Sashe 2
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kinyi kyau uwar masu gida, yau zuciyar mahassada sedai ta buga dan baƙin ciki" Hajiyar ta faɗa tana ƙarasawa kusa da ita. Hajiya ƙarama ta saki murmushi kafin ta shiga juyawa dan ta nunawa Hajiyar kwalliyarta dakyau, Fitted gown ce ta wani cotton London Brocade a jikinta dark blue me zanen flower sea green da fari a jiki, kudinsa ya tasamma dubu sittin, Jafar ne ya aikowa da Hajiyar su sun kai guda goma yace a ɗinka mata dogayen riguna saboda laushinsa yasan zeyi dadin sakawa shine Hajiya ƙaramar ta kwashe uku dan tasan ba ɗinkawa Hajiyar zatayi ba ta kai aka mata lalatattun dinkuna a ciki wannan fitted gown din itace me ɗan dama dama dan ta rufe mata jiki gaba daya illarta kawai shape dinta daya bayyana ƙarara.
"Kin fa gama haɗewa Yar nan babu makusa" Hajiyar ta sake faɗa tana bata hannu suka kashe daidai nan wayarta tayi ƙara, sunan Abba Tee ya bayyana akan screen ɗin. Tsanar dadi harda wani maƙale hannaye Hajiya tayi sama kamar Kangaroo bakin nan ko har maƙogaronta ana hangowa, Hajiya ƙarama ta amsa wayar cikin muryar shagwaɓa kamar zata fashe da kuka tace
"Harka iso"
"Yes Babe, ina waje" ya bata amsa daga cikin wayar, ta sake narkewa tana cewa
"Baka shigo ciki ba? Issa baya nan ne? Kayi horn ze buÉ—e maka Get ya shogar dakai palour kafin na fito"
"He isn't here, oh kamar gashi nan wani Buzu ko? ya buÉ—e Get É—in bari na shigo"
" Saurayin ya sake FaÉ—a kafin ya katse wayar.
Hajiya ta sake bata hannu suka kashe tana cewa
"Wai, Allah ya taimakemu, maza kije ki ƙara turare, duba ɗakina akwai wannan Disaina da kike nacin na baki na gurin Yayanki ki ɗauka, bari na duba abincin idan sun kammala"
"An gama kumai har na shirya a Try kaowa kawai za'ayi" Inji Hajiya ƙarama
"Yauwa yar gari, jeki to kar yayita zama Allah ya bada sa'a" cewar Binta. Hajiya ƙarama ta wuce ɗaki ta ƙaro turare kamar yanda Binta tace ta fito tana takun yauƙi Albarkatun jikinta na motsawa danma kayan jikin nata sun matseta kam hakan ya rage musu samun damar rangaji yanda ya kamata.
Yanda Yaran Alhaji Audu Maza suke Dogaye ginannu idan ka cire Ahmad daya ɗauki Jikin Aisha bashida ƙiba sam haka beyi irin tsahonsu ba to Matan ma duk haka suke dogaye masu cikakken jiki, Allah ya taimake su da ƙira mai kyau ta jiki data fuska musamman da dukansu se akayi katari suka ɗauko fuskar Dada, Farare tas ɗin cikinsu Amina, Aslmaiyya da Hajiya ƙarama da yan Biyun Hajiya Rabi Baba Bilki takance kamanninsu kwabo da kwabo da Dadarsu.
"Yauwa, saura kuma ki sake maimaita abinda kikayi wancan karon kika saka yayi fushi, kina kallo dai har dubuta dari Turai ta damfareni, koda yake kwalliya ta biya kuɗin sabulu tunda an janyoshi yazo, soyayyar nan ta zamani ke sekace ba wayayya ba da ita ake kama samarin nan, banda abinki waye ze kwasheki haka siɗan ba tareda ya tabbatar kin iya kalar soyayyar da yake da buƙata ba, yar rungumar nan da kis ne dai Allah na tuba ai ba wani abu bane, ban dai ce kije ki buɗe kafa ba ki saka mu shiga uku kuma kuyi a hankali Alhaji ma sama ze iya saukowa kowan...."
