← Book details Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 52 OF 71

Sashe 52

Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Awwwnn I'm blushing" ya faɗa yana shafa kai tareda satar kallon Ahmad dake kallon wayar babu kyaftawa yana auna kalaman me magana a cikin wayar ɗaya da ɗaya. Be sani ba ko kewar Fatima ce tasa yakejin muryar Budurwar Jafar tamkar tata ko kuma irin shauƙi me nuna tsantsar soyayyar da take yiwa wanda take magana dashi wanda ya daɗe yana fatan yaji daga Fatima ne yasa har yake hakaito ita take maganar ko yaya? Besan Jafar ya kashe wayar ba seda ya taɓa shi yana cewa

"Da akwai abinci a gidan nan kuma? Yunwa nakeji wlh"
"This is past 1 fa Jafar kai kake neman abinci irin wannan lokacin?"

"Bazaka gane ba, zumuÉ—in ganin Afeeyah yasa na kasacin komai, naji haushi sosai da ba zan ganta yau ba, Allah badan Alhaji ze hana ba yanzu zan tafi Kano irin 6 na isa na wuce gidansu kawai"

"Ka ɗauka a Turai kake kenan ko Yaya? To a Naija Ƙwamushe mutane akeyi a Abuja-Kaduna Road yanzun da tsakiyan rana ma balle ka kai musu kanka da daren nan, Allah ya tsare hanya kaga Ransom ɗin da zasu saka akanka nasan sedai FIFA ta biya badai Alhaji ba".

Da Jafar yayi wanka ya haÉ—o Tea nan ya hana Ahmad sakat da zancen Afeeyah, idan ya buÉ—e wayarsa ze nuna masa hotonta se kuma yace
"Aa ma, gobe zamuje kawai ka ganta face to face kaga Mace ba muna mata ba irin wadda kake wahalar da kanka akanta bata san kanayi ba"

"Uhm, Allah ya nuna mana" Ahmad ya faɗa yana kwanciya, gaskiya Jafar ya faɗa Son maso wani yakeyi da hausawa sukace ƙoshin wahala to amma yaya zeyi? So halittace ce wadda baka iya sanin sanda zata shigeka sannan baka da zaɓin kan wa zata faɗa, masu ganin laifinsa akan yaso Fatima suna bashi mamaki domin jarabtar data same shi tana iya faɗawa akansu suma. Tsananta soyayya tamkar gado ne a gurinsu, abin a jininsu yake, suna da matuƙar zafafawa akan abinda suke so hakan nan in suka ƙi abu toh fa ya shiga uku. Yanzu irin yanda yaga son Afeeyah a idanun Jafar ya tabbatar da ace shima tasa jarabawar ta zamto irin tasa ma'ana yana sonta ita kuma wani daban take so ta yuwu wawancin da zeyi a soyayya se yafi wanda shi Ahmad yakeyi.

Bacci be ishe su ba amma saboda yanda Jafar ya azazzaleshi tilas suka tafi Kano a Mota dan sunyi missing Jirgin Safe da already sukayi booking, na rana da probabilityn ayi postponing ɗinsa ya haɗe da na dare kamar yanda wanda ya kira ya sake musu booking ya sanar masa shi kuwa Jafar baya iya jiran har Bayan Magrib kafin ya isa Kano shiyasa yace su tafi a Mota. Sun shiga Kaduna ya kunna layinsa na Nigeria dan ta WhatsApp yake waya da Afeeyah tun jiyan saboda Hajiya kuma yaƙi kunna wayar ilahi kuwa yana kunnata sega kiranta kamar tana jira ta fara masa masifa da bala'in da suka zame mata kalaman barka da zuwa ya ringa bata haƙuri dan faɗan akan meye ze kira Ahmad ya ɗakko shi bayan ta hana?

