Sashe 33
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wato farar fatar ce da dogon gashi suka ruÉ—eka ko?" Alhajin ya faÉ—a fuska babu wasa yana tsare Ahmad da ido nan ya diririce murnar da yake ta koma ciki, cikin in ina yace
"Aa wlh Alhaji kawai dai.."
"Kawai dai me? Da ba Suhaima yar gurin Alhaji Lamin kake nema ba?" Alhajin ya dakatar dashi. Tamkar ze fasa masa kuka yace
"Ni daman ita ta ke sona, kuma daga baya tace ita ba zata zauna a Nigeria ba tunda yan gidansu sun koma US sedai na bita can nima abinda ya rabamu kenan"
"Eh anyi haka, naji yayyenta biyu ma duk auransu ya mutu da sukace zasu bi uban su koma can da zama, Lamin,Lamin ban san kalar kwayar da yake sha ba. Haka kawai ya tattara wai shi ya bar Nigeria banda shirme waÉ—anda suke a wajenma idan girma ya riskesu dawowa gida suke su mutu cikin Ahalinsu se shi ze tattara ya koma can, to ita kuma Safiyyah yar wajen Goggonka Salaha fa?" Alhajin yayi kiÉ—ansa ya taka rawarsa lokaci É—aya.
Ahmad da gaba ɗaya ya gama shigewa ruɗani, da fari abu kamar ze zo a sauƙaƙe amma kuma yana neman yayi wahala Alhajin se wani kale kalen magana yakeyi, ta maza yayi dan duk ji yake kamar ya fashe da kuka ko Alhajin ze barshi da zaɓinsa yace
"Ai ita Abbanta yace yayi mata Miji, Momy bata gaya maka ba auran ma saura wata biyu yanzun ma Anty Maimuna tazo siyan kayan Lefe ÆŠan Mijinta ne wanda Safiyyan zata aura"
"Wato sun hanaka zasu bawa ÆŠan Mijin Maimuna, kai dashi waya fi kusanci dasu?" Alhaji yayi maganar cikin faÉ—a Ahmad besan sanda ya É—age kai da hannu biyu ya saki sitiyari ba yana cewa
"Wallahi tallahi ba hanani sukayi ba, gajiya Abban yayi da jiran kuje ayi magana kuma daman ya rigani fara nemanta seda ma Anty Salahan tace a fasa dashi Mony ce tace Aa ba za'ayi haka ba tunda dai ya riga a bashi"
"Baka da hankali zaka saki mota?" Alhajin ya buga masa tsawa se ya nemi gefw ya faka, Allah yasa babu mota dake biye dasu gab kuma ba gudu yake sosai ba shiyasa daya sakwta bata watsasu wani gurin ba. To fisabilillahi kamar wanda aka ritsa a Kotu Alhaji se zabga masa tambayoyi yakeyi yana muzurai ba dole ya manta abinda yakeyi ba?
Shiru ne ya biyo baya, babu kalar addu'ar da Ahmad beyi a ransa ba akan Allah ya sassauto zuciyar Alhaji ya amince da buƙatarsa babu ja in ja.
"Tada motar muje gida, zamu ƙarasa maganar a can" Alhajin ya faɗa bayan daya mula. Jiki ba laka Ahmad yaci gaba da tuƙi, har wani zazzaɓi yake ji yana shirin saukar masa domin yanayin Alhajin ya nuna koda ace ze yarda da batunsa tofa se an kai ruwa rana.
Sun shiga Kano anyi magriba, a kusada wata Majalisa yace ya tsaya ganin suna hada jam'i da alama makararru ne nan suka yi alwala suka bisu. Bayan sun idar ganin Alhaji na lazumi Ahmad ya tsallaka inda yaga wani me gasa Nama yayi sa'a akwai wanda sukayi nan da nan yasa aka shiga yanka masa kashi kashi aka gama tsaf ya basu kuɗinsu yara suka kai masa mota ya sake jido fruits ya ƙara daidai nan Alhaji ya shafa Addu'arsa ya taso suka cigaba da tafiya.
