar Ruqayyah tana nema na" yace "Ruqayyah da aka kai dakin miji, maybe ma suna can suna zuba soyayya ita da mijin ta ke kina nan kin hana ni ganin hakorinki" tace " koma dai me take yi ni ka kaini in ganta, dan Allah" yace "sai kin yi dariya" ta sake hade rai yace "Please, pretty please!" Ta dauke kanta gefe daya sai ya saki stirring ya hade hannayensa alamar roko "Please Please Please" da sauri tace "Adam zaka yar da mu fa?" Yace "kiyi dariya to" ba shiri ta yangare baki daga gani kasan dariyar karya ce, ya kama stirring yana dariya yace "bara dai in kaiki, ba dan halinki ba" sannan ya juya kan motar zuwa gidan su Hussain.
Suna shiga idanunta suka sauka a kan gidan Hussain, ta saki baki tana kallo sai taga kuma gidan Hassan, sannan sai taga sunyi packing a kofar Hassan, ta juya tana kallon gidan Hussain sai kuma ta sake dawowa ta kalli gidan Hassan, tagan shi a bude mutane suna ta hada hada, daga ciki ta jiyo an rangada guda.
Gabanta ya fadi, ta juyo da budaddun idanuwa tana kallon Adam fuskarta da alamun tambaya. Yace "can gidan oga Hussain ne, he Calls himself "dangoten Kaduna" . Nan shine gidan Ruqayyah, gidan oga Hassan kenan. Nan zaki shiga". Sumayya bata jira sauran wani karin bayani ba ta bude kofar mota ta fita da sauri, ko rufewa bata tsaya tayi ba, yace "hey, babu thank you balle goodnight? Kin bar jakarki a ciki" bata ko kalle shi ba ta shige gidan da sauri.
Tun a bakin kofa ta jiyo gunjin kulan Ruqayyah, gabanta ya fadi. Innalillahi, wannan wanne irin rashin ta ido Ruqayyah take nuna wa? Ba tare da tunanin komai ba ta ratsa mutanen da suke palon har zuwa gaban Ruqayyah da har yanzu take durkushe a kasa tana ta risgar kuka da iyakacin karfin ta. Nafisa tace "alhamdulillah, ga Sumayyan nan ma, zo ki yi mata magana ko zata yi shiru" Sumayya ta durkusa a gaban Ruqayyah sannan ta tallafi fuskarta a hannayenta tana jin yadda fatarta tayi zafi, ba tare data ce mata komai ba sai ta kama ta ta mikar da ita tsaye ta rungume ta a jikinta ta fara tafiya tace "ina za'a kaita?" Nan take aka yi mata jagora zuwa Bedroom din Ruqayyah da yake sama. Ta zaunar da ita a bakin gado kamar yadda ake zaunar da ko wacce amarya sannan ta goge mata hawayen fuskarta ta ja mayafi ta rufe mata fuskarta ta kuma zauna a kusa da ita ta rike hannun ta a cikin nata, a hankali Ruqayyah tace "Sumayya, Hassan ya yaudare ni" Sumayya tayi shiru bata bata amsa ba saboda mutane da suka fara shigowa, suna ta tsokanar Ruqayyah da sunan amarya mai kuka, yan uwansu da suka kawo ta suka yi mata sallama abokan wasa suna tsokanar ta, kusan kuma duk wanda yazo yi mata sallama sai ya yabi gidanta "Ruqayyah ki godewa Allah, kinga kyawun gidan ki kuwa? Masha Allah. Wannan miji naki ba karamin sonki yake ba, ki rike kayan ki hannu bibbiyu Allah kuma ya baku zaman lafiya" Sumayya ce mai amsawa da ameen.
Sai da aka ragu saura kawayensu da suke palon kasa suna ta dauke dauken hotuna dan a samu na burga sannan Sumayya ta rufe kofar dakin ta dawo kusa da Ruqayyah ta zauna tace "Ruqayyah me nene hakan kika so ki aikata? Wannan wanne irin abin kunya kika so ki jawo wa kanki ki jawo mana?" Ruqayyah ta bude fuskarta data kumbura cikin dasashshiyar murya tace "abin kunya? Abin kunya kike magana akai? Shin baki kalli gidan can ba? Kin tambayi kanki gidan waye kuwa?" Sumayya tace "ba kaina na tambaya ba, mai motar daya kawo ni na tambaya kuma ya gaya min cewa gidan Hussain ne and so what? Me yasa za ki juya ki kalli gidan Hussain bayan ga gidan Hassan kina cikin sa? Me yasa ba zaki kalli abinda yake hannun kin a matsayin mallakin ki ba sai kike juyawa kina kallon abin hannun wani? Ba ki ji abinda yanuwan mu suke fada ba? Cewa badu taba ganin gidan da yake da kyawun naki ba? Ni ma kuma haka, ban taba shiga gida mai kyan wannan ba, ban taba zama a kan gadon mai kyan wannan ba. Which of the favors of your God do you deny?"
