Sashe 7
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bangaren Land and properties ya tafi ya samu Alhaji Musbahu, basa shiri saboda duk sanda suka tashi cefanar da wani abun muddin basu kai masa takadda ta gaske me ɗauke da signature Chairman ba baya basu Approval, Zakariyyan kuma baya duba Girma ko Shakarun Alhaji Musbahun haka ze zageshi a gabansa yace ai bashida gadon ubansu balle ya ringa hanasu Taɓa dukiyarsu, yau ɗin se gashi harda risinawa ya gaidashi kafin ya tambayeshi suwa aka bawa Filin da har suka fara gini"
"Ban sani ba, kaje ka samu uban naka kaitsaye, ku masu jiran Gado ma kuke É—auka kuyi yanda kuka so da guri balle me abun daya tara da guminsa?" Amsar da Alhaji Musbahu ya bashi kenan shima kuma ita ya mayarwa da Hajiya.
Ranar akayi dacen itace da Girki dukda Alhaji Audu baya gari ya tafi Umara amma a daren ranar ake saka ran dawowarsu shida Hajiya Rabi da Yammatan gidan duka suka tafi Umara wanda Albarkacin Tafiyar da za'ayi da Hajiya ƙarama da Sarah, wanda ze buga musu Visa da karanbaninsa ya haɗa da duka sauran Yara Matan da suke a gidan se kuwa gashi Alhajin bece komai ba akai. Amma fa seda akayi uwarka ubanka da Hajiya Binta kafin tafiyar ta yuwu harda Allah ya isa yanda kasan kuɗinta aka ɗiba akayi tafiyar dasu.
Babu shirin da tayi na cewar yau Megidan ze dawo tunda ya tafi ma sau biyu sukayi waya Albarkacin zata bashi sautin Dogayen Rigunan Gumama wanda take bulalawa a tsakar gida tayita yawo kamar Maroƙiya, idan tacewa Hafsatu ko Sarah su siyo mata cewa zasuyi ta tura da kuɗi shiyasa ta aikawa da Alhajin hotunan kalarsu kamar wani Yaronta tace guda biyar za'a siyo, da taji shiru be duba saƙon ba shine ta kirashi, na biyun ma tinin an siya tayi masa yace Eh Alhalin ko downloading yaga me ta tura beyi bama.
Ƙarfe goma na dare jirginsu ya sauka kafin a gama dakko musu kayansu su tafi gida sha biyu saura shi Alhajin dama VIP lounge na Arrival ya shige abinsa yace idan sun gama a sanar masa dan baze tafi ya barsu su duka mata ba ga dare, Ahmad ne kaɗai ya tsaya Tarbarsu a samarin gidan, a cikin gida kuma Momy ta musu ɗan abin taɓawa dukda dawowar darece amma tasan Alhajin baya cin abincin jirgi ko China zeje sedai yasha ruwa ko shayi shiyasa ta tanadar masa abinda zeci dukda ba girkinta bane sedai ganin Yau Hajiyar ko Hanyar kitchen bata kalla ba yasa tayi, kamar ma dai bata da lafiya ne dan karaɗin da take isarsu dashi a gidan ma yau shiru kunnuwansu sun samu sa'ida.
A Ɗakinsa Momyn ta shirya masa komai ta bari tayi masa sannu da zuwa daga bakin ƙofa ta wuce Ɗakinta da Yammatanta da suka ruƙunƙumeta suna faɗin sunyi kewarta. Dukda darene haka ma'aikatan gidan Maza suka ringa shiga Babban Falo suna masa sannu da zuwa, Hamshaƙai kuwa, Yakubu, Faisal da Salim harda Mu'allim suna Ɗakunansu babu kuma wanda yake bacci a cikinsu daga masu chatting se masu waya da Yammata gara Mu'allim ɗin ya fita ya tarbi uwarsa ya rakata cikin gida kafin ya koma yaci gaba da Chatting, Tashen Balaga yake akayi rashin sa'a kuma Yayyensa da suke kewaye dashi babu wani gwani da ze kwafi abin Arziƙi a gurinsa shiyasa shima yake nema ya tashi da Ɗabi'u irin na gidansu da ya zame musu Gado wato halin ko in kula.
