Sashe 91
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Lokacin data farfaɗo jin kanta tayi yayi mata nauyi sosai. Ta saka hannu tana dafe kan tare da kokarin yin salati, amma sai taji ba wai kan bane kadai yayi nauyi gabaki daya jikin tane yayi nauyi, ta jima a kwance a inda take sannan ta fara samun karfin bude idonta, abinda ta fara lura dashi shine duhun da gari ya fara yi. Ta dafe kanta ta mike zaune tana numfashi da sauri da sauri har ta samu ta dawo hayyacin ta. Abu na farko da taji a jikinta shine azabar zafin da yake tahowa daga kafarta zuwa sauran sassan jikinta. Gabanta ya fadi tana kai duba izuwa kafafuwan ta. Wani karfe ta gani ya huda naman cinyarta ya wuce. Ta kama shi da hannu daya sannan ta dafe kafar da hannu daya ta zare shi daga jikin ta tana jin azaba tamkar ranta zai bar jikin ta. Sai ta samu kanta da godewa Allah da bata taho da Hussain karami ba. Ta yanki gefen dankwalin ta ta nannade ciwon tana tsayar da zubar jinin da yake yi.
Sai a lokacin tasamu damar karewa gurin da take kallo, motarsu tana can gefe ta daki wata bishiya ta tsaya a kife, tayoyinta a sama, daga inda take tana iya jiyo kauri kamar wani abu yana konewa. Ta mike a hankali tana dai-dai ta tsayuwar ta sannan ta fara jan kafa zuwa inda motar take ta leka ciki, sai ta dawo baya da sauri tana rufe bakinta idanuwan ta kamar zasu fado kasa, kallo daya tayi wa drivern ta san ya mutu saboda yadda wuyansa ya karkace gefe, ta hadiye kukan daya taso mata tana zagayawa barin da Minal take. Idanuwan ta a bude suna kallon Ruqayyah amma ita bata kallon ta, jini yana fita ta kunnen ta da hancin ta. Ta girgiza ta. "Minal, Minal, Minal" amma ita kanta tasan babu Minal ta tafi inda ba'a dawowa. "Inna lillahi wa inna ilaihir rajiun" ta fada tana kallon katon cikin Minal din wanda ake saka ran haihuwarsa ko yau ko gobe. Ta zame gefe daya ta zauna hannun ta akan ta tana rusa kukan rashin kawarta aminiyarta tare da abinda yake cikinta.
Ta sake tashi tana leka bayan motar tana neman Fatima, babu ita babu alamun ta.
"Fatimah! Fatimah" ta fara kwalla kiran Fatima da duk iyakacin karfinta amma shiru. A lokacin ne ta lura da abinda yake kauri, motar ce take kamawa da wuta daga kasa, nan take tsoro ya kama ta fara kokarin jawo gawar Minal daga gurin da take dunkule a tsakanin karafunan inji amma ta kasa, duk da ita ba likita bace ba daga yanayin kwanciyar Minal din ta tabbatar tayi rugu rugu. Ta zagaya side din driver tayi kokarin fito dashi shima amma injin motar da kuma kujerar sa sun matse shi a guri ɗaya. Ta ja baya tana mayar da numfashi tana kallon yadda wutar take kara ruruwa har ta fara cin seat din baya, hasken ta yana haska gurin, a lokacin ta lura da alamar sawun mutum ya bar gurin motar ya shiga cikin bishiyoyi. Fara bin sawun tana kiran sunan Fatima, tana dauke ganin ta daga wutar da take cin gawawwakin a cikin mota.
