Sashe 75
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hassan yana zaune rike da hannun Hussain aka gama procedure din, doctor din yana nuna masa abinda yake gani yana kuma yi masa bayani, ya nuna masa ciwon da idonsa ya gani ya kuma gaya masa tun jiya da yayi wa Hussain manual exam ya fahimci cewa akwai ciwon da gaske, ganin hankalin Hassan ya tashi sosai sai ya kwantar masa da hankali ta hanyar gaya masa cewa ba wani problem bane ba tunda an yi detecting da wuri kuma akwai means na neman magani babu wani problem, ya gaya masa kuma yayi iyakacin kokarin sa na ganin ya kwantar wa da Hussain hankali dan lokuta da dama tashin hankali shi yake kashe patient ba wai ainahin ciwon ba. Ya kuma jaddada masa muhimmancin jin surgery da wuri "ita cancer tana spreading ne, tana kara yaduwa, in aka barta zata ci gaba kuma ba zata tsaya a hanjin kadai ba zata taba wadyu vital organs din da suke cikinsa. Dan haka I suggest ayi surgery as soon as possible. Daga anyi surgery an cire tumor din sai kuma a kashe surrounding area din da radiotherapy yadda in akwai saura ma zata mutu" Hassan ya gyada kansa yana assuring doctor din cewa kafin su bar kasar za'a yi surgery din. Ba zai bar kasar ba sai da healthy Hussain.
Sanda Hussain ya farka, Hassan ya gani a gefensa rike da hannun sa ya kwantar da kansa a jikin gadon da Hussain yake kwance idonsa a rufe. Hussain ya dago hannunsa ya dan taba fuskarsa yace "hey bro" Hassan yayi saurin bude kumburarrun jajayen idanuwan sa ya dora akan Hussain, sai yaga Hussain din yayi masa dariya yace "have you been crying?" Ya sake dariya "sai na gaya wa Ruqayyah mijinta rago ne" Hassan ya harare shi ya tashi ya shiga toilet ya wanke fuskarsa ya fito sai ya tarar dashi yana kokarin tashi zaune sannan ya zare drip din da aka saka masa. Ya kamashi yana kokarin kwantar dashi amma yaki kwanciya ya tashi yana cewa "ni yunwa nake ji wallahi, kamar anyi min sata a hanji na" sai kuma ya bude ido yana kallon Hassan yace "gaya min gaskiya, ko har sun yanke hanjin ne?" Sai kawai yayi dariya ya kama hanyar fita.
Hassan ya bishi amma yaki dawowa, sai da ya tuna masa da cewa rigar asibitin ce a jikin sa sannan ya dawo briefly ya mayar da kayansa ya kuma fita. A dole Hassan ya dauko takardun su da kuma wayoyin su ya biyo shi a baya. Sai da suka je gurin cin abinci suka zauna suna ci sannan Hussain yace "na san abinda doctor yace, you don't have to tell me, na riga na gaya maka dama kai ne baka yarda ba. Yanzu tunda ka yarda can we please go home? I have to get back to making that baby you know?"
Hassan ya dauke kansa gefe yace "babu wani home da zaka tafi, you are going to have a surgery next week. Na riga nayi filling takardu har na biya kudi" Hussain ya bude ido cikin mamaki yace "no, na riga na gaya maka am not going to go through that" ya ajiye spoon din hannunsa ya mike ya fice daga gurin. Hassan ya biya bill da sauri ya bishi a baya. Ya tarar dashi a hanya suka jera yana cewa "Hussain Please, doctor din nan fa yayi min bayani, ya nuna min komai a screen na gani ba wai wani guri ne mai yawa ba, yace da zarar sunyi surgery sun cire shikenan sai......." Hussain yace "sai ayi radiology a kashe gurin sannan chemotherapy dan a tabbbar komai ya mutu, after three months kuma sai in dawo a sake wani colonoscopy din a gani idan bata yi regrowing ba, idan kuma tayi sai a sake going through that same precess, a haka har sai hanjin ya kare yadda babu abinda za'a kuma yankewa, ko kuma in ta taba wani vital organ din, sai kuma abar mutum ya karasa mutuwa, yes I know about all the process and no am not going through that. Na gaya maka tun acan".