Hajiya Binta bata saurara ko Babbar Riga Alhajin ya cire ba yana sallamar Masu aiki ya hau sama ta dirar masa a Ɗaki, ransa a jagule da rashin ganin sauran Yaran dake cikin gidan tamkar yanda Ahmad yazo ya tsaya kuma yaga motar kowannensu a ajiye dan ya kafa dokar hana yawon dare ƙarfe goma ake rufe masa Get ba shiga sedai fita duk kuma wanda ya kwana a waje shi yasan ta yanda yake hukuntasu kuma sun biyu suna bin dokar.
"Yawwa Alhaji sannunku da sauka, nace ɗazu naje Goron dutse se nabi ta Zoo road zan karbi saƙo, base naga gini tsiriri a filin kaba? Ni na gaza fahimtar ma me ake ginawa yo bulune ta ko ina an tayar da katangu inaga hawa uku ma aka ɗora bene a gurin" Hajiya ta faɗa tana zama idanunta kuma akan kwanukan da Momy ta ajiye. Alhaji ya shiga kacaniyar zare kayan jikinsa, sati biyun nan yaji dadinsu ya samu lokaci da Amaryarsa dan har wani ɗan kumari yayi yanzu ya dawo zata fara ƙwarzabarsa, ita bata tarairayeshi ba sannan ta addabi masu tarairayarsa ta hana musu sukuni.
Seda ya cire rigarsa ta rage singlet da Wandon dakakkiyar Gedzenar jikinsa kafin ya janyo teble ya bude Casserole ɗin da Momyn ta ajiye, Irin dankalin nan na yan gayu da ake soyawa sama sama sannan a gasa yaji Albasa da Koren tattasai da Yellow da zafinsa alamar yanzu aka gama ko akayi Microwaving ƙamshi na tashi. Ya tsiyaya Shayin dake cikin yar buta yayi bismillah ya faraci ba tareda ya bata amsa ba. A daren take son jin yanda ake ciki dan haka tayi shiru ta tuno da tsohuwar kissa ta matsa tana cewa
"Yi haƙuri duk na sha'afa banma ce maka ga abinci ba, Allah sa be huce ba dan na daɗe da gamawa".
"Da dai harshena ya dena tantance É—anÉ—ano sena yarda, sannan yaushe kika fara siyan irin kwanukan nan? Ina cewa kikayi na yara ne sedai a siyawa su Dada ko kuma kin canza shawara kinbi sahun su Aisha tsofai tsofai daku kuna Asarar kuÉ—i a siyan kayan kitchen?" Alhajin ya mayar mata da martani yana murmushin rainin hankali. Tayi tsam, har yar kunya ce ta kamata wato yasan ba ita ta ajiye ba kenan? Amma seta waske tajira harya cinye tas ya shiga banÉ—aki ya kuskuro baki ya zauna a bakin gado yana duba wayarsa.
Maganar ta sakw soka masa hankalinsa naga saƙonnin da yake dubawa yace mata
"Ahmad ne ze bude kanti a gurin".
Ruwa take sha babu shiri ta ƙware nan ta shiga tuttula tari kamar zata amayo kayan cikinta Alhajin na jera mata sannu. Seda ya lafa mata ido da fuska sunyi jajir se sauke numfashi takeyi dan ta shaƙu amma bata daddara ba ta kalli Alhajin tana zaro ido tace
"Ban fahimci Ahmad ne ze buÉ—e kanti ba? Ka gane inda nake maka zance kuwa? Filin Mota fa nake magana bawai wani guri daban ba"
"Nan É—in nima nake miki zance ai, ba kince kinga ana ta gini ba? Shopping Mall ze buÉ—e a gurin" ya sake bata amsa. Yanzun ta tabbatar da ya gane inda take nufin kuma gaskiyar zancen yake gaya mata. A fusace tace
"Ahmad ze buÉ—e shopping Mall ko zaka buÉ—e masa? Ni zaka ninke a baibai wannan filin zakace ka bawa Ahmad ya bude kanti a ciki ina nan da Me sunan Alhaji yace yana son gurin cewa kayi da tanadin da kakeyi akai ashe ÆŠan gidan Aisha kakeyiwa tanadi zaka buÉ—e masa kanti?"