A hanya taga wayar Fatima, ta dauka tana lura da cewa bata mutu ba duk da cewa screen din ya fashe amma tana ganin hoton Hussain a jikin screen din yanayi mata murmushi, ta tuna da labarin da Minal ta basu a mota wai Hussain ya mutu. Ta cigaba da kiran Fatima tana kara kutsa kai cikin bishiyoyi, suddenly ta ganta a gabanta kamar an jeho ta tana kallon ta da budaddun idanuwa tana cewa
"help me please, ki taimaka mini dan Allah"
gaban Ruqayyah ya fadi saboda fahimta da tayi cewa wadannan suna exact words din da Hassan ya gaya mata ranar da ta fara ganinsa a toilet din su, and it seemed like a long time ago amma shekaru biyu ne kawai. Ta rike ta "Fatima lafiya kike? Babu abinda ya same ki? Minal ta mutu ita da driver" Fatima tace "mafarki nake yi, ki tashe ni dan Allah. Mafarki nake yi wai Hussain ya mutu, wai munyi hatsari a hanyar Abuja, wai ina labor zan haihu a daji" sai a lokacin Ruqayyah ta lura da jinin da yake bin kafafuwan Fatima. "Innalillahi, na shiga uku, Fatima haihuwa zaki yi" Fatima tace "ki tashe ni daga bacci dan Allah, ki kira min Hussain dan Allah" surutai kawai take yi wanda Ruqayyah tabbatar ba a cikin hankalin ta take ba, ta jata gefe ta kwantar da ita, a haka ta haihu a hannun Ruqayyah, danta namiji katoto dashi lafiyayye.
Ruqayyah ta daga dan bayan mabiya ta fito , ita bata san yadda zata yi ta yanke masa cibiya ba dan batada wani abun da zata iya yanke cibiya dashi. Ta daga shi tana nuna wa Fatima, "gashi kin haihu, kin samu da namiji" Fatima ta karbe shi ta rungume shi a kirjinta duk da ba'a hayyacin ta take ba amma taji matsananciyar soyayyar abinda ta haifa. Hawaye ya zubo mata, Sai kuma ta mikawa Ruqayyah tace "ki kaiwa Hussain shi shima ya ganshi, burinsa kenan yaga abinda zan haifa. Bana so in ganshi ni kadai ba tare da shi ba" Ruqayyah ta karba tana kallon babyn, kamar an tsaka kara shida Hassan, hakan yana nufin kamannin Hussain ne dashi kuma da fatar Hassan tunda yafi Fatima ma duhun fata. Ta mayar da dubanta ga Fatima sai ta ji ta shiru, ta girgiza ta da hannu daya "Fatima Fatima" amma shiru.
Ta mike tsaye tana kallon Fatima sannan kuma ta kalli babyn da yake hannunta yana ta tsanyara kuka da dukkan karfin sa. Shikenan yanzu bashi da uba bashi da uwa kenan? Shikenan yanzu shine....... Sai kuma wani tunani ya fado mata. Yanzu wannan jaririn na hannunta shine sole heir na H and H and all its assets. Dogon gidan Hussain, tarin motocin sa, kamfanonin sa na shinkafa, fulawa, sukari, siminti duk yanzu na wannan yaron ne na hannun ta. Wannan yaron na hannunta shine kadai yanzu abinda yake tsakanin ta da H and H, tsakanin ta da zama matar CEO. Wannan yaron da bai fi ta taka shi ta wuce ba.
Tayi saurin katse wannan tunanin daga ranta tana realizing cewa wannan moment din da take ciki, right here right now shine maganar da malamin duban nan yayi mata. A yanzu tana da options guda biyu, ko dai ta tafi da yaron nan gida ta kaishi gurin Hassan da dauran yan uwa su raine shi ya girma su cigaba da rayuwar su a karkashin sa, maybe ma in ya girma ya wulakanta su tunda basu duka haife shi ba ko kuma ta bayar dashi right here and right now and her husband will have majority share ta H and H. Already ta haifa masa maza guda uku, already gidan sa nata ne.
Ta girgiza kanta da sauri, no no no, no matter how much take son dukiya, no matter how much take son ta zama mai kudi she can never kill for it, ko babba ba zata iya kashewa ba ballantana wannan dan jaririn. Ta tuna da maganar malamin "zabi ya rage naki" ta sake girgiza kai kamar yana kallonta, ta kalli Fatima, tana tunawa da Matsayin ta da martabar ta, sai ta tsallake ta ta wuce, ta fara tafiya a hankali har yanzu vata yanke shawarar abinda zata yi ba. Ta cire dankwalin kanta ta nannade jaririn tare da mahaifarsa a ciki sannan ta cigaba da tafiya, a haka ta fito bakin titi tana kallon motoci suna wucewa amma saboda bata yanke hukuncin abinda zata yi da jaririn hannunta ba sai ta kasa tsayar da mota ta nemi taimakon su, ta cigaba da tafiya a kafa ta cikin bishiyoyin bakin titi, tana cikin tafiyar ne taga wata mota kamar ta Hussain tazo wucewa, sai tayi sauri ta buya, jaririn hannunta ya fara kokarin kuka sai ta toshe masa baki, sai taga kamar motar tayi slowing down kamar zata tsaya sai ta kara shigewa cikin bishiyoyi da sauri.
