Sashe 47
Nida Kishiyoyina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
ta hanata Wayarta kawai shine a jikinta Ko takalmi da mayafi babu sau biyu kenan Salis na gwada aikata lahira tasan ta kara bari suka hadu sai ya aikata lahiran Salis da take juyawa san ranta duk abinda take so jiki na rawa yake Mata yau shi wai yake neman rabata da ranta, "Aunty Luba Aunty Luba" Taji muryar Ashraf a bayanta tsayawa tayi ta juya tana kallonsa har lokacin numfarfashi take ba abinda ke rabata da Ashraf sai harara da zagi,dan haka kawai ta tsane shi Koda ya iso inda take harararsa take shi kuwa idonsa kyar a kanta Yana kallonta "Lafiya ka tsayar dani ka tsare ni da ido ko na zama sa'ar ka"? "Bazan tsayar dake haka kawai batare da wani dalili ba tambaya kawai nake so na miki" "Bazan tsaya ka min tambayoyin ba har ni zaka tsayar sabida bakada kunya karka ga wai dan na rabu da mahaifin ku wlh bazan d'auki raini ba" Luba tace tare da jan tsaki ta fara k'ok'arin tafiya Ashraf yayi sauri yace"ya akayi kika san Abba shine mahaifin Nana"? "Kaje ka tambaye shi yanda akayi nasani bani zaka zo kayi wa wanan Tambayar ba" "Aunty Luba ya akayi ke kadai kika san sirrin shi"? "Kaje ka tambaye shi nace maka zai gaya maka yanda akayi nasan abin kunyar da ya aikata sanan dan na tona Masa asiri ya sakeni,abin kunya dai mahaifinku ya riga da ya aikata,kaje ka tambaye shi a Ina yake samun irin wadanan kudin da yake facaka dashi kasan karya ne dai ace iya albashinsa da asibitinsa ke shigo Masa da kudi haka,har zaka Zo kana min tambayoyi ga Wanda ya dace kaje ka Masa tambayoyi acan" Luba ta karashe tana Jan dogon tsaki zuciyarta fal da bakin cikin yanda bata samu ta d'auko akwatin sarkarta ba" Ashraf sai da ya daina hangota ya juya jikinsa a sanyaye ya koma ciki ya shige dakinsa ya kwanta yana Kara nazartar maganganun Luba,ya dade yana zargin ta hanyar da mahaifinsa ke samun irin Wanan kudaden, ya tuna lokacin da sukayi fada da wani abokinsa Hakeem yace mahaifinsa dan yankan Kai ne,ko kad'an bai tab'a zargin Mahaifinsa ba ta hanyar halal yake neman kudinsa va tunda Yana harkar Ngo Yana da asibitin kansa Kuma Yana aiki da babban asibtin dake Abuja daga lokacin da ya amsa da bakinsa akan shi yayi wa muhasim fyade yaji ya tsorata da lamarin mahaifin nasa dan ko da wasa bai tab'a kawowa zai iya aikata haka ba,auren Luba da yayi da halin da mahaifiyarsa ta shiga duk ya daga musu hankali dan duk da basu gama mallakar hankalinsu ba sun san auren cin Amana suka yi,ko da ya girma hankali ya ringa saka wa mahaifin nasa ido, burinsa ya gano ko dai dagaske Yana yankan Kai din sai dai ko kusa bai ga alama ba,a jiya zargin haka ya Kara tasowa a ransa da Luba ta tona masa asiri akan shi yayi wa muhasim fyade baisan mai yasa yake san zargin Yana da hannu a karkacewar wuyan ta ba har Yana danganta hakan da kila bayan ya mata fyaden yayi kudi da ita ta zama haka, zargin itama Luba kawai yake dan dole akwai wani boyayyen alamari dole itama tana da hannu a duk Abunda ya faru. Ringing din wayarsa ya katse masa tunanin daya tafi yaga "Uncle mustapha" Ke