Sashe 11
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A gidan Aunty ma daren ranar basu yi bacci ba, gabaki daya suka hadu a bedroom din aunty suna kai wa ubangiji kukansu. Daga mai sallah sai mai karatu sai mai zikiri a haka har assuba da cimmusu, suka yi sallar assuba sannan suka zauna Aunty tana jero Adduoi su kuma suna amsa mata da ameen har ta gama suka shafa. Suna shafawa ana turo kofar dakin da sauri, suka waiga kusan a tare suna kallonsa kamar yadda yake binsu shima da kallo daya bayan daya yana haki tamkar wanda ya taho a guje tun daga China. Aunty ta mike "Hussain?" Yace "Aunty kidnappers ne suka dauki Hassan, sun kira ni da wayarsa sun kuma turo min hotonsa a daddaure, kudi suke nema, 1billion naira suke nema".
Ga masu son siya zasu iya turo kudinsu ₦300 ta account
GT Bank
Account Name : Nafisa Usman Tafida
Account Number : 0139433741
Sai su turo shaidar transaction din ta hanyar WhatsApp zuwa wannan layin
08067081020
Wadanda basu da account zasu turo katin MTN na ₦300 zuwa wannan layin
08067081020.
Dan girman Allah banda kira, WhatsApp only
Please duk wadda ta turo min kudi tayi min magana, in baki yi min magana ba ba zan san number din da zanyi adding ba.
Notice
Saura episodes uku mu gama free.......
Dan girman Allah banda kira, WhatsApp only👬🏻 TAGWAYE 👭🏻
By
Maman Maama
Episode eight : Kidnapped
Hasken da ya shigo ta window ne ya sauka a dai dai fuskarsa. Ya kikkifta idon sannan yayi kokarin amfani da hannunsa gurin tare hasken amma sai yaji ya kasa motsa hannun nasa. Wani irin ciwo jikinsa yake yi masa tamkar wanda aka kwana ana duka da ƙulki. Ya bude idonsa da kyar, su kansu eyelids dinsa sunyi masa nauri kamar an dora wani abu akan su. Idonsa ya sauka akan window din da take kallonsa ta inda hasken ranar yake shigowa. Ya sake rufe idon da sauri saboda hasken daya kashe masa ido amma already yaga tagar kuma a ransa ya fahimci cewa bai san ta ba. A ina yake? Ya sake kokarin motsa hannunsa amma yaji ya kasa, wannan ya tabbatar masa da cewa hannayen sa a daddaure suke sannan ya fahimci ƙafafuwan sa ma haka. Bakinsa ma a like yake ta hancin sa kawai yake numfashi. Ya juya fuskarsa gefe sannan ya bude idonsa yana numfashi sama sama cikin tsoro, a hankali ya zagaye gurin da yake da idanunsa sannan ya fahimci cewa toilet ne, ya kuma fahimci shi kadai ne a gurin. Sai a lokacin tunanin abinda ya faru dashi ya dawo masa.
Farkon abinda ya fara fahimta shine har ya kwana ya hantse kenan, tashin hankalin sa shine wanne hali yan'uwansa suke ciki? Wanne hali Hussain yake ciki? Shin kidnappers din sunyi contacting dinsu ko kuwa? Abu na biyu daya tuna kuma shine bai yi Sallah ba, bai yi magrib ba bai yi isha ba baiyi assuba ba.
Ya ja ƙafafuwan sa ya lankwasa su yana jin tamkar zasu karye saboda sandarewa da suka yi ga kuma azabar ciwo da suke yi masa, ya yi kokari ya jingina bayansa da jikin bango sannan yabi bangon ya mike zaune yana jin jikinsa gabaki daya yana amsawa saboda ciwo, ciwon tafiyar da akayi dashi a booth din mota, daure shin da akayi for hours da kuma kwana da yayi akan tantagaryar sumunti. Ya sake karewa ban dakin kallo yaga bashi da wani girma sosai daga kofar da take a rufe sai yar karamar tagar da take can sama a rufe itama da glass. Kasa kasa yake jin muryoyin mutane yana shigowa ta kofar.