Kamar daga sama taga wani katon gini a gabanta, a jikin gate dinsa an rubuta baro baro "Nationa Orphanage of Nigeria" ta tsaya tana kallon rubutun sannan ta kalli yaron da yake hannunta "orphane" bashi da uba bashi da uwa dan haka orphane ne kuma babu inda ya dace dashi irin Orphanage. Ba tare da tunanin komai ba tabi inuwar jikin ginin zuwa bakin gate din sannan ta sunkuya ta ajiye shi tana kawar da ganinta daga kansa dan kada tausayin sa ya hana ta aikata abinda ta riga ta yanke shawara.
Ta juya da sauri tana barin gurin, sai kuma ta tuna da dankalin ta da yake jikin yaron, evidence ne, za'a iya amfani dashi a binciko wadda ta ajiye shi dan haka ta koma da sauri ta zare dankwalin nata daga jikinsa ta koma cikin bishiyoyi da sauri, tana jin gurin gabaki daya yana amsa kuwwa da karar kukansa. Ta saka hannayenta ta toshe kunnuwan ta tana kara sauri, zuciyarta tana gaya mata yanzu za'a dauke shi dan ta tabbatar kukan ya shiga har cikin gidan.
Sauri take yi sosai tana retracing steps dinta har ta dawo gurin accident din, wutar har tayi kasa sosai ta kusa karasa mutuwa, a gefe taga jakar Minal tare da karafunan motar da suka fita, ta dauka ta jefa ta cikin wutar tana kallon ta ta kama tana konewa, tana jin wani abu a zuciyarta wanda ta kasa fasaltawa.
Babu wanda yasan sun taho da Minal, maybe mai gadi ya ganta shima kuma in ya fada zata iya cewa a hanya suka ajiyeta ta tafi gida, babu mai musa mata. In akazo gurin motar abinda za'a gani shine gawar driver da mace mai ciki a gaba, babu wanda zai ce ba Fatima bace ta mutu tare da abinda yake cikin ta. Problem solved.
Ta juya tana kallon hanyar inda Fatima ta haihu, ta kunna fitilar wayar Fatima da take hannunta ta tafi gurin tana tunanin yadda zata yi ta kawar da gawar .
Amma.........
Babu gawar Fatima babu alamar ta.......
Sai a lokacin tasamu damar karewa gurin da take kallo, motarsu tana can gefe ta daki wata bishiya ta tsaya a kife, tayoyinta a sama, daga inda take tana iya jiyo kauri kamar wani abu yana konewa. Ta mike a hankali tana dai-dai ta tsayuwar ta sannan ta fara jan kafa zuwa inda motar take ta leka ciki, sai ta dawo baya da sauri tana rufe bakinta idanuwan ta kamar zasu fado kasa, kallo daya tayi wa drivern ta san ya mutu saboda yadda wuyansa ya karkace gefe, ta hadiye kukan daya taso mata tana zagayawa barin da Minal take. Idanuwan ta a bude suna kallon Ruqayyah amma ita bata kallon ta, jini yana fita ta kunnen ta da hancin ta. Ta girgiza ta. "Minal, Minal, Minal" amma ita kanta tasan babu Minal ta tafi inda ba'a dawowa. "Inna lillahi wa inna ilaihir rajiun" ta fada tana kallon katon cikin Minal din wanda ake saka ran haihuwarsa ko yau ko gobe. Ta zame gefe daya ta zauna hannun ta akan ta tana rusa kukan rashin kawarta aminiyarta tare da abinda yake cikinta.
Ta sake tashi tana leka bayan motar tana neman Fatima, babu ita babu alamun ta.