Kiransa dagawa yayi yaji yace Yana waje yazo Ashraf mik'ewa yayi ya fita waje nesa da gidansu ya hango Yaya mustapha yayi parking motarsa,wajen motar ya nufa da isarsa Yaya mustapha ya fito daga motar Yana "Ina Abban ku Ina ta kiransa baya d'aukar wayata" "Dazun nan ya dawo gida bansan mai yasa bai d'auki wayarka ba,uncle dan Allah kayi hakuri da abunda ya faru ka yafewa Abba sharrin shaidan ne" "Ashraf karka damu na yafe ko ban yafe ba abinda ya faru ya riga da ya faru ba abinda zai iya canza hakan,ko a mafarki ban taba kawowa wai Salis zai iya aikata haka ba amma ya zakayi da kaddara ni magana nakeso muyi ta fahimtar juna,tunda har mun riga da munsan shine mahaifin Nana dole zaa zargi ko shi ya karkata mata baki,inaso ya ajiye jin nauyina a gefe ya fadamin iya gaskiyarsa,bazan so nayi kararsa akan zaluncin da yayi wa Yata ba dan Yana auren kanwata idan har sunansa ya b'aci tamkar sunan kanwata ne ya b'aci Kuma abin zai shafeku shiyasa nakeso muyi abin mu cikin gida ba Wanda yasani kullum burina da Addu'a ta shine Allah ya bawa muhasim lafiya shekara Sha biyar an tafi na Sha shidda sai dai a kwantar da ita a tayar,so nake naji abinda akayi mata ta koma haka,kila Yana gudun asirinsa ya tonu shiyasa ya mata haka bandai sani ba nafiso sai munyi magana dashi tukunna" "Uncle mustapha ngd da fahimtarka nasan Abba ya kasa d'aukar wayar ka ne sabida Yana Jin kunyar ka amma yanzu Zan Shiga ciki na fada masa kana kiransa,ko zaka zo mu Shiga ciki? Girgiza masa Kai Yaya mustapha yayi yace Yana cikin motarsa Yana jiransa. Ashraf ya nufi cikin gidan Koda ya Shiga d'akin Aneesa ya nufa dan anan Alhaji Salis yake kulle kansa Alhaji Salis Shi kadai yasan kalar tashin hankali da yake ciki tunda Aisha ta bar gidan ita da Aneesa ba barinsu gidan yafi daga masa hankali ba,bai san ya Yaya mustapha zaiji idan ta bashi labarin shine yayi wa muhasim fyade,Yaya mustapha ya daukeshi tamkar dan uwa bama shida abokin shawara sama dashi a yanzu ba abinda zaiyi ya iya wanke kansa a wajensa,sai a yanzu yake nadamar boye b'oyen da yayi wa Aisha da ace tun farko ya sanar da ita yanda Luba ke bibiyarsa tana San shi har zuwa kaddara da ta fada masa ta ringa masa barazana da kila duk bai tsinci kansa a wanan tashin hankalin ba,shima baisan mai ya toshe masa tunani ba Aisha tana da saukin kai da fahimta da zata fahimce shi,zuciyarsa cike take da fargabar mai zaije ya dawo wane irin mataki Yaya mustapha zai d'auka idan yasan shine yayi wa muhasim fyade ba wanan yafi daga masa hankali ba,bazasu tab'a yarda bashi ya karkata wa muhasim wuya ba,a lokacin da Ashraf ya dawo gidan Kamar kwai ya fashe masa a ciki bai ce masa komai ba dan yasan Aisha ta riga da ta fallasa Shi d'akin Aneesa ya shige yana Jin kansa kamar ya fashe,bai tab'a tsintar kansa da Jin kunya mai tsanani ba irin wanan hannunsa rawa kawai yake wajen shigar da lambarta ya hau kiranta sai dai Yana ringing take katsewa hakane yasa ya tura mata text duk da yasan da wuya ta saurareshi,tun Yana sa rai da reply dinta har ya hakura gidan ma kansa ba dadi yake masa ba dan