Ya muskuta a hankali har yaje jikin kofar sannan ya jingina jikinsa da kofar ya kasa kunnen sa yana so yaji abinda suke cewa amma har kansa ya fara ciwo saboda stressing kunnensa da yayi bai samu ya fahimci komai a maganganun nasu ba saboda can kasa suke maganar. Ya fara buga kansa a jikin kofar, yana jin kan yana kara yi masa ciwo amma yana so yayi calling attention din wadanda suke waje in mutanen kirki ne su taimaka masa in kuma holders dinsa ne ya nemi su kunce shi yayi sallah. Sukayi shiru da maganganun su a lokaci daya sannan suka taho bakin kofar da sauri suna gyara abinda suka rufe fuskokinsu dashi. Katon ne ya bude kofar da sauri yana auna Hassan da bakin bindigar da take hannunsa "Will you stop banging that door?" Ya fada murya can kasa kamar me rada. Hassan ya fara kokarin magana amma sai ya kasa saboda bakinsa yana rufe. Mutumin ya saka hannu daya ya cire abin bakin Hassan, Hassan yaji tamkar ya cire ne tare da fatar bakin gabaki daya saboda zafin da yaji amma babu hannun shafawa dan haka kawai ya runtse idonsa har zafin ya lafa, sannan yace "ina son zanyi Sallah dan Allah" mutumin ya sunkuyo fuskanta kusa data Hassan yace "kaga nayi kama da mai yin Sallah? Reserve your sallah kayi ta addu'a twin dinka ya biya mu kudin da muka nema and you will be out of here kaje kayi ta sallolinka".
Dayan ya matso yana turawa Hussain robar abinci data ruwa gasansa, ya kunce masa daurin hannunsa sannan yaja baya, mai bindigar yace cikin gurbatacciyar hausarsa "mu na nan a bakin kofa, if you dare try to make any sound I will fill your brain with bullets" and Hassan knows he means it.
Sai da suka rufe kofar sannan ya dauke ganinsa daga kansu ya mayar kan hannunsa yana shashshafa shi, bringing back blood, sai da yaji hannun ya danyi masa dama dama sannan ya jawo kafarsa yana noticing yadda ta kumbura ya fara kokarin kunce ta, da kyar ya iya kuncewa saboda karfin daurin da suka yi masa da kuma kumburin da kafar tayi. Ya jawo ta yana shashshafa ta sannan yayi kokarin mikewa yayi alwala da ruwan da suka bashi, bai san inane gabas ba kuma ko ya tambaya ba zasu gaya masa ba dan haka sai ya zabi guri ɗaya yayi niyya ya tayar da sallah sa, saboda shi addini mai sauki ne, ubangiji masani ne kuma mai rahama ne.
Bayan ya idar, yayi dogayen adduoi sannan ya zauna ya runtse idanunsa yana kokarin tuno yana yin da ya hango cikin dakin da mutanen suke. Dakin bashi da girma kuma da alama ba'a kammala shi ba dan jikin bangon babu penti kuma tagogin babu frames. Yayi assessing yadda yaga situation din, mutane biyu ya gani amma yasan su uku suka dauko shi, ina dayan? Ya tuno da muryar da yaji a mota, muryar da yaji kamar ya sani. Shin mai muryar ne baya nan? Ya tuna da yadda yaga suna magana cikin rada, da kuma yadda suka buga masa warning din kar yayi making sound, hakan yana nufin cewa a cikin gari suke, a cikin mutane suke. Ya kalli window din da take saman toilet din, glass ne, yana fasawa zasu ji kara kuma kafin ya gudu zasu harbe shi, dan babu imani sam sam a cikin idanun wannan katon.
Yayi ajiyar zuciya ya jingina kansa da jikin bango yana shafa fuskarsa yana jiyo maganagun su kasa kasa a cikin dakin, his only option is to wait har Hussain ya basu abinda suke so su sake shi. Ba shi da ko digon kokwanto cewa Hussain zai biya kudin, ko da kuwa zasu nemi dukkan abinda ya mallaka zai basu, ko da zasu nemi ya bada kansa zai basu, ko da wani aka kama ba shi ba Hussain zai iya biyan kudin ransom ya ceto mutum. Shi mutum ne da dukiyarsa sam bata dame shi ba.