Har bakin falonsa inda ya ɗauke shi ya tsaya da motar Alhajin ya sauka yana Hamdala, filin gidan tarwai da haske tamkar idan allurarka ta fadi zaka ganta. Sarah ce ta fito da Dogon Hijabi da alama aikenta akayi tana ganin Ahmad ta fasa ihun murna ta ɗaleshi, Alhaji ya zabga mata harara kafin ta sauka da gudu ta koma cikin gida se ga gayyar Maimuna da Yan biyun Anty da Mariya tareda Zayyad ta kirasu suka dabaibayeshi suna sowa da murna ga Yah Ahmad ga Yah Ahmad bakinsa ya gaza rufuwa ya ringa ɗaga wadanda ze iya yana saukewa kafin ya buɗe Boot ya shiga fito da ledojin ciki tun a gurin yasa aka ware dan haka ya danƙawa kowa ta ɗakinsu Hatta su Issa dake nan tsaye yayo musu kashinsu suka karba suna murna dayi masa Addu'a, ya gama rabon tsaf ya rage ledoji biyu a hannunsa, Alhaji na tsaye har sannan be shiga ciki ba yana kallon Ahmad.
A cikin Yaransa Ashirin da takwas ya fita daban kyautatawarsa ba kadan bace baga su iyayensa ba ga kowa daya rabeshi se yayi sambarka da halinsa, se yake ganinsa kamar shi a zamanin ƙuruciyarsa.
"Ina nawa Naman toh? Tun ɗazu nake haɗiyar yawu a mota" Alhajin ya tambaya fuska a tamke kuma, Ahmad ya ƙarasa gabansa ya rusuna yana miƙa masa Leda yace
"Fruits É—in idan an gyara se a kawo tunda kafi so a matse"
"Allah yayi Albarka" Alhajin ya faɗa bayan daya karɓi ledar, cikeda farinciki Ahmad ya amsa da "Amin" domin yasan alfanun Addu'ar iyaye, ita take dabaibaye dashi yake ganin haske a rayuwarsa. Tasowarda yayi kamar hadari yayiwa jama'a da yawa rumfa a matsayinsa na matashin Ɗan kasuwa, buɗe shopping mall ɗinsa ya saka kasuwar wasu da yawa tayi ƙasa badan tasirin addu'ar iyayen ba ai da yanzu maƙiya sun kaishi ƙasa.
Da kansa ya kaiwa Momy tata ledar kafin ya wuce ɗaki yayi wanka yayi sallar Isha'a dan an rigada anyi a masallaci. Ya ɗan jima a zaune yana azkar da be samu yayi ba a hanya kafin ya sake shiga cikin gidan yana tafe yana kiran layin Fatima wadda tun suna Haɗeja ya kirata basu wani yi magana me tsayi ba se yanzun yake sake so yaji ya take ya kuma ce ta tura masa da Kwalliyar Juma'ar da duk sati seya roƙa kafin ta bashi.
Busy yaji layin nata a ransa yayi tunani ƙila da yan gidansu take waya shi kansa badan tafiyar da yayi ba yau ya kamata ya leƙa ya gaida Baffa dan kusan duk sati indai yana Kano ko Fatima bata nan se yaje ya gaishe su, yanzun babban abinda yake a ransa jiran jin amincewar Alhaji game da maganar auransu wanda kuma a jikinsa yana ji in Allah ya yarda ba za'a samu matsala ba fatansa daya Allah yasa kar Alhajin yayi zancen da Hajiya har ya gaya mata yar wa yake nema ita kaɗaice a cikin gidan yake da tabbacin zatayi Adawa da auransa da Fatima domin ta tsani TALAUCI da TALAKA, ya tabbatar kuwa muddin ta sani se inda ƙarfinta ya ƙare gurin ganin haƙansa be cimma ruwa ba na auran Fatima, ko ba dan komai ba ta samu hanyar rama tsaya mata a maƙwogwaro da yayi ya hanata rawar gaban hantsi, ya tabbatar zata shiga ta fita gurin ganin be samu abin da yake so ba amma Allah ya fita.