"Hajiya!" YAKUBU da ke cin abincinsa tun shigarta be tanka maganar da sukeyi ba ya kira sunanta cikin ɗaga murya me kama da tsawa dan a firgice daga ita har Hajiya ƙaramar suka kalleta kowacce na tsammanin da ita yake. Farantin gabansa ya ture ya miƙe tsaye fuskar sa tamkar zatayi aman bacin ran daya turnuƙeshi lokaci daya.
Ya nuna Hafsatu da yatsa yana cewa
"Ashe abinda ake faÉ—a akanki gaskiya ne? Iskancin da aka ce kinayi dagaskene saboda kin shahara yanzu har cikin gidan ubanki kika kawo saurayi zakuyi iskanci?" Kai ta shiga girgiza masa tanaja baya domin Yakubu bashida daÉ—i, ba su ba uwar data haifeshi ma shakkarsa takeyi dan Lamarinsa me girma ne. Hajiya Binta ta dake tana hararar sa tace
"Kai bana son ɗiban Albarka, a gidan uwar masu faɗar aka ganta tana iskancin? Koda uban wani tayi a cikinsu da har suke bayar da shaida? Bakaji me nake faɗa bane? Ce mata nake fa ta saki jiki dashi ita ai gida huma ce duk samarin da kake gani suna zuwa suna tafiya ai ƙin basu fuska takeyi shi yake korarsu. Shifa wannan ɗin in gaya maka, Yaron Alhaji Mudi Tanko ne tsohon Senet piresiden kuma yanzu haka takarar gwamna yake a Garinsu, can kwanaki bana muku zancen sa ba har yazo sau ɗaya shine ya tafi be sake dawowa ba? Ai in gaya maka wannan shashashar yarinyar ce ta kusa kwafsa mana, wai fa ɗaukarta yayi sukaje Otal ya kama Ɗaki, daga cewa su shiga ciki shikenan ta gudo wai har da ce masa ita ba yar iska bace se kace yace mata wata tsiyar ze mata idan suka shiga. Shiko yayi fushi ya tafi, dakyar fa yanzu seda na baiwa Turai dubu ɗari ta kaiwa Malaminta akayi aiki akansa shine fa ya zo yanzu, faɗan da nake mata kenan kar a maimaita ta wnacan karon a samu a kamashi a hannu ya fito ayi zancen Auren nan masu yi mun dariya su sha kunya suji da ƙaryar sarauta suzo suga Arziƙi a inda yake dan duk na samu labarim gidansu ba ƙaramar wadaƙa ubansu yakeyi idan ya tashi Aurar da Yara ba".
Yanda take maganar hankali kwance tamkar me faɗar wani abin Arziƙi, Yakubu yayi sakato yana kallonta a ransa kuwa kokwanto yakeyi akan Hajiyar ce ta haifi Hafsatu ko kuwa Riƙonta takeyi?
Anya uwa zata yiwa yarta irin wannan huÉ—ubar kuwa?
"Zatayi mana, mussamman uwa irin taku da take bautawa duniya da abinda yake cikinta" zuciyarsa ta bashi amsa. Seya ja numfashi ya furzar kafin ya zabura ya nufi ƙofa, cikin Hajiya ƙarama ya kaɗa, Hajiya kuwa yatsine fuska tayi tace
"Ke da Allah rabu dashi, ance masa bansan duk abinda sukeyi bane su? Duk fa haka suke lallatse yammatan suma suna basu kuÉ—i balle ke da Aurenki ma zeyi jeki abinki manta dashi kar kuma ko manta uar soyayyar nan da ake nunawa a fim irinta zaki masa kinji ki hargitsa masa tunani yayi maza maza ya turo azo ayi magana kar zancen Auran Aslamiyya ya riga naki tashi".
A saluɓe Hafsan ta fita duk karsashin da take dashi ya barta. A ƙofar fita daga ainahin cikin gidan taci karo da Ali Daya daga cikin Ma'aikatan gidan me kula da shuke shuke, da gudu ya taho badan ta matsa masa ba da tuni yayi tafiyar gari da ita.