"Fatimah! Fatimah" ta fara kwalla kiran Fatima da duk iyakacin karfinta amma shiru. A lokacin ne ta lura da abinda yake kauri, motar ce take kamawa da wuta daga kasa, nan take tsoro ya kama ta fara kokarin jawo gawar Minal daga gurin da take dunkule a tsakanin karafunan inji amma ta kasa, duk da ita ba likita bace ba daga yanayin kwanciyar Minal din ta tabbatar tayi rugu rugu. Ta zagaya side din driver tayi kokarin fito dashi shima amma injin motar da kuma kujerar sa sun matse shi a guri ɗaya. Ta ja baya tana mayar da numfashi tana kallon yadda wutar take kara ruruwa har ta fara cin seat din baya, hasken ta yana haska gurin, a lokacin ta lura da alamar sawun mutum ya bar gurin motar ya shiga cikin bishiyoyi. Fara bin sawun tana kiran sunan Fatima, tana dauke ganin ta daga wutar da take cin gawawwakin a cikin mota.
A hanya taga wayar Fatima, ta dauka tana lura da cewa bata mutu ba duk da cewa screen din ya fashe amma tana ganin hoton Hussain a jikin screen din yanayi mata murmushi, ta tuna da labarin da Minal ta basu a mota wai Hussain ya mutu. Ta cigaba da kiran Fatima tana kara kutsa kai cikin bishiyoyi, suddenly ta ganta a gabanta kamar an jeho ta tana kallon ta da budaddun idanuwa tana cewa
"help me please, ki taimaka mini dan Allah"
gaban Ruqayyah ya fadi saboda fahimta da tayi cewa wadannan suna exact words din da Hassan ya gaya mata ranar da ta fara ganinsa a toilet din su, and it seemed like a long time ago amma shekaru biyu ne kawai. Ta rike ta "Fatima lafiya kike? Babu abinda ya same ki? Minal ta mutu ita da driver" Fatima tace "mafarki nake yi, ki tashe ni dan Allah. Mafarki nake yi wai Hussain ya mutu, wai munyi hatsari a hanyar Abuja, wai ina labor zan haihu a daji" sai a lokacin Ruqayyah ta lura da jinin da yake bin kafafuwan Fatima. "Innalillahi, na shiga uku, Fatima haihuwa zaki yi" Fatima tace "ki tashe ni daga bacci dan Allah, ki kira min Hussain dan Allah" surutai kawai take yi wanda Ruqayyah tabbatar ba a cikin hankalin ta take ba, ta jata gefe ta kwantar da ita, a haka ta haihu a hannun Ruqayyah, danta namiji katoto dashi lafiyayye.
Ruqayyah ta daga dan bayan mabiya ta fito , ita bata san yadda zata yi ta yanke masa cibiya ba dan batada wani abun da zata iya yanke cibiya dashi. Ta daga shi tana nuna wa Fatima, "gashi kin haihu, kin samu da namiji" Fatima ta karbe shi ta rungume shi a kirjinta duk da ba'a hayyacin ta take ba amma taji matsananciyar soyayyar abinda ta haifa. Hawaye ya zubo mata, Sai kuma ta mikawa Ruqayyah tace "ki kaiwa Hussain shi shima ya ganshi, burinsa kenan yaga abinda zan haifa. Bana so in ganshi ni kadai ba tare da shi ba" Ruqayyah ta karba tana kallon babyn, kamar an tsaka kara shida Hassan, hakan yana nufin kamannin Hussain ne dashi kuma da fatar Hassan tunda yafi Fatima ma duhun fata. Ta mayar da dubanta ga Fatima sai ta ji ta shiru, ta girgiza ta da hannu daya "Fatima Fatima" amma shiru.
Ta mike tsaye tana kallon Fatima sannan kuma ta kalli babyn da yake hannunta yana ta tsanyara kuka da dukkan karfin sa. Shikenan yanzu bashi da uba bashi da uwa kenan? Shikenan yanzu shine....... Sai kuma wani tunani ya fado mata. Yanzu wannan jaririn na hannunta shine sole heir na H and H and all its assets. Dogon gidan Hussain, tarin motocin sa, kamfanonin sa na shinkafa, fulawa, sukari, siminti duk yanzu na wannan yaron ne na hannun ta. Wannan yaron na hannunta shine kadai yanzu abinda yake tsakanin ta da H and H, tsakanin ta da zama matar CEO. Wannan yaron da bai fi ta taka shi ta wuce ba.
