Sashe 33
Nida Kishiyoyina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
tsoron wani yasan abinda ya shiga tsakaninsa da ita,a karantar da ya mata yasan tana da tsoro bazata tab'a fadawa kowa ba amma yasan zata na nuna Jin tsoronsa ko kin sakin jikinta a wajensa shi kansa bayan abinda ya Shiga tsakaninsa da ita baya Jin zai iya kara kallonta. Shigowar Aisha d'akin ya katse masa tunanin da ya tafi ganinsa a kwance shame shame yasa tayi kansa da sauri tana "Abban Ashraf lafiya kuwa yaushe ka dawo?Mai ya ke damun ka na ganka a kwance a kasa"? "Bana Jin dadi ne" Abu kadan ke rudata jikinsa ta hau tattabawa tana tambayarsa abinda yake damunsa. Sai gashi ta birkita akwatin magangunan ta d'auko Masa maganin zazzabi dan jikin nasa da zafi shima. Sai wajen tara ya iya Shiga bandaki yayi wanka ya daura alwala yayi sallah abincin ma har d'aki Aisha ta kawo masa bayaso ta fahimci damuwar da yake ciki hakane yasa ya dan ci sama sama. Yana ji tana ga Muhasim can itama a kwance wai bata da lafiya sai kuka take yiwa mutane ta hada da "ko zaka dan Mata allura" Girgiza mata kai kawai yayi dan shima bazai soma dosar muhasim da Sunan Allura ba tsaf zata tona Masa asiri wani irin nauyi yake ji a kirjinsa idan ya tuna wai shine yayi wa Muhasim fyade, abinan har karshen rayuwarsa yasan zai na masa ciwo. Addu'arsa shine Allah yasa Kar asirinsa ya tab'a tonuwa abinda ya bashi mamaki shine har washegari bai ji abin ya motsa masa ba baisani ba ko dan Yana cikin tashin hankaline. Muhasim kuwa ita kadai ta sha jinyarta bata fadawa kowa ba har Khadija yayarta da ta ringa nacin ta fada Mata abinda yake damunta. A mugun tsorace take da gidan a yanzu bata da burin daya wuce ta bar gidan amma idan ta tuna Magiyar da Salis ya mata akan Kar ta bar gidan sai ta fasa. Aisha kuwa haka take sako ta agaba da tambayoyin mai yake damunta ta zama shiru shiru haka sai tace ba komai a karshe Aisha tace Mata ko gida take so ta koma da sauri ta gyada mata kai a takaice a haka Aisha ta tattara Muhasim ta maida ta gida tana masifar halin da muhasim ta d'auko da ba nata ba Aunty mamy kuwa sai dariya take mata akan bazata Shiga tsakanin su ba dan tasan indai ita da muhasim ne baa shiga tsakanin su tasan nan ma da kwana biyu muhasim zata Kara birkicewa tace zata dawo Yaya mustapha kuwa shima ya ringa dariya Yana "Ai taga k'arfi da yaji kike neman kwashe dukansu kisa mu kadaici shiyasa ta tausaya mana ta dawo. Luba Luba kuwa tafiyar da mallamin yayi ya jinkirta mata zuwa wajen Salis din dan abinda zai bata tayi amfani dashi bai bata ba,a matse take da taga ta samu ta shawo Kan Salis anyi auren. Sai da aka samu sati biyu mallamin ya dawo ya cajeta kudi masu yawa ya d'auko mata maganin Kamar alewa yace idan ta shirya tafiya office din Salisu ta Shanye idan har ta samu ya kwanta da ita haka zaiji ta kamar alewar har zaiji Aisha na Masa daci idan bai aureta ba bazai tab'a samun sukuni ba. Da tsananin farinciki ta koma gida Washegari ta rangada Jan kunshi ta d'auko hular gashi ta saka taci gayu sosai tamkar zataje gidan biki. Wajen karfe biyu ta nufi office din Salis tasan yau zata samu kansa tunda ta masa abinda zai na Jin bukata a kowane lokaci bai isa yaki amsa tayin da zata masa ba. Koda ta tura k'ofar office din da sallama, Salisu dagowa yayi Yana kallonta har ta samu waje ta zauna tana ta wani bankaro kirjin tana wani karairaya. Salis kuwa kallonta kawai yake Yana tunanin abinda zai mata wlh ko ganin ta bayaso yayi,a yanzu kuma abinda yafi bashi mamaki bai wuce yanda ya dawo yanda yake ba tunda ga lokacin da abu ya Shiga tsakaninsa da muhasim bai kara Jin wanan bukatuwar tashin hankali ba ,tunda Kuma ta bar gidan yake Jin ba dadi yasan sabida abinda ya mata ta bar gidan har a yanzu yana so ya gano mai ya jefashi a wancan halin ya kasa gano wa. Luba kuwa batasan kallon da yake mata zurfi yayi a tunani ba Mik'ewa tayi ta ajiye mayafin ta ta nufi wajensa ta tsaya a gabansa tana wani juyi tana "Dame Aisha tafini da ka rufe idonka kace baka sona ka dubi irin baiwar da Allah ya min" Ganin kallonta kawai yake bai magana ba yasa ta matsa kusa dashi tana k'ok'arin rungumarsa. Salis ya hankadata da k'arfi har sai da