yaran kamar Suma kunyar abinda ya aikata suke ji. Hakane yasa ya fice daga gidan ya hau motarsa ya fita Yana zaga gari kiran worker da ya shigo wayarsa ya katse masa tunanin da ya tafi ya tsurawa wayar Ido kamar Yana so yaga fuskar Mai Kiran sai da ya masa kira uku kafin ya iya dagawa "Alhaji an Kama su lukman" "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun innalillahi wa Inna ilaihi ka bari dan Allah kar ka karamin tashin hankali akan Wanda nake ciki" "Wlh yanzu nan na kira John yace sun Shiga hannu nidai adduata Allah yasa Kar sunana ya fito kasan suka tona asiri da matsala" "Dan Allah kacewa John ya wurgar da sim dinsa Kar ayi tracing dinsa duk abinda za'ayi ka fada masa zamu bashi ko nawane Kar sunan mu ya fito already Ina cikin wani babban tashin hankali ga wani na Shirin b'ullo min uje da matsala idan asirin mu ya tonu a yau nake Shirin kiranka akan na bar harkar nan idan kudine an tara zai ishe mu har karshen rayuwar mu kar watarana asirin mu ya tonu sai gashi kuwa asirina na neman tonuwa" "Insha Allahu sunanmu bazai fito ba indai baa samu an Kama John ba ko an Kama shi ba lailai ya Kira sunan mu ba" "Innalillahi wa Inna ilaihi rajiun uje dan Allah ku rufamin asiri bansan da wane zanji ba da matsalar gidana zanji ko da wanan masifar dake tunkaroni" "Bari na Kira John ya karya sim din nasa" "Kayi sauri ka kirashi Ina jiranka" Salis ya kashe wayar kirjinsa na bugun tara tara yana ganin watan tonan asirin sa ne ya kama ya kifa kansa akan steering yana "Zainab kin cuceni" Kiran da ya sake shigowa wayarsa yasa yaji kirjinsa ya sake dokawa da k'arfi daya ga Yaya mustapha ke kiransa. Taya zai iya daga wayarsa Yana kallon Kiran har ta katse Da wane zaiji da tashin hankalin daya tunkaro shi zaiji ko da rashin Aisha da Aneesa ko da asirinsa daya riga da ya tonu. Da Wanan tashin hankalin ya dawo gida yazo ya tarar da Luba da a rayuwarsa ba wacce ya tsani gani kamar ta duk masifar nan da yake ciki ita ta jawo Masa. Yanda ta kuntata masa dole shima ya kuntata mata yasan kuntata mata kawai da zaiyi ta shiga gararin rayuwa bai wuce ya hanata d'aukar Koda cokali ba sosai yaga tsaurin idonta na zuwa d'aukar kayanta yaso sun barshi ya kasheta suka hana shi. Muryar Ashraf da bugun k'ofar da yake ya katse masa tunanin da yake. Murya can kasa ya masa izinin shigowa "Abba Yaya mustapha ke sallama da Kai a waje" Wani irin mik'ewa Salis yayi tare da zaro ido yana "kace masa bana nan Ashraf bazan iya hada ido dashi ba kunyarsa nake ji dan Allah jeka ce masa bana nan" "Abba wlh ba wani tashin hankali yazo dashi ba mun yi magana ta fahimtar juna dashi yace magana kawai zakuyi so yake ka fada masa idan kana da hannu a larurar muhasim, Abba dan Allah ka fito ka fada masa kawai gaskiya kawai" "Wlh Ashraf banida hannu a larurarta nasan ba lailai su yarda bani bane tunda har ni na Mata fyade ni kaina bansan Mai ya sameta ba bansan Wanda ya mata haka ba" "Abba toh ya akayi Aunty Luba tasan Kaine mahaifin Nana haka kawai naji Ina zarginta" "Zan baka labari kila ka gano idan tana da hannu a ciki tunda Kai lawyer ne