Hankali kwance dan seda ya kishingida kafin ya bata amsa yace
"Ko kaÉ—an yanda dai kikaji nace miki shi ze buÉ—e to hakan ne nidai na bashi fili mun kumayi Agreement harya biyani wani kaso zan gina masa gurin a hankali idan kasuwa ta kafu ze ringa biyana har mu warware"
Data rasa abin ce masa se kawai tace
"Ai shikenan" ta fice daga É—akin.
Da Asubar Allah ta tattago Naziru da Zakariyya ta shaida musu abinda akw ciki, suka ƙule a ɗaki suna ta ƙulleƙullen yanda za'ayi a rusa maganar amma sun gaza samo hanya domin a yanda Alhajin ya iya bata amsa jiya tasan ba wata magana da zata faɗa yanzu ta samu shiga a gurinsa. Idan ya murɗe barinsa takeyi domin a garin tace seta latsa dole se ayi rashin sa'a kwaɓarta tayi ruwa shiyasa yanzun ma kamar zatayi kuka tace
"Kubar komai a hannuna zan barshi dai yanzu tunda naga kansa yana hayaƙi amma zan maidashi hankalinsa ne kuma wlh ba Ɗan Aisha ba ko ubanta ne yayi kaɗan daya mallaki gurin nan se an karɓeshi".
NAZIRU da yayi shiru yana ta tunani ya gyara zama yace
"Wani tunani nayi, tunda kince yace miki ba kyauta ya bashi gurin ba na tabbatar kuma dagaske ba kyautar bane, me ze hana mu bi abin a siyasance? Nasan dai a shekara goma Ahmad indai ba Naman mutane ze ringa siyarwa ba a gurin nan baze haÉ—a kuÉ—in filin nan da ginin da za'ayi masa ba..."
"Kai na rabaka, ka dena ganin yaron nan yana yawo tsalo tsalo dashi wlh neman kuɗine ya hanashi ƙiba, yanda kasan wannan tsohon haka yake babu sana'ar da baya gwadawa" Alhaji Zakariyya ya tare Nazirun. Seya ja tsaki yace
"Ka dakata Malam kaji point ɗina, i know what I'm saying, kai kasan nawa ake taya filin nan Tsohon nan yaƙi siyarwa? Kuma kaidai kasan riba kawai ya sani babu batun faɗuwa ko mu da yake mana Gwanjon kayansa ai saboda uwarmu ta iya ƙasarta ne, ni shirin dana hasaso yanzu as i was saying a shekara goma Ahmad baze biya kuɗin gurin nan ba shi kuma Tsohon nan nasan duk Nacinsa shekara biyar gaba ma yaci ace ya dunguri ƙasa dukda ma naga Sugar nasa da hawan jinin wani sanɗa sukeyi sunƙi su rarakeshi yanda ya kamata ya buɗa mu samu muja kaya.
Yawwa maganata a nan a bar maganar akwace guri ko wani abu, da zarar Alhaji ya sheƙa lokacin kuma Ahmad ya gama wahala da gurin ya rayashi kawai zamu tayar da rigima muce guri na Alhaji ne, babu ruwanmu da ko nawa sukayi yarjejeniya ya biyashi bamu san anyi ba dan haka guri yana cikin lissafinmu".