Haka suka yi ta fama har suka je hotel din da suka sauka, suna ziwa Hussain ya fara hada kaya yana zubawa a jaka Hassan kuma yana kashewa yana mayar wa gurin ajjiyar kaya, "waye ya gaya maka zata sake regrowing? Dan ta wasu tayi that doesn't mean taka ma zata yi. Doctor din fa yace tana stage 2, he is 90% sure cewa zai iya cire ta completely" Hussain yace "I am sorry but I don't believe him. Tunda za'a bashi kudin sa ya karbe ai zai fadi haka dama. Ni ba zan bari likitoci su mayar dani lab animal dinsu ba".
Hassan ya koma ya zauna yana kallon Hussain, he have been stubborn and strong headed tun suna yara, anty ma da kanta ta sha ba da labarin irin taurin kansa da yadda yake bata wahala kafin ta juya shi, in yasa kansa abu to kuwa sai da dabara kafin a iya hana shi. Sai ya dauko wayarsa yace "shikenan tunda kaki jin magana ta, bara in kira Fatima in gaya mata halin da ake ciki watakila in ita tayi maka magana zaka ji" sai Hussain ya tsaya daga hadan kayan da yake yi yana kallon Hassan yace "you won't do that, ai amana na baka maganar nan, kana nufin zaka karya alkawarin da kayi min na cewa ba zaka gaya wa kowa ba?" Hassan ya daga kafada yace "yes of course, idan har hakan yana nufin saving life dinka ne zanyi. Kuma try me ka gani idan ba da gaske nake ba" Hussain ya tsaya yana kallonsa, baiga alamar wasa a fuskarsa ba sai ya ajiye kayan hannunsa ya hau kan gado ya kwanta, sai kuma ya tashi ta shiga toilet yayo alwala ya fito ya tayar da sallah.
Hassan ya mike ya mammayar da kayan da Hussain ya baza, sannan shima yaje yayo alwalar ya fito ya tayar da tasa sallar.
Hussain ya hakura ya yarda za'a yi masa aiki amma sam babu walwala a fuskarsa, sai Hassan ya fahimci kamar aikin yafi damunsa a kan ciwon ma gabaki dayansa. A haka har aka gama preparation ya zama saura kwana daya ayi aikin sai suka tafi asibitin zasu kwana acan, a lokacin ne zuciyar Hassan ta karye yace da Hussain "ina ganin a fasa aikin nan Hussain, ni bana jin dadin yadda kake reacting to it ka ƙi kwantar da hankalin ka bayan kuma kai ba mai yawan tayar da hankali akan abu bane ba, ni duk sanyaya min jiki kake yi wallahi, na kasa fahimtar if am doing the right thing or not. Please bro, ka gaya min cewa ba wai takura maka zanyi ayi maka aikin nan ba, dan Allah ka gaya min" sai Hussain yayi masa murmushi yace "ba wai ka takura min bane Hassan, ba kuma na yarda bane saboda kayi threatening cewa zaka gaya wa Fatima ba, na yarda ne saboda kai, saboda ina so in faranta maka, saboda ina so kaji cewa you did your best kar kayi feeling cewa ka gaza gurin kula dani. But ina so kai ma kayi mini wani alkawari Hassan. Ina so kayi min alkawarin cewa wannan shine surgery na farko kuma na karshe da zaka saka ayi min akan wannan cutar" Hassan ya sunkuyar da kansa kasa, Hussain ya dago fuskarsa yana kallon idonsa yace "say it. Kace kayi min alkawari" Hassan ya karbe fuskarsa sannan yace "nayi alkawari. Kuma nasan ma wannan aikin akwai nasara a cikin sa, mun gaya wa Allah kuma ya dubi kokarin mu. Zamu samu nasara am sure" sai Hussain yayi murmushi yace "good" . Sai ya koma ya kwanta ya rufe idonsa har aka zo aka tafi dashi.