Hassan ya yanke shawarar zai jira, yasan jiran ba zai yi masa dadi ba amma bashi da wani option than that. Zai jira har sai Hussain ya biya kudin sannan su sallame shi ya koma gida sannan kuma ya yanke shawarar yana komawa gida zai yi aure.
Five days later...............
Tunda Hussain ya dawo Nigeria yake jiran barayin Hassan su sake kiransa amma shiru, ba kira babu message babu komai, shima kuma in ya kira number din Hassan din bata tafiya. Hankalin sa in yayi dubu ya tashi kuma commissioner of police ya gaya masa abinda suke so kenan, so suke su gama tsorata shi yadda duk abinda suka ce yayi zaiyi.
Hussain ya girgiza kansa yace "then they don't know me as they claimed they do. I will give up anything for Hassan. One billion naira suka ce masa suna so in dollar bills kuma gata nan na hada na zuba a irin jakar da suka ce in zuba su kawai naje jira su gayamin yadda zanyi da ita" ya karasa maganar yana mikewa yana zagaye dakin. Haka yake tun sanda ya dawo daga China, baya taba zama na minti biyar a guri daya zai mike kamar wanda ake mintsinin sa, fuskarsa tayi baki, idonsa yayi ja kuma ya fada ciki saboda rashin cin abinci, rashin bacci da kuma rashin kwanciyar hankali.
A ranar da aka sace Hassan, Hussain Yana sauka a Beijing ya kira Hassan da niyyar ya gaya masa ya sauka, a lokacin kidnappers din suka dauka kuma direct suka gaya masa cewa yana hannunsu, suka bashi umarnin ya dawo Nigeria sannan suka gaya masa adadin kudin da suke bukata. Sai kuma suka turo masa hoto, hoton Hassan a daddaure a yashe a bandaki, hoton da har yau shine yake yawo a kwakwalwar Hussain, shine yake hana shi bacci.
Ranar da ya dawo Nigeria gidan su ya cika da police da yanuwansu na Gombe da sauran abokan arziki da abokan aiki, kusan duk uncles dinsu da aunties da cousins dinsu sun zo. Yana shiga gidan zai gansu duk a zazzaune da charbi suna ja kamar gidan makoki, sai gidan yake nuna masa kamar Hassan ya mutu ne, sai yake tunawa da mutuwar Abban su.
Ga masu son siya zasu iya turo kudinsu ₦300 ta account
GT Bank
Account Name : Nafisa Usman Tafida
Account Number : 0139433741
Sai su turo shaidar transaction din ta hanyar WhatsApp zuwa wannan layin
08067081020
Wadanda basu da account zasu turo katin MTN na ₦300 zuwa wannan layin
08067081020.
Dan girman Allah banda kira, WhatsApp only
Please duk wadda ta turo min kudi tayi min magana, in baki yi min magana ba ba zan san number din da zanyi adding ba.
Notice
Saura episodes uku mu gama free.......
Dan girman Allah banda kira, WhatsApp only👬🏻 TAGWAYE 👭🏻
By
Maman Maama
Episode eight : Kidnapped
Hasken da ya shigo ta window ne ya sauka a dai dai fuskarsa. Ya kikkifta idon sannan yayi kokarin amfani da hannunsa gurin tare hasken amma sai yaji ya kasa motsa hannun nasa. Wani irin ciwo jikinsa yake yi masa tamkar wanda aka kwana ana duka da ƙulki. Ya bude idonsa da kyar, su kansu eyelids dinsa sunyi masa nauri kamar an dora wani abu akan su. Idonsa ya sauka akan window din da take kallonsa ta inda hasken ranar yake shigowa. Ya sake rufe idon da sauri saboda hasken daya kashe masa ido amma already yaga tagar kuma a ransa ya fahimci cewa bai san ta ba. A ina yake? Ya sake kokarin motsa hannunsa amma yaji ya kasa, wannan ya tabbatar masa da cewa hannayen sa a daddaure suke sannan ya fahimci ƙafafuwan sa ma haka. Bakinsa ma a like yake ta hancin sa kawai yake numfashi. Ya juya fuskarsa gefe sannan ya bude idonsa yana numfashi sama sama cikin tsoro, a hankali ya zagaye gurin da yake da idanunsa sannan ya fahimci cewa toilet ne, ya kuma fahimci shi kadai ne a gurin. Sai a lokacin tunanin abinda ya faru dashi ya dawo masa.