"Ji banza, kai matsalata dakai wani lokacin se ka ringa magana kamar wani ɗan ƙwaya wlh, da kake cewa idan Alhaji ya wulla semu tada rigima ana maganar yanda za'ayi guri ya zama mallakinmu kana kawo shirme ko kuwa ka manta bamu kaɗai Alhajin ya haifa ba idan anzo rabon kowa se an fitar masa da kasonsa dai dai da namu?"
"Ban sani ba, kaje ka samu uban naka kaitsaye, ku masu jiran Gado ma kuke É—auka kuyi yanda kuka so da guri balle me abun daya tara da guminsa?" Amsar da Alhaji Musbahu ya bashi kenan shima kuma ita ya mayarwa da Hajiya.
Ranar akayi dacen itace da Girki dukda Alhaji Audu baya gari ya tafi Umara amma a daren ranar ake saka ran dawowarsu shida Hajiya Rabi da Yammatan gidan duka suka tafi Umara wanda Albarkacin Tafiyar da za'ayi da Hajiya ƙarama da Sarah, wanda ze buga musu Visa da karanbaninsa ya haɗa da duka sauran Yara Matan da suke a gidan se kuwa gashi Alhajin bece komai ba akai. Amma fa seda akayi uwarka ubanka da Hajiya Binta kafin tafiyar ta yuwu harda Allah ya isa yanda kasan kuɗinta aka ɗiba akayi tafiyar dasu.
Babu shirin da tayi na cewar yau Megidan ze dawo tunda ya tafi ma sau biyu sukayi waya Albarkacin zata bashi sautin Dogayen Rigunan Gumama wanda take bulalawa a tsakar gida tayita yawo kamar Maroƙiya, idan tacewa Hafsatu ko Sarah su siyo mata cewa zasuyi ta tura da kuɗi shiyasa ta aikawa da Alhajin hotunan kalarsu kamar wani Yaronta tace guda biyar za'a siyo, da taji shiru be duba saƙon ba shine ta kirashi, na biyun ma tinin an siya tayi masa yace Eh Alhalin ko downloading yaga me ta tura beyi bama.
Ƙarfe goma na dare jirginsu ya sauka kafin a gama dakko musu kayansu su tafi gida sha biyu saura shi Alhajin dama VIP lounge na Arrival ya shige abinsa yace idan sun gama a sanar masa dan baze tafi ya barsu su duka mata ba ga dare, Ahmad ne kaɗai ya tsaya Tarbarsu a samarin gidan, a cikin gida kuma Momy ta musu ɗan abin taɓawa dukda dawowar darece amma tasan Alhajin baya cin abincin jirgi ko China zeje sedai yasha ruwa ko shayi shiyasa ta tanadar masa abinda zeci dukda ba girkinta bane sedai ganin Yau Hajiyar ko Hanyar kitchen bata kalla ba yasa tayi, kamar ma dai bata da lafiya ne dan karaɗin da take isarsu dashi a gidan ma yau shiru kunnuwansu sun samu sa'ida.
A Ɗakinsa Momyn ta shirya masa komai ta bari tayi masa sannu da zuwa daga bakin ƙofa ta wuce Ɗakinta da Yammatanta da suka ruƙunƙumeta suna faɗin sunyi kewarta. Dukda darene haka ma'aikatan gidan Maza suka ringa shiga Babban Falo suna masa sannu da zuwa, Hamshaƙai kuwa, Yakubu, Faisal da Salim harda Mu'allim suna Ɗakunansu babu kuma wanda yake bacci a cikinsu daga masu chatting se masu waya da Yammata gara Mu'allim ɗin ya fita ya tarbi uwarsa ya rakata cikin gida kafin ya koma yaci gaba da Chatting, Tashen Balaga yake akayi rashin sa'a kuma Yayyensa da suke kewaye dashi babu wani gwani da ze kwafi abin Arziƙi a gurinsa shiyasa shima yake nema ya tashi da Ɗabi'u irin na gidansu da ya zame musu Gado wato halin ko in kula.