A haka ya shiga cikin gidan Hajiya Rabi na tsakar gidan tana bawa Baba Mairo sallahun abinda zata taho mata dashi wani satin idan zata zo, Baba Mairo dai me girkin gidan tun zamanin Hajiya na Amarya duk haifarsu akayi suka ganta a gidan bayan sun dawo nan Hotoro GRA kusan shekaru Ashirin kenan, wannan tazarar tasa bata biyo su ba saboda har yanzun Mijinta yana raye yana kwance yana Jinya se ya zama se sati sati take zuwa tana girkin Sadaka ana biyanta dukda girma ya kamata yanzun amma macece me lafiya da kazar kazar sannan aikin na rufa mata asiri shiyasa bata saki duka ta daina ba.
"Yaya Ahmad, an dawo" Antyn ta faÉ—a kamar yanda yaran gidan suke kiransa tana murmushi, ya sunkuyar da kansa shima yana murmushin yace
"Tun dazu Anty, har nayi wanka naje sallah ina wuni" ya gaisheta bayan daya idasa kaiwa tsugunne ya sake kallon Baba Mairo da bakinta yaƙi rufuwa da ganinsa yace
"Iya, ina wuni? Ya jikin Baba?"
"Lafiya lau Alhaji, Malam jiki da sauƙi Alhamdulillahi ko da zan fito seda yace na gaishe ka na kuma ƙarayi maka godiya. Na dai barwa Hajiyar tsakiya sallahu da aka ce baka nan amma naji daɗisosai dana ganka mun gode Alhaji Allah ya saka da Alkhairi yaci gaba da yalwata arziƙi ya kuma rabaka da Alhaji Babba da Hajiya lafiya".
Anty ce ta amsa da Amin fuskarta a washe ta tabbata halin nasa yayi musu na Alkhairi, kyautar Ahmad irin wadda Annabi yace ayi ce, ka bayar da hannun dama ba tareda Hagunka ma ta gani ba, ya miƙe yana sake cewa Anty
"Ina Aboki? Dana dawo da safe banshi ba ina sauri shiyasa ban shigi na dubashi ba"
"Ai bama nan ma da wuri na fita ma kaishi Allura seda muka dawo Momy tace ka shigo amma kun fita da Alhaji, yana ciki rigima yake tayi tunda akayi allurar bari Hasna ta kawo maka shi ko zaka shiga?"
"Bari na leƙashi to ance idan anyi allurar ba'aso ana jagwalgwalasu ko ƙila zafi take masa" ya faɗa yana nufar ɗakinta. Tun daga wajen falon kuwa yake jiyo kukan Abdallah Autan gidan a yanzu me watanni uku kuma shine Ɗa na shida da Antyn ta haifa. Babban Ɗanta Musa da suke kira Mu'allim nada shekara goma sha takwas yanzu, se yan biyu mata Husna da Hasna masu shekaru sha biyar sannan Mariya me goma Zayyad me shekaru takwas sai kuma Abdallah data haifa watanni uku baya.
Fadar tashin hankalin da akasha da Hajiya akan cikin nan bata baki ne dan tabbas Allah ya hakunta zuwan sa badan haka ba iyakar baƙin cikin da takaicin da Anty ta ringa sha na Hajiya da gori da cin mutunci akan tazo tana ta zuba yaya saboda taci gado yar matsiyata yaci ace cikin ya bare kota haifi yaron da lalura se gashi Allah ya bata lafiyayyan Ɗa kuma Namiji abinda ya sake gigita Hajiyar ta ringa abu kamar wadda ta zauce, Allah kaɗai yasan da yanda tasha kan Alhaji haka ya saka Antyn a gaba taje Asibiti aka juyar mata da mahaifa wai da shekarunsa rututu ga manyan yaya abin kunya ne ace har yanzu ana haihuwa a gidansa yana haifar Ƙannen Jikokinsa badan Manyan Yayan Alhaji Babannan da Babangida duk Mazane ba da yanzu ma ya fara aurar da jikoki itama Antyn tace daman ko bece ba ta gama haihuwar.