Ta fito da bismillah kamar yadda Aunty tace, sannan Hajiyan Kano ta kama hannayenta tana tafiya da ita yan uwanta ta suka rako ta suna take musu baya. A palo ne taga hoton su ita da Hassan wanda suka dauka last week yace enlargement za'a yi musu a kafe musu a palon su. Kafafuwanta taji sun kasa daukan ta, jikinta yayi sanyi kwakwalwar ta tana neman toshewa. Ta tafi kamar zata fadi, Aunty tayi saurin riketa "subhanallah. Ruqayyah lafiya? Sai ta taba wuyanta, wuyan da lokaci daya da dauki mugun zafi ta ce "ya salam, jikinta zafi, dama bata jin dadi?" Goggo Habibah yayar Inna Ade tace "anya kuwa, kamar lafiyar ta kalau" Ruqayyah ta fara kuka a hankali irin wanda sheshsheka ce kawai take fitowa, tana jin tamkar duniya ce gabaki daya take ruguzo mata aka, tana jin kamar duk mafarkanta suna tarwatsewa a gaban idonta. Zuciyarta tana rada mata wata magana, wata mummunar magana.
Hussain shine CEO na H and H ba Hassan ba.
And that explains alot of things. Tayi saurin tana girgiza kanta kamar mai fada fa zuciyar tata. No, no, no. Ta ringa maimaitawa
She felt her dreams shattering. Ta sake girgiza kanta trying to comport herself, wani barin na zuciyarta yana gaya mata "ba haka bane ba, kinsan Hassan da makale aljihu, shine zai zabi gina karamin gida ba wai dan ba shine mai Company ba" sai daya barin yace "kuma sai yabar kaninsa ya gina babban gidan da ya fi nashi?" Nan take sautin kukanta ya karu
Kuka take yi kamar ranta zai fita, Hassan ya yaudareta yaci amanar ta, yayi mata karya dan ya aureta. Zuciyarta zafi take mata, zuciyarta ciwo take yi mata, anya kuwa ba ciwon zuciya ne zai kama ta ba?
Tana jin maganganun mutane a kusa da ita, yawancin su hakuri suke bata, sama sama kuma tana jin dariyar wasu. Sai ta fahimci sun dauka kukan barin gida take yi. "Kaji yarinyar nan, har muna yabonta muna cewa yarinya karama amma bata yi kuka ba ashe kukan zuci take yi sai yanzu zata yi na fili" "kiyi hakuri Ruqayyah, muma duk da haka muka sossoma wai kuturu yaga mai kyasbi" suka kwashe da dariya wasu daga ciki suka yi guda, "ni sanda za'a kaini gidan nawa mijin ma guduwa nayi, sai da akayi ta nema na aka rasa har aka hakura sannan na dawo, ina dawowa kuwa aka kama ni aka kaini" aka sake wata dariyar.
Ruqayyah taji tamkar ta samu bindiga Ak47 duk ta bi su da bullet goma goma. Dan dai tasan sun fi ta karfi ne da babu Abinda zai hana ta tashi ta rufe duk mutanen gurin da duka. But bata son ta bata rawar ta da tsalle, zargi ne ai kawai take yi, bata tabbatar ba lokacin taji muryar Nafisa a kusa da ita, "kiyi hakuri kiyi shiru kinji yayata kar kanki yazo yana yi miki ciwo, kinga duk su Aunty tsokanar ki suke yi" sai itama tayi dariyar sannan kuma ta juya tana waigen neman Sumayya tace "ina Sumayya? Wata kila ita zata iya rarrashinta"
"Kaga Adam kazo ka mayar dani inda ka dauko ni ko kuma ka kaini inda zaka kaini, ka daina yawo dani a titi" yace "sai kinyi dariya tukunna. Haka kawai dan Ruqayyah tayi aure sai ki zauna kiyi ta kuka har idonki yayi wannan kumburin? Kinga fuskarki kuwa?" ta kuma hade rai "ni bana cikin mood din dariya, dan Allah ka rabu dani" yace "in rabu dake fa kika ce? Kamar fa kina nufin in rabu da wani sashe na jikina in daina amfani dashi kenan fa? Kina ganin haka zai yiwu?" Ta kara hade rai "kaga fa za'a neme ni a can, in aka fahimci yawo na tafi kuma za'a yi min fada. Dan Allah ka kaini, ni jikina bani yake yi kamar Ruqayyah tana nema na" yace "Ruqayyah da aka kai dakin miji, maybe ma suna can suna zuba soyayya ita da mijin ta ke kina nan kin hana ni ganin hakorinki" tace " koma dai me take yi ni ka kaini in ganta, dan Allah" yace "sai kin yi dariya" ta sake hade rai yace "Please, pretty please!" Ta dauke kanta gefe daya sai ya saki stirring ya hade hannayensa alamar roko "Please Please Please" da sauri tace "Adam zaka yar da mu fa?" Yace "kiyi dariya to" ba shiri ta yangare baki daga gani kasan dariyar karya ce, ya kama stirring yana dariya yace "bara dai in kaiki, ba dan halinki ba" sannan ya juya kan motar zuwa gidan su Hussain.