Farkon abinda ya fara fahimta shine har ya kwana ya hantse kenan, tashin hankalin sa shine wanne hali yan'uwansa suke ciki? Wanne hali Hussain yake ciki? Shin kidnappers din sunyi contacting dinsu ko kuwa? Abu na biyu daya tuna kuma shine bai yi Sallah ba, bai yi magrib ba bai yi isha ba baiyi assuba ba.
Ya ja ƙafafuwan sa ya lankwasa su yana jin tamkar zasu karye saboda sandarewa da suka yi ga kuma azabar ciwo da suke yi masa, ya yi kokari ya jingina bayansa da jikin bango sannan yabi bangon ya mike zaune yana jin jikinsa gabaki daya yana amsawa saboda ciwo, ciwon tafiyar da akayi dashi a booth din mota, daure shin da akayi for hours da kuma kwana da yayi akan tantagaryar sumunti. Ya sake karewa ban dakin kallo yaga bashi da wani girma sosai daga kofar da take a rufe sai yar karamar tagar da take can sama a rufe itama da glass. Kasa kasa yake jin muryoyin mutane yana shigowa ta kofar.
Ya muskuta a hankali har yaje jikin kofar sannan ya jingina jikinsa da kofar ya kasa kunnen sa yana so yaji abinda suke cewa amma har kansa ya fara ciwo saboda stressing kunnensa da yayi bai samu ya fahimci komai a maganganun nasu ba saboda can kasa suke maganar. Ya fara buga kansa a jikin kofar, yana jin kan yana kara yi masa ciwo amma yana so yayi calling attention din wadanda suke waje in mutanen kirki ne su taimaka masa in kuma holders dinsa ne ya nemi su kunce shi yayi sallah. Sukayi shiru da maganganun su a lokaci daya sannan suka taho bakin kofar da sauri suna gyara abinda suka rufe fuskokinsu dashi. Katon ne ya bude kofar da sauri yana auna Hassan da bakin bindigar da take hannunsa "Will you stop banging that door?" Ya fada murya can kasa kamar me rada. Hassan ya fara kokarin magana amma sai ya kasa saboda bakinsa yana rufe. Mutumin ya saka hannu daya ya cire abin bakin Hassan, Hassan yaji tamkar ya cire ne tare da fatar bakin gabaki daya saboda zafin da yaji amma babu hannun shafawa dan haka kawai ya runtse idonsa har zafin ya lafa, sannan yace "ina son zanyi Sallah dan Allah" mutumin ya sunkuyo fuskanta kusa data Hassan yace "kaga nayi kama da mai yin Sallah? Reserve your sallah kayi ta addu'a twin dinka ya biya mu kudin da muka nema and you will be out of here kaje kayi ta sallolinka".
Dayan ya matso yana turawa Hussain robar abinci data ruwa gasansa, ya kunce masa daurin hannunsa sannan yaja baya, mai bindigar yace cikin gurbatacciyar hausarsa "mu na nan a bakin kofa, if you dare try to make any sound I will fill your brain with bullets" and Hassan knows he means it.
Sai da suka rufe kofar sannan ya dauke ganinsa daga kansu ya mayar kan hannunsa yana shashshafa shi, bringing back blood, sai da yaji hannun ya danyi masa dama dama sannan ya jawo kafarsa yana noticing yadda ta kumbura ya fara kokarin kunce ta, da kyar ya iya kuncewa saboda karfin daurin da suka yi masa da kuma kumburin da kafar tayi. Ya jawo ta yana shashshafa ta sannan yayi kokarin mikewa yayi alwala da ruwan da suka bashi, bai san inane gabas ba kuma ko ya tambaya ba zasu gaya masa ba dan haka sai ya zabi guri ɗaya yayi niyya ya tayar da sallah sa, saboda shi addini mai sauki ne, ubangiji masani ne kuma mai rahama ne.
