Sashe 21
Nida Kishiyoyina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Aneesa k'ofar. Hindatu dirin motar Alhaji Salis da taji yasa ta kwasa a guje tayi d'aki dan bataso Yazo yaga tana fada da luba. Alhaji Salis hankalinsa a tashe ya dawo dan dama baiyi nisa ba kukan da yaji Aneesa nayi ya matukar daga Masa hankali Yana fadowa palon ya tsaya Yana kallon Luba dake tsaye a bakin k'ofar Aneesa tana ta sokawa Aneesa zagi tana rantsuwar sai ta mata dukan mutuwa idan ta bud'e har su zatazo ta kwacewa miji a hada da yi musu bariki Alhaji Salis ya daina ma kulasu. Ganin Alhaji Salis bai sa ta fasa maganganu ba illa ma harararsa da farayi. Alhaji Salis kuwa fadar b'acin ran da yake ciki ma ai bata bakine dan jikinsa har rawa yake ya gaji idan yace bai gaji da Luba ba yayi karya wajenta ya nufa bai yi wata wata ba ya damko hannunta ya fara janta tana tirjewa akan ya cika mata hannu bai cika din ba har sai da ya kai ta dakinta ya cikata tare da shake mata wuya da iya karfinsa yana "Na gaji Luba na gaji Luba sakinki zanyi na huta shekara kusan goma sha biyar kina kunsa min bakin ciki na rasa yanda zanyi dake wlh na gaji luba duk abinda zai faru sai dai ya faru Luba kuwa Ido warwaje ta ringa k'ok'arin cire hannunsa daga wuyanta dan ba karamin shak'a ya mata ba Yana cikata ta zub'e a kasa tana maida numfashi Alhaji Salis kuwa jiki na rawa ya hau neman biro da takarda Yana ci gaba da rantsuwar sakinta da zaiyi "Ka sakeni Salis kagani kasan sirrin ka a tafin hannuna yake ba abinda bansani akan ka ba har sirrinka na kasar waje wlh nasani fadama ne kawai ban tab'a yi ba wlh wlh ba sirrin ka da bazan fitar ba da kai kanka ko kudi aka baka ka fita waje baza ka iya ba yaran ka sai kasan duk bayanin da zaka musu kuma nasan zaka iya tunanin kau da ni ko a yanzu ka kasheni wlh Ina da wacce zata fitar ma da duk sirrinka" Alhaji Salis ya saki biro da takardar hannunsa kirjinsa na wani irin bugawa Luba kuwa ta mik'e tsaye tana "Ka rubuta mana mai kake jira"? Alhaji Salis kuwa a yanzu bashida Kuma bakin magana Luba ta gama dashi gabad'aya cikin rawar murya yace "Luba yarana uku dake ko dan zuriar dake tsakanin mu bazaki tab'a shafamin lafiya ba luba mai amfanin Aurenmu bayan burinki kiga kina daga min hankali kina min barazana da kaddarar da ta afka min da ba wai a San raina bane karki manta fa ko da kin tona min asiri kema wlh sai ya shafeki" "Ya shafeka dai ba dai sakina zaka yi ba ka sakeni ni din kagani haka kawai zaka auro yarinya Yar ficika ta saka ka a daki ka ringa zunduma ihu,bakaji kunya ba tunda ka auro ta ka daina bamu hakkin mu toh wlh zaman lafiya dai a gidanan babu har sai ka saki yarinya nan" "Luba bazan tab'a sakinta ba ban aureta dan na saketa ba idan takamar ki cigaba da min barazana ne kicigaba Luba akwai ranar da zaki kaini bango da Kaina zan fallasa sirrina sai naga Kuma yanda zakiyi Nagaji da halinki a kullum Kara tsanarki nake a raina babu digon kaunarki a raina amma ba komai koma ya kusa zuwa karshe. Ya fice daga d'akin da sauri Luba taja tsaki tana su zuba su gani. Alhaji Salis kuwa na fita d'akin Aneesa yayi ya Kira sunanta akan tazo ta bud'e Masa. Tana bud'e k'ofar yaji wani sabon tashin hankali ya Kara rufe shi dan fuskarta ta kumbura sosai sabida kukan da ta sha Jikinsa bai kara sanyi ba sai daya ga bata fado jikinsa kamar yanda ta Saba ba hasali ma komawa tayi ta zauna a gefen gadon koda ya zauna a gefenta sai ya rasa Mai zai ce mata tunda kullum dai kalmar daya ce hakuri Yana k'ok'arin Magana Aneesa ta katse shi tana "Wlh bby Nagaji Allah bazan iya cigaba da zama a gidanan ba ana aure dan a samu nutsuwa da kwanciyar hankali amma ni tunda nayi Aure ba kwanciyar hankali a ranar ma da aka kaini sai da akazo aka dagamin hankali dolene sai na zauna a gidanan karka manta wanan ba shine alkwarin da kamin ba idan she is mentally ill ka ware mata nata gidan mana balle karantar da na Mata wlh kalau take tunda badani kawai take tashin hankalin ba da kowa ma Yi take ko Kai bata kyalle ba kullum Ina d'aki a kulle sabida Kar ta kawo min duka wlh na fara nadamar Auren" Alhaji Salis yayi sauri ya rufe mata baki ya hau girgiza mata kai idonsa yayi jajjawur ita kuwa ta Aneesa ta cire hannunta daga bakinta ta mik'e tana "Kai nake aure kana da iko akan mu gabadaya na gaji da zaman gidanan ka kaini ko daki dayane da zaman gidanan ba haka kayi da iyayena ba Baby am tired" "Karki min haka Aneesa ki bani time zan kawo karshen