ta bugu da bango. Salis bai wata wata ba ya zare belt din jikinsa ya hau tafkarta yana ba ya hanata zuwa office dinsa ba Ihun da take yasa aka shigo office dinsa aka zo aka karbeta a hannunsa shi kuwa ya cigaba da zaginta Yana ko gidansa ta Kara zuwa sai ya ballata. Mayafinta da Jakarta duk sai mika mata akayi. Luba da kuka ta karasa gidan su Asabe tana zuwa ta hau nuna mata jikinta cikin kuka tana "Kinga irin dukan da yamin har ni wanan tsinanen mallamin zai yaudara yace min ya Masa aikin da zai aureni sai gashi duka naci ma a hannunsa dama sai da na fada miki ban yarda da mallaman nan ba wlh kudin mutane kawai suke ci da ace maganin da aka Mai ya kamashi ai Yana tozali dani zai wawuroni sai gashi bakin duka na sha a hannunsa" "Ke mutumin nan fa ya iya aiki bansan mai yasa naki aikin baiyi ba nikam inaga gwara kawai ki hakura ki Nemo wani" "Na hakura duk uwar wuyan Nan da nake sha wlh bazan hakura ba" "Toh idan baki hakura ba ya zakiyi" Wlh haka zan ta bibiyarsa Asabe har sai ya gaji da nacina ya aureni. Salis A ranar Yana komawa gida ya rufe Aisha da fada akan bayaso ya Kara ganin Luba a gidansa luba ba matuniyar arziki bace ba ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba. Aisha kuwa yanda ya ke magana a zuciye yasa bata samu zarafin yi Masa tambayar Mai ta Masa ba ta riga tasa a ranta tsanar Luba kawai yayi, iya saninta ba abunda luba ta Mata da lokaci guda zata rabu da ita. A takaice haka luba ta cigaba da nacin zuwa office din Salis duk da a yanzu bata samun ma Shiga office din nasa sabida dokar da yasa haka zata karaci zamanta har ya fito idan kuwa ya fito haka zai sheka mata rashin mutunci. Muhasim Tana zaune ajinsu tayi jigum tana kallon allon ajinsu. Kwana biyu kenan tana fama da rashin taste a bakinta duk abinda taci bata Jin dadinsa har a yau ta kasa manta abinda Salis ya mata tunda ta baro gidan bata sake komawa ba duk nacin kuwa da Aisha ta ringayi har dasu siyayya duk dan ta yaudareta ta koma kin komawa tayi,Khadija kuwa na makale a gidan taki dawowa sai dai duk hidiman da ake yiwa khadija itama ana mata,sau daya Salis yaje gidan gaida su Yaya mustapha da kuwa ya tambayi t Aunty Mami ta sa baki ta kirata ji take Kamar bazata fito ba amma haka ta daure ta fito ta gaishe shi ya amsa yana tsokanarta da ta gudu tak'i dawowa ko bata ce komai ba Aunty mamy ta biyeshi suka cigaba da magana sai da yazo tafiya yace tazo ya bata Sako ta kawo. Koda tabi bayansa hakuri ya Kara bata ya roketa akan Kar ta tab'a fadawa kowa ta taimaka ta dawo gidan Kar a zargi wani Abu. Ce masa kawai tayi zata dawo a haka ya kwaso siyayya da ya musu ya bata ya Kara Mata da kyautar kudi. Shigowar mallamin biology dinsu ya katse mata tunanin da ta tafi. Biology ya rubuta a allo menstrual cycle shine topic dinsu. Tun kafin a gama darasin ta jike da gumi wata biyu kenan da sati biyu bata ga Al adarta ba a bayanin da ta gama ji yanzu Yana daukewa ne idan an samu juna biyu" Har lokacin tashi yayi kuka kawai ta ringayi dan ta gane juna biyu ne da ita. Ko da ta koma gida ba yanda Aunty mamy batayi da ita akan ta fada mata Mai ke damunta ba taki. Lokacin islamiya nayi ta shirya ta fita bata zame ko'ina ba sai asibitin su Salis dan wani zubin Aisha na Aiko su da abinci tasan asibitin ya zama dole ta fada masa halin da take ciki. Luba dake zaune a wajen da ta saba zaman jjran Salis dan Salis yasa doka ba ta iya Shiga office dinsa. Kamar ance ta dago ta hango muhasim da hijabinta ta nufi office din Salis. Mamakin ganin muhasim yasa ta mik'e tsaye ta fara bin bayanta......... Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne, knuckles,wrinkles,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using sabulun mg's batare da kunbukaci wani Mai b Mai bukata should Chat 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Team glow Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne, knuckles,wrinkles,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using sabulun mg's batare da kunbukaci wani Mai b Mai bukata should Chat 08062991549 07046881166 07067210195 Call 08064532391 Team glow *WANAN LITTAFIN NA KUDINE BIYA 500 TA WANAN ACCT 0272061655 WEMA BANK NAFISA NUHU KO KATIN