Hajiya Binta bata saurara ko Babbar Riga Alhajin ya cire ba yana sallamar Masu aiki ya hau sama ta dirar masa a Ɗaki, ransa a jagule da rashin ganin sauran Yaran dake cikin gidan tamkar yanda Ahmad yazo ya tsaya kuma yaga motar kowannensu a ajiye dan ya kafa dokar hana yawon dare ƙarfe goma ake rufe masa Get ba shiga sedai fita duk kuma wanda ya kwana a waje shi yasan ta yanda yake hukuntasu kuma sun biyu suna bin dokar.
"Yawwa Alhaji sannunku da sauka, nace ɗazu naje Goron dutse se nabi ta Zoo road zan karbi saƙo, base naga gini tsiriri a filin kaba? Ni na gaza fahimtar ma me ake ginawa yo bulune ta ko ina an tayar da katangu inaga hawa uku ma aka ɗora bene a gurin" Hajiya ta faɗa tana zama idanunta kuma akan kwanukan da Momy ta ajiye. Alhaji ya shiga kacaniyar zare kayan jikinsa, sati biyun nan yaji dadinsu ya samu lokaci da Amaryarsa dan har wani ɗan kumari yayi yanzu ya dawo zata fara ƙwarzabarsa, ita bata tarairayeshi ba sannan ta addabi masu tarairayarsa ta hana musu sukuni.
Seda ya cire rigarsa ta rage singlet da Wandon dakakkiyar Gedzenar jikinsa kafin ya janyo teble ya bude Casserole ɗin da Momyn ta ajiye, Irin dankalin nan na yan gayu da ake soyawa sama sama sannan a gasa yaji Albasa da Koren tattasai da Yellow da zafinsa alamar yanzu aka gama ko akayi Microwaving ƙamshi na tashi. Ya tsiyaya Shayin dake cikin yar buta yayi bismillah ya faraci ba tareda ya bata amsa ba. A daren take son jin yanda ake ciki dan haka tayi shiru ta tuno da tsohuwar kissa ta matsa tana cewa
"Yi haƙuri duk na sha'afa banma ce maka ga abinci ba, Allah sa be huce ba dan na daɗe da gamawa".
"Da dai harshena ya dena tantance É—anÉ—ano sena yarda, sannan yaushe kika fara siyan irin kwanukan nan? Ina cewa kikayi na yara ne sedai a siyawa su Dada ko kuma kin canza shawara kinbi sahun su Aisha tsofai tsofai daku kuna Asarar kuÉ—i a siyan kayan kitchen?" Alhajin ya mayar mata da martani yana murmushin rainin hankali. Tayi tsam, har yar kunya ce ta kamata wato yasan ba ita ta ajiye ba kenan? Amma seta waske tajira harya cinye tas ya shiga banÉ—aki ya kuskuro baki ya zauna a bakin gado yana duba wayarsa.
Maganar ta sakw soka masa hankalinsa naga saƙonnin da yake dubawa yace mata
"Ahmad ne ze bude kanti a gurin".
Ruwa take sha babu shiri ta ƙware nan ta shiga tuttula tari kamar zata amayo kayan cikinta Alhajin na jera mata sannu. Seda ya lafa mata ido da fuska sunyi jajir se sauke numfashi takeyi dan ta shaƙu amma bata daddara ba ta kalli Alhajin tana zaro ido tace
"Ban fahimci Ahmad ne ze buÉ—e kanti ba? Ka gane inda nake maka zance kuwa? Filin Mota fa nake magana bawai wani guri daban ba"
"Nan É—in nima nake miki zance ai, ba kince kinga ana ta gini ba? Shopping Mall ze buÉ—e a gurin" ya sake bata amsa. Yanzun ta tabbatar da ya gane inda take nufin kuma gaskiyar zancen yake gaya mata. A fusace tace
"Ahmad ze buÉ—e shopping Mall ko zaka buÉ—e masa? Ni zaka ninke a baibai wannan filin zakace ka bawa Ahmad ya bude kanti a ciki ina nan da Me sunan Alhaji yace yana son gurin cewa kayi da tanadin da kakeyi akai ashe ÆŠan gidan Aisha kakeyiwa tanadi zaka buÉ—e masa kanti?"