The surgery took 3 hours. A cikin 3 hours din nan Hassan sai da yayi nadamar da basu gaya wa kowa ba, at least da an taya su addu'a, dan ji yake yi kamar bakin sa shi kadai yayi kadan a addu'ar. A cikin awa ukun nan har wata irin rama yayi.
Yana tsaye aka fito da Hussain, aka tura shi recovery room, inda kuma anan ne zai cigaba da karbar treatment dinsa.
Wannan littafin na siyarwa ne, idan kin ganshi a wani gurin na sata ne, in kina son karanta halaliyar ki kiyi min magana ta wannan number din through WhatsApp 08067081020*The Email*
Washegarin da akayi aikin aka fara yiwa Hussain chemotherapy treatment tare kuma da radiation therapy, at the same time kuma ana monitoring warkewar gurin da aka yi masa aiki internal da external. It has not been easy on him duk da cewa Hassan yana tare dashi kuma likitocin suna kulawa dashi sosai, magana mai dadi, karfafa guiwa, da tabbatar da cewa he is comfortable. Shi kansa yasan ya rame, tun kafin ayi aikin kuma ya rane din dan Fatima tasha yi masa mita a waya cewa ya rame, tun yana kakkaucewa har dai ya daina kiran ta video call itama kuma inta kira baya dauka sai yace mata phone dinsa ta samu matsala.
A haka har ya fara jin dadin jikinsa, su kansu doctors din suna yabawa da yadda jikin nasa yayi kyau, ya rage yin amai sosai wanda yana daga cikin side effect na chemotherapy kuma shi yake saka rama, saboda jikinsa ya fara sabawa da magungunan da ake bashi. Sai kuma ya dage da cin abinci, ya kuma cire damuwa a ransa nan da nan ya kara murmure wa. An gama radiation therapy din, magunguna ne kawai yake sha dan haka ya fara maganar yana son ya tafi gida. Da farko doctor din yaki yarda, ya fi son ya kara kwanaki ciwonsa ya kara warkewa duk da cewa ba zasu tabbatar da cewa surgery din is a success ba sai bayan wata uku sannan zasu sake dubawa su gani idan cancer din bata dawo ba, still daga nan ma ba za'a saki kiji ba za'a cigaba da dubawa bayan wata uku uku har sai an tabbatar ta tafi.
Sanda Hussain ya farka, Hassan ya gani a gefensa rike da hannun sa ya kwantar da kansa a jikin gadon da Hussain yake kwance idonsa a rufe. Hussain ya dago hannunsa ya dan taba fuskarsa yace "hey bro" Hassan yayi saurin bude kumburarrun jajayen idanuwan sa ya dora akan Hussain, sai yaga Hussain din yayi masa dariya yace "have you been crying?" Ya sake dariya "sai na gaya wa Ruqayyah mijinta rago ne" Hassan ya harare shi ya tashi ya shiga toilet ya wanke fuskarsa ya fito sai ya tarar dashi yana kokarin tashi zaune sannan ya zare drip din da aka saka masa. Ya kamashi yana kokarin kwantar dashi amma yaki kwanciya ya tashi yana cewa "ni yunwa nake ji wallahi, kamar anyi min sata a hanji na" sai kuma ya bude ido yana kallon Hassan yace "gaya min gaskiya, ko har sun yanke hanjin ne?" Sai kawai yayi dariya ya kama hanyar fita.