Ita bata ce zata sake haɗa masa taro ba amma ai ta gaya masa muddin ze zo ya sanar da Faisal ko Lawan suje su taro shi daga koma ina ne ba Ahmad ba amma seji tayi ance ya tafi Abujar ƙarin baƙin cikinra tafiyarsu tareda Alhaji harda Hajiya Rabi, ko sallama be mata ba Yakubu daya kawo masa takaddu ya saka hannu kafin suka tafi ne ya gaya mata, kwana tayi tana tijara, ita da taso abinda ya faru ya haifar da Ƙiyayya mai tsanani tsakanin Ahmad da Alhajin amma tun daga Jinyar sa da yakeyi taga alamun shaƙuwa ce take sake shiga tsakaninsu ba wai barakar da tayi fatan a samu ba.

Ta ringa kiran layin Jafar kuma a kashe alamar be kunna ba bayan an tabbatar mata daya sauka shine tun farar Asuba take sake gwadawa har Allah yasa yanzu ta shiga ta rusa masa budget É—insa na biyawa gidansu Afeeyah tilas suka wuce gida Ahmad na masa dariya domin yasan dama za'a runa ya tabbatar kuma nasa kason yana nan yana jiransa abu guda dai shidai baze bari wani hargagi ko cin mutunchin Hajiya ya shiga tsakanin zumunchinsa da É—an uwansa ba.

Aiko yasa zagi da tijara kamar ko yaushe yayi murmushi ya fice daga gidan, ya rasa me yasa wayar da Jafar yayi da Afeeyah jiya ta tsaya masa a rai ta kuma tado masa da kewar Fatima dan muryarta keyi masa gewaye a ƙwaƙwalwa, da daddare Baba Alƙali ya kirashi yake shaida masa ya kira mahaifin Fatima sunyi magana a waya ya sanar masa da zasuje nema masa auranta yayi murna sedai yace yana neman Alfarma da su bashi lokaci domin akwai shirye shiryen da yake so ya kammala kafin tasowar maganar auran.

"Yace daga nan zuwa sati huɗu zamu ji shi duk yanda ake ciki, amma Ahmad anya kuwa iyayen yarinyar nan da kansu suka ce ka turo maganar aure?" Baba Alƙalin ya tambayeshi. Ya sosa kai kamar yana gabansa zuciyarsa na dukan uku uku, Baffa yace a dakata da zuwa nema masa aure bayan shi da kansa yace ya bashi dama daya turo to me hakan yake nufi?? A sanyaye yace masa

"Wlh shi da kansa yace mun na turo"
"Toh inaga ko wani abun ne ya taso da yake buƙatar ƙarin lokaci, to babu laifi ai sati huɗun daya ambata kamar yauce. Kafin nan shima Jafaru idan inda yake neman sun shirya se aje muku gaba ɗaya a huta" da haka sukayi sallama jikin Ahmad yayi wani laƙwas kamar an zubawa Salak gishiri, ta tabbata dai ya rasa Fatima tunda har Baffa da kansa yace su dakata to tabbas nauyin Baba Alƙali yaji kai tsaye ba ze iya ce musu baze bashi yarsa ba. Amma me yasa Baffa zeyi masa haka? Koda yake ba laufin Baffa bane tunda dai bashi ze aura ba ita kuma Fatiman tace bata ra'ayinsa ai ba za'ayi mata dole ba.

Zazzaɓi ne ya dawo masa haɗe da ciwon kai me zafi dan kasa maida kansa gida yayi se Salim ya kira dan Hajiya ta saka Jafar a Ɗaki kamar sabuwar Amarya tunda suka dawo ta hanashi motsawa ko nan da can.

PAGE 19
FATIMA
Duk irin ɗaure fuskar da Umma take mata tareda maganganu be saka taji ko ɗar a zuciyarta dangane da zaɓinta ba musamman da ta samu lako lako a gurin Baffa, shine me bayar da auranta tasan kuma bazeyi mata dole ba. Idan gidan ya isheta ta gaji da faɗan Umma sta tattara ta tafi gidan Anty Sauda can idan ta nemi ta takura mata da zancen Ahmad buɗe baki take ta mayar mata da martani saɓanin Umma da sedai ta sunkuyar da kai tayi hawaye.