"Aa wlh Alhaji kawai dai.."
"Kawai dai me? Da ba Suhaima yar gurin Alhaji Lamin kake nema ba?" Alhajin ya dakatar dashi. Tamkar ze fasa masa kuka yace
"Ni daman ita ta ke sona, kuma daga baya tace ita ba zata zauna a Nigeria ba tunda yan gidansu sun koma US sedai na bita can nima abinda ya rabamu kenan"
"Eh anyi haka, naji yayyenta biyu ma duk auransu ya mutu da sukace zasu bi uban su koma can da zama, Lamin,Lamin ban san kalar kwayar da yake sha ba. Haka kawai ya tattara wai shi ya bar Nigeria banda shirme waÉ—anda suke a wajenma idan girma ya riskesu dawowa gida suke su mutu cikin Ahalinsu se shi ze tattara ya koma can, to ita kuma Safiyyah yar wajen Goggonka Salaha fa?" Alhajin yayi kiÉ—ansa ya taka rawarsa lokaci É—aya.
Ahmad da gaba ɗaya ya gama shigewa ruɗani, da fari abu kamar ze zo a sauƙaƙe amma kuma yana neman yayi wahala Alhajin se wani kale kalen magana yakeyi, ta maza yayi dan duk ji yake kamar ya fashe da kuka ko Alhajin ze barshi da zaɓinsa yace
"Ai ita Abbanta yace yayi mata Miji, Momy bata gaya maka ba auran ma saura wata biyu yanzun ma Anty Maimuna tazo siyan kayan Lefe ÆŠan Mijinta ne wanda Safiyyan zata aura"
"Wato sun hanaka zasu bawa ÆŠan Mijin Maimuna, kai dashi waya fi kusanci dasu?" Alhaji yayi maganar cikin faÉ—a Ahmad besan sanda ya É—age kai da hannu biyu ya saki sitiyari ba yana cewa
"Wallahi tallahi ba hanani sukayi ba, gajiya Abban yayi da jiran kuje ayi magana kuma daman ya rigani fara nemanta seda ma Anty Salahan tace a fasa dashi Mony ce tace Aa ba za'ayi haka ba tunda dai ya riga a bashi"
"Baka da hankali zaka saki mota?" Alhajin ya buga masa tsawa se ya nemi gefw ya faka, Allah yasa babu mota dake biye dasu gab kuma ba gudu yake sosai ba shiyasa daya sakwta bata watsasu wani gurin ba. To fisabilillahi kamar wanda aka ritsa a Kotu Alhaji se zabga masa tambayoyi yakeyi yana muzurai ba dole ya manta abinda yakeyi ba?
Shiru ne ya biyo baya, babu kalar addu'ar da Ahmad beyi a ransa ba akan Allah ya sassauto zuciyar Alhaji ya amince da buƙatarsa babu ja in ja.
"Tada motar muje gida, zamu ƙarasa maganar a can" Alhajin ya faɗa bayan daya mula. Jiki ba laka Ahmad yaci gaba da tuƙi, har wani zazzaɓi yake ji yana shirin saukar masa domin yanayin Alhajin ya nuna koda ace ze yarda da batunsa tofa se an kai ruwa rana.
Sun shiga Kano anyi magriba, a kusada wata Majalisa yace ya tsaya ganin suna hada jam'i da alama makararru ne nan suka yi alwala suka bisu. Bayan sun idar ganin Alhaji na lazumi Ahmad ya tsallaka inda yaga wani me gasa Nama yayi sa'a akwai wanda sukayi nan da nan yasa aka shiga yanka masa kashi kashi aka gama tsaf ya basu kuɗinsu yara suka kai masa mota ya sake jido fruits ya ƙara daidai nan Alhaji ya shafa Addu'arsa ya taso suka cigaba da tafiya.