Suna shiga idanunta suka sauka a kan gidan Hussain, ta saki baki tana kallo sai taga kuma gidan Hassan, sannan sai taga sunyi packing a kofar Hassan, ta juya tana kallon gidan Hussain sai kuma ta sake dawowa ta kalli gidan Hassan, tagan shi a bude mutane suna ta hada hada, daga ciki ta jiyo an rangada guda.
Gabanta ya fadi, ta juyo da budaddun idanuwa tana kallon Adam fuskarta da alamun tambaya. Yace "can gidan oga Hussain ne, he Calls himself "dangoten Kaduna" . Nan shine gidan Ruqayyah, gidan oga Hassan kenan. Nan zaki shiga". Sumayya bata jira sauran wani karin bayani ba ta bude kofar mota ta fita da sauri, ko rufewa bata tsaya tayi ba, yace "hey, babu thank you balle goodnight? Kin bar jakarki a ciki" bata ko kalle shi ba ta shige gidan da sauri.
Tun a bakin kofa ta jiyo gunjin kulan Ruqayyah, gabanta ya fadi. Innalillahi, wannan wanne irin rashin ta ido Ruqayyah take nuna wa? Ba tare da tunanin komai ba ta ratsa mutanen da suke palon har zuwa gaban Ruqayyah da har yanzu take durkushe a kasa tana ta risgar kuka da iyakacin karfin ta. Nafisa tace "alhamdulillah, ga Sumayyan nan ma, zo ki yi mata magana ko zata yi shiru" Sumayya ta durkusa a gaban Ruqayyah sannan ta tallafi fuskarta a hannayenta tana jin yadda fatarta tayi zafi, ba tare data ce mata komai ba sai ta kama ta ta mikar da ita tsaye ta rungume ta a jikinta ta fara tafiya tace "ina za'a kaita?" Nan take aka yi mata jagora zuwa Bedroom din Ruqayyah da yake sama. Ta zaunar da ita a bakin gado kamar yadda ake zaunar da ko wacce amarya sannan ta goge mata hawayen fuskarta ta ja mayafi ta rufe mata fuskarta ta kuma zauna a kusa da ita ta rike hannun ta a cikin nata, a hankali Ruqayyah tace "Sumayya, Hassan ya yaudare ni" Sumayya tayi shiru bata bata amsa ba saboda mutane da suka fara shigowa, suna ta tsokanar Ruqayyah da sunan amarya mai kuka, yan uwansu da suka kawo ta suka yi mata sallama abokan wasa suna tsokanar ta, kusan kuma duk wanda yazo yi mata sallama sai ya yabi gidanta "Ruqayyah ki godewa Allah, kinga kyawun gidan ki kuwa? Masha Allah. Wannan miji naki ba karamin sonki yake ba, ki rike kayan ki hannu bibbiyu Allah kuma ya baku zaman lafiya" Sumayya ce mai amsawa da ameen.
Sai da aka ragu saura kawayensu da suke palon kasa suna ta dauke dauken hotuna dan a samu na burga sannan Sumayya ta rufe kofar dakin ta dawo kusa da Ruqayyah ta zauna tace "Ruqayyah me nene hakan kika so ki aikata? Wannan wanne irin abin kunya kika so ki jawo wa kanki ki jawo mana?" Ruqayyah ta bude fuskarta data kumbura cikin dasashshiyar murya tace "abin kunya? Abin kunya kike magana akai? Shin baki kalli gidan can ba? Kin tambayi kanki gidan waye kuwa?" Sumayya tace "ba kaina na tambaya ba, mai motar daya kawo ni na tambaya kuma ya gaya min cewa gidan Hussain ne and so what? Me yasa za ki juya ki kalli gidan Hussain bayan ga gidan Hassan kina cikin sa? Me yasa ba zaki kalli abinda yake hannun kin a matsayin mallakin ki ba sai kike juyawa kina kallon abin hannun wani? Ba ki ji abinda yanuwan mu suke fada ba? Cewa badu taba ganin gidan da yake da kyawun naki ba? Ni ma kuma haka, ban taba shiga gida mai kyan wannan ba, ban taba zama a kan gadon mai kyan wannan ba. Which of the favors of your God do you deny?"