"Dan Allah ku barni na auri abinda nake so, yanzu da dole aka miki zaki samu wannan walwakar da kik ciki harki ringa ƙiba kina walwali? Ni ban taɓa cewa ina son Ahmad da aure ba ko shima yasanda haka, to akan me kuma za'a kafa mun ƙahon zuƙa dan nace ga wanda nake so yanzu?" Ta faɗa tana turawa Anty Sauda dake mata mitar zancen Ahmad ƙeya.

"Ai shikenan daman mu yan mu baki shawara ne kamar yanda kika ce kece me zaman auren ba wani ba, amma ki sani hausawa sukace Alamar ƙarfi tana ga mai ƙiba, ko Ahmad kika aura na tabbatar se kin haɗa da haƙuri da ɗauke kai saboda matashine da uwar kuɗinsa a hannunsa abinda kika raina ɗin wasu na can suna haƙilon yanda zasuyi su same shi balle kuma kuma wannan da kike So ai wlh faɗuwar gaba da tunanin ina yake su waye tare dashi kaɗai ya isheki, baki kuma isa kice zaki raba shi da mata ba dan dasu kika ganshi. Mutumin dake karakaina cikin masu jajayen kunnuwa Mata masu kyau ba irin wacce be gani ba, Allah kaɗai yasan nawa yake tare dasu a yanzu dan ko be nemi Mace ba su zasu kai masa kansu, to dan Allah meye ribar auran soyayyar da zuciyarka kullum zata zama a tsaye? Ai wlh ka auri Mijin da son sa yafi naka shine ka morewa aure, koda kika ce ina ƙiba saboda Mijina na so na ne, ina juyashi son raina idan nace ina son abu jiki na rawa zeyi mun in ko nace bana so haka ze bari wannan shine burin kowacce me hankali data san me takeyi ba irinki ba da kike nemarwa kanki Jafa'i Mijin da ze ringa ɗaure miki fuska yana fafara miki tsawa" Anty Sauda take sababi.

Afeeyah tace "nawa zaɓin kenan, se a tayani da addu'a yanda akeyiwa kowa". Saboda takaici Anty Sauda bata sake ce mata komai ba, daman wai taje ne ta sanar mata Jay ya ɗaga ranar zuwansa. Ita saboda yanda abin yake ɓata mata rai ko Mijinta bata gayawa shegantakar da Afeeyar tazo da ita ba, randa ya tsinci tana mata faɗa ne tayi briefing nasa akan wani ta samo kuma wai yanzu ba Ahmad ba, dake ya iya ɗaurewa ƙarya ƙugu shima yace wai a bita a hankali, Aure da mutuwa babu me tsara su tafe suke da lokacinsu da kuma wanda zasu riska babu kuma wansa ya isa ya canza haka.

A ranar bayan Afeeyah ta koma gida da daddare Baffah ya kirata, suna zaune a Baranda saboda garin akwai zafi kuma babu wutar Nepa har Umma tayi masa shimfiÉ—a a gurin da yace indai ba an maido wuta ba ko kuma ruwan sama ya sauka a nan ze kwana. Ita kanta zafin ya addabeta amma dole ta zauna a É—aki saboda gujewa maganganun Umma ga Yah Malam ya koma makaranta sun fara Final Exam daman dayana nan ne take samun yancin zaman tsakar gida ko Baffah baya nan tunda yana tare mata faÉ—an da Umma ta ara ta yafa ya zama halinta yanzu dukda dai shima bawai ya goyi bayan abinda take so tayi bane dan abinda ya gaya mata shima É—in dai kamar sauran ne
Chapter 52 · 0% Book details