Hassan ya bishi amma yaki dawowa, sai da ya tuna masa da cewa rigar asibitin ce a jikin sa sannan ya dawo briefly ya mayar da kayansa ya kuma fita. A dole Hassan ya dauko takardun su da kuma wayoyin su ya biyo shi a baya. Sai da suka je gurin cin abinci suka zauna suna ci sannan Hussain yace "na san abinda doctor yace, you don't have to tell me, na riga na gaya maka dama kai ne baka yarda ba. Yanzu tunda ka yarda can we please go home? I have to get back to making that baby you know?"
Hassan ya dauke kansa gefe yace "babu wani home da zaka tafi, you are going to have a surgery next week. Na riga nayi filling takardu har na biya kudi" Hussain ya bude ido cikin mamaki yace "no, na riga na gaya maka am not going to go through that" ya ajiye spoon din hannunsa ya mike ya fice daga gurin. Hassan ya biya bill da sauri ya bishi a baya. Ya tarar dashi a hanya suka jera yana cewa "Hussain Please, doctor din nan fa yayi min bayani, ya nuna min komai a screen na gani ba wai wani guri ne mai yawa ba, yace da zarar sunyi surgery sun cire shikenan sai......." Hussain yace "sai ayi radiology a kashe gurin sannan chemotherapy dan a tabbbar komai ya mutu, after three months kuma sai in dawo a sake wani colonoscopy din a gani idan bata yi regrowing ba, idan kuma tayi sai a sake going through that same precess, a haka har sai hanjin ya kare yadda babu abinda za'a kuma yankewa, ko kuma in ta taba wani vital organ din, sai kuma abar mutum ya karasa mutuwa, yes I know about all the process and no am not going through that. Na gaya maka tun acan".
Haka suka yi ta fama har suka je hotel din da suka sauka, suna ziwa Hussain ya fara hada kaya yana zubawa a jaka Hassan kuma yana kashewa yana mayar wa gurin ajjiyar kaya, "waye ya gaya maka zata sake regrowing? Dan ta wasu tayi that doesn't mean taka ma zata yi. Doctor din fa yace tana stage 2, he is 90% sure cewa zai iya cire ta completely" Hussain yace "I am sorry but I don't believe him. Tunda za'a bashi kudin sa ya karbe ai zai fadi haka dama. Ni ba zan bari likitoci su mayar dani lab animal dinsu ba".
Hassan ya koma ya zauna yana kallon Hussain, he have been stubborn and strong headed tun suna yara, anty ma da kanta ta sha ba da labarin irin taurin kansa da yadda yake bata wahala kafin ta juya shi, in yasa kansa abu to kuwa sai da dabara kafin a iya hana shi. Sai ya dauko wayarsa yace "shikenan tunda kaki jin magana ta, bara in kira Fatima in gaya mata halin da ake ciki watakila in ita tayi maka magana zaka ji" sai Hussain ya tsaya daga hadan kayan da yake yi yana kallon Hassan yace "you won't do that, ai amana na baka maganar nan, kana nufin zaka karya alkawarin da kayi min na cewa ba zaka gaya wa kowa ba?" Hassan ya daga kafada yace "yes of course, idan har hakan yana nufin saving life dinka ne zanyi. Kuma try me ka gani idan ba da gaske nake ba" Hussain ya tsaya yana kallonsa, baiga alamar wasa a fuskarsa ba sai ya ajiye kayan hannunsa ya hau kan gado ya kwanta, sai kuma ya tashi ta shiga toilet yayo alwala ya fito ya tayar da sallah.
Hassan ya mike ya mammayar da kayan da Hussain ya baza, sannan shima yaje yayo alwalar ya fito ya tayar da tasa sallar.