Har bakin falonsa inda ya ɗauke shi ya tsaya da motar Alhajin ya sauka yana Hamdala, filin gidan tarwai da haske tamkar idan allurarka ta fadi zaka ganta. Sarah ce ta fito da Dogon Hijabi da alama aikenta akayi tana ganin Ahmad ta fasa ihun murna ta ɗaleshi, Alhaji ya zabga mata harara kafin ta sauka da gudu ta koma cikin gida se ga gayyar Maimuna da Yan biyun Anty da Mariya tareda Zayyad ta kirasu suka dabaibayeshi suna sowa da murna ga Yah Ahmad ga Yah Ahmad bakinsa ya gaza rufuwa ya ringa ɗaga wadanda ze iya yana saukewa kafin ya buɗe Boot ya shiga fito da ledojin ciki tun a gurin yasa aka ware dan haka ya danƙawa kowa ta ɗakinsu Hatta su Issa dake nan tsaye yayo musu kashinsu suka karba suna murna dayi masa Addu'a, ya gama rabon tsaf ya rage ledoji biyu a hannunsa, Alhaji na tsaye har sannan be shiga ciki ba yana kallon Ahmad.
A cikin Yaransa Ashirin da takwas ya fita daban kyautatawarsa ba kadan bace baga su iyayensa ba ga kowa daya rabeshi se yayi sambarka da halinsa, se yake ganinsa kamar shi a zamanin ƙuruciyarsa.
"Ina nawa Naman toh? Tun ɗazu nake haɗiyar yawu a mota" Alhajin ya tambaya fuska a tamke kuma, Ahmad ya ƙarasa gabansa ya rusuna yana miƙa masa Leda yace
"Fruits É—in idan an gyara se a kawo tunda kafi so a matse"
"Allah yayi Albarka" Alhajin ya faɗa bayan daya karɓi ledar, cikeda farinciki Ahmad ya amsa da "Amin" domin yasan alfanun Addu'ar iyaye, ita take dabaibaye dashi yake ganin haske a rayuwarsa. Tasowarda yayi kamar hadari yayiwa jama'a da yawa rumfa a matsayinsa na matashin Ɗan kasuwa, buɗe shopping mall ɗinsa ya saka kasuwar wasu da yawa tayi ƙasa badan tasirin addu'ar iyayen ba ai da yanzu maƙiya sun kaishi ƙasa.
Da kansa ya kaiwa Momy tata ledar kafin ya wuce ɗaki yayi wanka yayi sallar Isha'a dan an rigada anyi a masallaci. Ya ɗan jima a zaune yana azkar da be samu yayi ba a hanya kafin ya sake shiga cikin gidan yana tafe yana kiran layin Fatima wadda tun suna Haɗeja ya kirata basu wani yi magana me tsayi ba se yanzun yake sake so yaji ya take ya kuma ce ta tura masa da Kwalliyar Juma'ar da duk sati seya roƙa kafin ta bashi.
Busy yaji layin nata a ransa yayi tunani ƙila da yan gidansu take waya shi kansa badan tafiyar da yayi ba yau ya kamata ya leƙa ya gaida Baffa dan kusan duk sati indai yana Kano ko Fatima bata nan se yaje ya gaishe su, yanzun babban abinda yake a ransa jiran jin amincewar Alhaji game da maganar auransu wanda kuma a jikinsa yana ji in Allah ya yarda ba za'a samu matsala ba fatansa daya Allah yasa kar Alhajin yayi zancen da Hajiya har ya gaya mata yar wa yake nema ita kaɗaice a cikin gidan yake da tabbacin zatayi Adawa da auransa da Fatima domin ta tsani TALAUCI da TALAKA, ya tabbatar kuwa muddin ta sani se inda ƙarfinta ya ƙare gurin ganin haƙansa be cimma ruwa ba na auran Fatima, ko ba dan komai ba ta samu hanyar rama tsaya mata a maƙwogwaro da yayi ya hanata rawar gaban hantsi, ya tabbatar zata shiga ta fita gurin ganin be samu abin da yake so ba amma Allah ya fita.