komai zan maidaki Abuja kawai kinga kina kusa da gida nan da wata uku zamu koma gabad'aya na kusa gama aikin da nake yi anan din dan Allah suga ki rufamin asiri karki dagamin hankali karki manta kince koma a wane irin yanayine Zaki zauna dani" A takaice duk yanda Aneesa taso ta bijire sai da Salis ya shawo kanta Sai da ya tabbatar ya saka ta dariya ya goyata Kamar yanda ya keyi suna zagaye d'aki tana kyalkyala dariya kafin ya fito daga d'akin sukayi kicibis da Luba a bakin k'ofa da alama labe take musu. Salis ya mata wani irin kallo Yana tunanin dai kau da luba daga rayuwarsa amma ta hanyar da zai bi yake tunani batare da ya zama abin zargi ba. Luba kuwa ganin duk abinda tayi dan ta daga wa Salis hankali akan ya saki Aneesa da take ji tamkar ta jefata a wuta duk yaki yasa ta fara tunanin d'aukar mumunan mataki abinda ya Kara saka Mata tsanar Aneesa bai wuce ranar girkinta yanda Alhaji Salis ke rawar kafa akanta ba amma har lokacin idan kwananta ya zagayo idan zata hau sama ta Fado bazai tab'a sauraranta ba abinda bai tab'a yi ba sai da ya auro Aneesa Kuma idan kwanan Aneesa ya zago a laben da take yi tasan Alhaji Salis budurinsa kawai yake a d'akin. A ranar da tayi labe na karshe ko bacci bata iya yi ba a daren ta Kira kawarta Asabe tana dauka ta fada mata abinda take so ta tura mata kudi mai balain yawa sai a lokacin ta tuna irin kudin da ta kashe akan raba Hindatu da Alhaji Salis amma abu yaci Tura afadar Asabe wai itama Hindatu ba'a zaune take ba tana fatan wanan aikin da takeso ayi mata yayi aiki. Sati uku a tsakani a laben da tayi ta gane aikin da tayi yayi a ranar cikin farin ciki ta kwana zuciyarta fes. Alhaji Salis Watan Aneesa hudu a gidan ya wayi gari da daina iya tab'uka komai a d'akin Aneesa da yake matukar samun nutsuwa da ita,amma abin mamaki idan Yana d'akin Aisha ko Hindatu Yana iyawa Luba ce da tsanarta ke Kara hauhawa a zuciyarsa ya daina nemanta dan dama Rabin neman itace Kuma ko ta nema baya bata dan ya Sha d'aukar pilo ma daddare Yana Jin Kamar ya danneta har sai ta daina numfashi har kudi ya bawa wasu akan su tareta su kashe ta sai dai a ranar sai yaji kamar bazai iya kisan Kai ba gashi har hoton Luba ya basu sai Kuma ya tuna wayanda tace Suma sun San sirrinsa Kuma ta fada musu idan dai kasheta akayi toh shine wanan tunanin yasa shi kiransu akan ya janye karsu mata komai. Yayiwa Aneesa wani irin sabo tunda suka yi Aure indai Yana dakinta sai ya nemeta ko period take sai ya mata dabaru ta samu nutsuwa har mamakin irin lafiyar da Allah ya hore mata yake. Baisani ba ko dan yarinya ce indai zai Shiga dakinta ko ba ranar girkinta bane sai sunyi dan romance taji Dadi. Daga lokacin da Kuma ya tsinci kansa da daina iya tab'uka komai idan itace da girki sai tafi shi shiga tashin hankali da damuwa. Ya rasa mai ya jawo haka,ko shi yafi Aneesan Shiga damuwa bai tab'a nuna mata bane,a dole ya fara zargin dole akwai abinda Luba ta masa ya daina iya saduwa da Aneesan ba Kuma zargi yake ba ya tabbatar da ba mai Masa wanan aika aikan sai Luba sai ya fara nemawa kansa magani. Wasa Wasa suka tafi wata biyar rabonsa da ya sadu da Aneesan da ta a yanzu Kuma ya fara tausayin ta jiki da jini ko dan romance din yayi da ita kamar Kara tsokanarta yayi haka zatayi ta kuka. A yau. Da yake d'akin Luba kasancewar itace da girki a kwance kawai yake Yana juyi idan har zai tuno Aneesa sai yaji Yana cikin bukatar ta sai dai Yana zuwa zaiyi lakwas duk abinda zaiyi sa da dabaru ba abinda zai iya tab'uka wa a karshe sai dai ya bar Aneesa da hawaye a hankali ya daga kansa ya lek'a fuskar Luba da tayu nisa a bacci ko bai kalli agogo ba yasan wajen karfe biyun dare ne,tun karfe goma ya kwanta badan Yana Jin bacci ba ya kwanta ne kawai sabida bayasan takurar da Luba ke masa idan dai itace da girki, gabad'aya zuciyarsa na wajen Aneesa so yake ya ganta ko zaiji sanyi a ransa dan gabad'aya yau bai sakata a idonsa ba sabida Luba ke da girki ta kafa ta tsare bazai shiga dakinta ba indai itace da girki,a yanzu Kuma abu kad'an sai ta hau rantsuwar zata tona Masa asiri kawai ta huta salo salon iskanci ta karo, a hankali ya sauko daga kan gadon cikin sanda ya bud'e k'ofar a hankali yana waiwaiyen Luba dake ta sakin munshari. Addua kawai yake Allah yasa k'ofar dakin Aneesa a bud'e yake shi kansa yau ji yake idan bai samu Aneesa ba zai iya zaucewa wata biyar ba Wasa ba a hankali ya murda k'ofar handle din Allah cikin ikonsa yaji ta bud'e jiki na