Bayan ya idar, yayi dogayen adduoi sannan ya zauna ya runtse idanunsa yana kokarin tuno yana yin da ya hango cikin dakin da mutanen suke. Dakin bashi da girma kuma da alama ba'a kammala shi ba dan jikin bangon babu penti kuma tagogin babu frames. Yayi assessing yadda yaga situation din, mutane biyu ya gani amma yasan su uku suka dauko shi, ina dayan? Ya tuno da muryar da yaji a mota, muryar da yaji kamar ya sani. Shin mai muryar ne baya nan? Ya tuna da yadda yaga suna magana cikin rada, da kuma yadda suka buga masa warning din kar yayi making sound, hakan yana nufin cewa a cikin gari suke, a cikin mutane suke. Ya kalli window din da take saman toilet din, glass ne, yana fasawa zasu ji kara kuma kafin ya gudu zasu harbe shi, dan babu imani sam sam a cikin idanun wannan katon.
Yayi ajiyar zuciya ya jingina kansa da jikin bango yana shafa fuskarsa yana jiyo maganagun su kasa kasa a cikin dakin, his only option is to wait har Hussain ya basu abinda suke so su sake shi. Ba shi da ko digon kokwanto cewa Hussain zai biya kudin, ko da kuwa zasu nemi dukkan abinda ya mallaka zai basu, ko da zasu nemi ya bada kansa zai basu, ko da wani aka kama ba shi ba Hussain zai iya biyan kudin ransom ya ceto mutum. Shi mutum ne da dukiyarsa sam bata dame shi ba.
Hassan ya yanke shawarar zai jira, yasan jiran ba zai yi masa dadi ba amma bashi da wani option than that. Zai jira har sai Hussain ya biya kudin sannan su sallame shi ya koma gida sannan kuma ya yanke shawarar yana komawa gida zai yi aure.
Five days later...............
Tunda Hussain ya dawo Nigeria yake jiran barayin Hassan su sake kiransa amma shiru, ba kira babu message babu komai, shima kuma in ya kira number din Hassan din bata tafiya. Hankalin sa in yayi dubu ya tashi kuma commissioner of police ya gaya masa abinda suke so kenan, so suke su gama tsorata shi yadda duk abinda suka ce yayi zaiyi.
Hussain ya girgiza kansa yace "then they don't know me as they claimed they do. I will give up anything for Hassan. One billion naira suka ce masa suna so in dollar bills kuma gata nan na hada na zuba a irin jakar da suka ce in zuba su kawai naje jira su gayamin yadda zanyi da ita" ya karasa maganar yana mikewa yana zagaye dakin. Haka yake tun sanda ya dawo daga China, baya taba zama na minti biyar a guri daya zai mike kamar wanda ake mintsinin sa, fuskarsa tayi baki, idonsa yayi ja kuma ya fada ciki saboda rashin cin abinci, rashin bacci da kuma rashin kwanciyar hankali.
A ranar da aka sace Hassan, Hussain Yana sauka a Beijing ya kira Hassan da niyyar ya gaya masa ya sauka, a lokacin kidnappers din suka dauka kuma direct suka gaya masa cewa yana hannunsu, suka bashi umarnin ya dawo Nigeria sannan suka gaya masa adadin kudin da suke bukata. Sai kuma suka turo masa hoto, hoton Hassan a daddaure a yashe a bandaki, hoton da har yau shine yake yawo a kwakwalwar Hussain, shine yake hana shi bacci.
Ranar da ya dawo Nigeria gidan su ya cika da police da yanuwansu na Gombe da sauran abokan arziki da abokan aiki, kusan duk uncles dinsu da aunties da cousins dinsu sun zo. Yana shiga gidan zai gansu duk a zazzaune da charbi suna ja kamar gidan makoki, sai gidan yake nuna masa kamar Hassan ya mutu ne, sai yake tunawa da mutuwar Abban su.