A haka ya shiga cikin gidan Hajiya Rabi na tsakar gidan tana bawa Baba Mairo sallahun abinda zata taho mata dashi wani satin idan zata zo, Baba Mairo dai me girkin gidan tun zamanin Hajiya na Amarya duk haifarsu akayi suka ganta a gidan bayan sun dawo nan Hotoro GRA kusan shekaru Ashirin kenan, wannan tazarar tasa bata biyo su ba saboda har yanzun Mijinta yana raye yana kwance yana Jinya se ya zama se sati sati take zuwa tana girkin Sadaka ana biyanta dukda girma ya kamata yanzun amma macece me lafiya da kazar kazar sannan aikin na rufa mata asiri shiyasa bata saki duka ta daina ba.
"Yaya Ahmad, an dawo" Antyn ta faÉ—a kamar yanda yaran gidan suke kiransa tana murmushi, ya sunkuyar da kansa shima yana murmushin yace
"Tun dazu Anty, har nayi wanka naje sallah ina wuni" ya gaisheta bayan daya idasa kaiwa tsugunne ya sake kallon Baba Mairo da bakinta yaƙi rufuwa da ganinsa yace
"Iya, ina wuni? Ya jikin Baba?"
"Lafiya lau Alhaji, Malam jiki da sauƙi Alhamdulillahi ko da zan fito seda yace na gaishe ka na kuma ƙarayi maka godiya. Na dai barwa Hajiyar tsakiya sallahu da aka ce baka nan amma naji daɗisosai dana ganka mun gode Alhaji Allah ya saka da Alkhairi yaci gaba da yalwata arziƙi ya kuma rabaka da Alhaji Babba da Hajiya lafiya".
Anty ce ta amsa da Amin fuskarta a washe ta tabbata halin nasa yayi musu na Alkhairi, kyautar Ahmad irin wadda Annabi yace ayi ce, ka bayar da hannun dama ba tareda Hagunka ma ta gani ba, ya miƙe yana sake cewa Anty
"Ina Aboki? Dana dawo da safe banshi ba ina sauri shiyasa ban shigi na dubashi ba"
"Ai bama nan ma da wuri na fita ma kaishi Allura seda muka dawo Momy tace ka shigo amma kun fita da Alhaji, yana ciki rigima yake tayi tunda akayi allurar bari Hasna ta kawo maka shi ko zaka shiga?"
"Bari na leƙashi to ance idan anyi allurar ba'aso ana jagwalgwalasu ko ƙila zafi take masa" ya faɗa yana nufar ɗakinta. Tun daga wajen falon kuwa yake jiyo kukan Abdallah Autan gidan a yanzu me watanni uku kuma shine Ɗa na shida da Antyn ta haifa. Babban Ɗanta Musa da suke kira Mu'allim nada shekara goma sha takwas yanzu, se yan biyu mata Husna da Hasna masu shekaru sha biyar sannan Mariya me goma Zayyad me shekaru takwas sai kuma Abdallah data haifa watanni uku baya.
Fadar tashin hankalin da akasha da Hajiya akan cikin nan bata baki ne dan tabbas Allah ya hakunta zuwan sa badan haka ba iyakar baƙin cikin da takaicin da Anty ta ringa sha na Hajiya da gori da cin mutunci akan tazo tana ta zuba yaya saboda taci gado yar matsiyata yaci ace cikin ya bare kota haifi yaron da lalura se gashi Allah ya bata lafiyayyan Ɗa kuma Namiji abinda ya sake gigita Hajiyar ta ringa abu kamar wadda ta zauce, Allah kaɗai yasan da yanda tasha kan Alhaji haka ya saka Antyn a gaba taje Asibiti aka juyar mata da mahaifa wai da shekarunsa rututu ga manyan yaya abin kunya ne ace har yanzu ana haihuwa a gidansa yana haifar Ƙannen Jikokinsa badan Manyan Yayan Alhaji Babannan da Babangida duk Mazane ba da yanzu ma ya fara aurar da jikoki itama Antyn tace daman ko bece ba ta gama haihuwar.