Hussain ya hakura ya yarda za'a yi masa aiki amma sam babu walwala a fuskarsa, sai Hassan ya fahimci kamar aikin yafi damunsa a kan ciwon ma gabaki dayansa. A haka har aka gama preparation ya zama saura kwana daya ayi aikin sai suka tafi asibitin zasu kwana acan, a lokacin ne zuciyar Hassan ta karye yace da Hussain "ina ganin a fasa aikin nan Hussain, ni bana jin dadin yadda kake reacting to it ka ƙi kwantar da hankalin ka bayan kuma kai ba mai yawan tayar da hankali akan abu bane ba, ni duk sanyaya min jiki kake yi wallahi, na kasa fahimtar if am doing the right thing or not. Please bro, ka gaya min cewa ba wai takura maka zanyi ayi maka aikin nan ba, dan Allah ka gaya min" sai Hussain yayi masa murmushi yace "ba wai ka takura min bane Hassan, ba kuma na yarda bane saboda kayi threatening cewa zaka gaya wa Fatima ba, na yarda ne saboda kai, saboda ina so in faranta maka, saboda ina so kaji cewa you did your best kar kayi feeling cewa ka gaza gurin kula dani. But ina so kai ma kayi mini wani alkawari Hassan. Ina so kayi min alkawarin cewa wannan shine surgery na farko kuma na karshe da zaka saka ayi min akan wannan cutar" Hassan ya sunkuyar da kansa kasa, Hussain ya dago fuskarsa yana kallon idonsa yace "say it. Kace kayi min alkawari" Hassan ya karbe fuskarsa sannan yace "nayi alkawari. Kuma nasan ma wannan aikin akwai nasara a cikin sa, mun gaya wa Allah kuma ya dubi kokarin mu. Zamu samu nasara am sure" sai Hussain yayi murmushi yace "good" . Sai ya koma ya kwanta ya rufe idonsa har aka zo aka tafi dashi.
The surgery took 3 hours. A cikin 3 hours din nan Hassan sai da yayi nadamar da basu gaya wa kowa ba, at least da an taya su addu'a, dan ji yake yi kamar bakin sa shi kadai yayi kadan a addu'ar. A cikin awa ukun nan har wata irin rama yayi.
Yana tsaye aka fito da Hussain, aka tura shi recovery room, inda kuma anan ne zai cigaba da karbar treatment dinsa.
Wannan littafin na siyarwa ne, idan kin ganshi a wani gurin na sata ne, in kina son karanta halaliyar ki kiyi min magana ta wannan number din through WhatsApp 08067081020*The Email*
Washegarin da akayi aikin aka fara yiwa Hussain chemotherapy treatment tare kuma da radiation therapy, at the same time kuma ana monitoring warkewar gurin da aka yi masa aiki internal da external. It has not been easy on him duk da cewa Hassan yana tare dashi kuma likitocin suna kulawa dashi sosai, magana mai dadi, karfafa guiwa, da tabbatar da cewa he is comfortable. Shi kansa yasan ya rame, tun kafin ayi aikin kuma ya rane din dan Fatima tasha yi masa mita a waya cewa ya rame, tun yana kakkaucewa har dai ya daina kiran ta video call itama kuma inta kira baya dauka sai yace mata phone dinsa ta samu matsala.
A haka har ya fara jin dadin jikinsa, su kansu doctors din suna yabawa da yadda jikin nasa yayi kyau, ya rage yin amai sosai wanda yana daga cikin side effect na chemotherapy kuma shi yake saka rama, saboda jikinsa ya fara sabawa da magungunan da ake bashi. Sai kuma ya dage da cin abinci, ya kuma cire damuwa a ransa nan da nan ya kara murmure wa. An gama radiation therapy din, magunguna ne kawai yake sha dan haka ya fara maganar yana son ya tafi gida. Da farko doctor din yaki yarda, ya fi son ya kara kwanaki ciwonsa ya kara warkewa duk da cewa ba zasu tabbatar da cewa surgery din is a success ba sai bayan wata uku sannan zasu sake dubawa su gani idan cancer din bata dawo ba, still daga nan ma ba za'a saki kiji ba za'a cigaba da dubawa bayan wata uku uku har sai an tabbatar ta tafi.