Hankali kwance dan seda ya kishingida kafin ya bata amsa yace
"Ko kaÉ—an yanda dai kikaji nace miki shi ze buÉ—e to hakan ne nidai na bashi fili mun kumayi Agreement harya biyani wani kaso zan gina masa gurin a hankali idan kasuwa ta kafu ze ringa biyana har mu warware"
Data rasa abin ce masa se kawai tace
"Ai shikenan" ta fice daga É—akin.
Da Asubar Allah ta tattago Naziru da Zakariyya ta shaida musu abinda akw ciki, suka ƙule a ɗaki suna ta ƙulleƙullen yanda za'ayi a rusa maganar amma sun gaza samo hanya domin a yanda Alhajin ya iya bata amsa jiya tasan ba wata magana da zata faɗa yanzu ta samu shiga a gurinsa. Idan ya murɗe barinsa takeyi domin a garin tace seta latsa dole se ayi rashin sa'a kwaɓarta tayi ruwa shiyasa yanzun ma kamar zatayi kuka tace
"Kubar komai a hannuna zan barshi dai yanzu tunda naga kansa yana hayaƙi amma zan maidashi hankalinsa ne kuma wlh ba Ɗan Aisha ba ko ubanta ne yayi kaɗan daya mallaki gurin nan se an karɓeshi".
NAZIRU da yayi shiru yana ta tunani ya gyara zama yace
"Wani tunani nayi, tunda kince yace miki ba kyauta ya bashi gurin ba na tabbatar kuma dagaske ba kyautar bane, me ze hana mu bi abin a siyasance? Nasan dai a shekara goma Ahmad indai ba Naman mutane ze ringa siyarwa ba a gurin nan baze haÉ—a kuÉ—in filin nan da ginin da za'ayi masa ba..."
"Kai na rabaka, ka dena ganin yaron nan yana yawo tsalo tsalo dashi wlh neman kuɗine ya hanashi ƙiba, yanda kasan wannan tsohon haka yake babu sana'ar da baya gwadawa" Alhaji Zakariyya ya tare Nazirun. Seya ja tsaki yace
"Ka dakata Malam kaji point ɗina, i know what I'm saying, kai kasan nawa ake taya filin nan Tsohon nan yaƙi siyarwa? Kuma kaidai kasan riba kawai ya sani babu batun faɗuwa ko mu da yake mana Gwanjon kayansa ai saboda uwarmu ta iya ƙasarta ne, ni shirin dana hasaso yanzu as i was saying a shekara goma Ahmad baze biya kuɗin gurin nan ba shi kuma Tsohon nan nasan duk Nacinsa shekara biyar gaba ma yaci ace ya dunguri ƙasa dukda ma naga Sugar nasa da hawan jinin wani sanɗa sukeyi sunƙi su rarakeshi yanda ya kamata ya buɗa mu samu muja kaya.
Yawwa maganata a nan a bar maganar akwace guri ko wani abu, da zarar Alhaji ya sheƙa lokacin kuma Ahmad ya gama wahala da gurin ya rayashi kawai zamu tayar da rigima muce guri na Alhaji ne, babu ruwanmu da ko nawa sukayi yarjejeniya ya biyashi bamu san anyi ba dan haka guri yana cikin lissafinmu".
"Ji banza, kai matsalata dakai wani lokacin se ka ringa magana kamar wani ɗan ƙwaya wlh, da kake cewa idan Alhaji ya wulla semu tada rigima ana maganar yanda za'ayi guri ya zama mallakinmu kana kawo shirme ko kuwa ka manta bamu kaɗai Alhajin ya haifa ba idan anzo rabon kowa se an fitar masa da kasonsa dai dai da namu?"