Tayi saurin katse wannan tunanin daga ranta tana realizing cewa wannan moment din da take ciki, right here right now shine maganar da malamin duban nan yayi mata. A yanzu tana da options guda biyu, ko dai ta tafi da yaron nan gida ta kaishi gurin Hassan da dauran yan uwa su raine shi ya girma su cigaba da rayuwar su a karkashin sa, maybe ma in ya girma ya wulakanta su tunda basu duka haife shi ba ko kuma ta bayar dashi right here and right now and her husband will have majority share ta H and H. Already ta haifa masa maza guda uku, already gidan sa nata ne.
Ta girgiza kanta da sauri, no no no, no matter how much take son dukiya, no matter how much take son ta zama mai kudi she can never kill for it, ko babba ba zata iya kashewa ba ballantana wannan dan jaririn. Ta tuna da maganar malamin "zabi ya rage naki" ta sake girgiza kai kamar yana kallonta, ta kalli Fatima, tana tunawa da Matsayin ta da martabar ta, sai ta tsallake ta ta wuce, ta fara tafiya a hankali har yanzu vata yanke shawarar abinda zata yi ba. Ta cire dankwalin kanta ta nannade jaririn tare da mahaifarsa a ciki sannan ta cigaba da tafiya, a haka ta fito bakin titi tana kallon motoci suna wucewa amma saboda bata yanke hukuncin abinda zata yi da jaririn hannunta ba sai ta kasa tsayar da mota ta nemi taimakon su, ta cigaba da tafiya a kafa ta cikin bishiyoyin bakin titi, tana cikin tafiyar ne taga wata mota kamar ta Hussain tazo wucewa, sai tayi sauri ta buya, jaririn hannunta ya fara kokarin kuka sai ta toshe masa baki, sai taga kamar motar tayi slowing down kamar zata tsaya sai ta kara shigewa cikin bishiyoyi da sauri.
Kamar daga sama taga wani katon gini a gabanta, a jikin gate dinsa an rubuta baro baro "Nationa Orphanage of Nigeria" ta tsaya tana kallon rubutun sannan ta kalli yaron da yake hannunta "orphane" bashi da uba bashi da uwa dan haka orphane ne kuma babu inda ya dace dashi irin Orphanage. Ba tare da tunanin komai ba tabi inuwar jikin ginin zuwa bakin gate din sannan ta sunkuya ta ajiye shi tana kawar da ganinta daga kansa dan kada tausayin sa ya hana ta aikata abinda ta riga ta yanke shawara.
Ta juya da sauri tana barin gurin, sai kuma ta tuna da dankalin ta da yake jikin yaron, evidence ne, za'a iya amfani dashi a binciko wadda ta ajiye shi dan haka ta koma da sauri ta zare dankwalin nata daga jikinsa ta koma cikin bishiyoyi da sauri, tana jin gurin gabaki daya yana amsa kuwwa da karar kukansa. Ta saka hannayenta ta toshe kunnuwan ta tana kara sauri, zuciyarta tana gaya mata yanzu za'a dauke shi dan ta tabbatar kukan ya shiga har cikin gidan.
Sauri take yi sosai tana retracing steps dinta har ta dawo gurin accident din, wutar har tayi kasa sosai ta kusa karasa mutuwa, a gefe taga jakar Minal tare da karafunan motar da suka fita, ta dauka ta jefa ta cikin wutar tana kallon ta ta kama tana konewa, tana jin wani abu a zuciyarta wanda ta kasa fasaltawa.
Babu wanda yasan sun taho da Minal, maybe mai gadi ya ganta shima kuma in ya fada zata iya cewa a hanya suka ajiyeta ta tafi gida, babu mai musa mata. In akazo gurin motar abinda za'a gani shine gawar driver da mace mai ciki a gaba, babu wanda zai ce ba Fatima bace ta mutu tare da abinda yake cikin ta. Problem solved.
Ta juya tana kallon hanyar inda Fatima ta haihu, ta kunna fitilar wayar Fatima da take hannunta ta tafi gurin tana tunanin yadda zata yi ta kawar da gawar .
Amma.........
Babu gawar Fatima babu alamar ta.......