"Yawwa Hajiya kiyi sauri, ga Alhaji Yakubu can yana dukan baƙonki" ya faɗa yana haki. Ƙirji ta dafe tana zaro ido daga inda take kuma tana iya jiyo ihun kukan data tabbatar na Abba Tee ne da kuma hargowar Yakubu yana faɗin
"Daga yau ka sake zuwa wani gida ka yi iskanci da ƙanwar wasu". Da gudu ta juya ciki tana kuka tana kiran Hajiya. Binta nacan tana gyara zaman kofunan da za'a kaiwa Baƙon tana kwararaqa me aikinta Ashar akan wai bata goge su dakyau ba so take yace musu ƙazamai sega Hafsa na kuka jage jage, bata ko iya sauraronta gaba daya ba tayi waje cikin tashin hankali tana kiran Yakubu.
Yakubu kuwa dukan Ɗa da Uba yakeyiwa saurayin Hafsatu ya fasa masa baki da hanci ga hauri yana kai masa a ƙafafu yana kiran seya karya su yaga da wanda ze ringa yawon iskancin Hajiya ta iso ta cakumeshi tana zaginsa se kuma ta saka kuka tana cewa
"Shikenan kaima an taɓa ka, nidai yanda naga ka fito ido a jirkice daman kamar wanda iska ta shafa nasan da walakin, ni aka tozarta a gidan nan ko? Anga Asirin da akayiwa Yata yaƙici kullum sababbin Manema take samu shine aka biyo ta wannan hanyar ko? To wlh mu zuba mu gani, bana Boka bana Malam amma ko wanene ya taɓani seyaji a jikinsa" se kuka wiwiwiwi. Ma'aikatan gidan gaba daya sukayi dafifi suna kallon ikon Allah, Drama a gidan dai ba sabon abu bace ta safe daban ta rana daban ba kuma sa gundira da tirka tirkan gidan domin kullum sabon abu suke gani. Audu da hayaniyar ta fito dashi ya isa gurin cikin dakakkiyar murya yake tambayar abinda ya faru se sannan kuma Abba Tee ya samu ya miƙe ya nuna Yakubu yace zasu gamu seya san shiya taɓa, Yakubu ya zabura ze sake damƙarsa ya taka ya gurin motarsa da sauri ya shige yana cigaba da faɗin
"We shall meet in court, zaka san ni ka daka se ka gane baka da wayo".
Cikin tsawa Audu ya bawa ma'aikatan umarnin su watse kowa ya juya gurin aikinsa. Ya kalli Hajiya dake kuka har sannan Hafsatu ta runguketa itama tana kukan kafin ya mayar da hankalinsa kan Yakubu yana tambayarsa meya faru? Waye wancan É—in kuma meya haÉ—a u harta kai ga duka? Kafin ya bashi sa Hajiya tayi zuruf tace
"Me kuwa ya haɗasu? Magautane sukayi masa turen Aljani haka kawai ya rufeshi da duka saurayin Hafsa ne fa, anga Allah ya fito mata da Miji na nunawa Sa'a shine aka bi yanda akayi shima aka koreshi kuma wlh ba'a taɓa banza ba ko wacece a cikin matanka tayi abin nan ta kwana da shirin zubin Adashi tayi ɗauka kuma dole, ka wuce kai kuma ka kwanta kana tsaye kana wa mutane muzurai ko Aljani ƙarƙuzu ne wlh sekaci ubanka sannan ka koma kan wadda ta aiko ka" ta faɗa tana aikawa da Yakubu wata harara me tafe da gargaɗi. Juyawar yayi kamar yanda tace ya fice daga gidan gaba ɗaya ita ma suka koma ciki da Hafsa dake kuka har sannan.
"Kin fa gama haɗewa Yar nan babu makusa" Hajiyar ta sake faɗa tana bata hannu suka kashe daidai nan wayarta tayi ƙara, sunan Abba Tee ya bayyana akan screen ɗin. Tsanar dadi harda wani maƙale hannaye Hajiya tayi sama kamar Kangaroo bakin nan ko har maƙogaronta ana hangowa, Hajiya ƙarama ta amsa wayar cikin muryar shagwaɓa kamar zata fashe da kuka tace
"Harka iso"
"Yes Babe, ina waje" ya bata amsa daga cikin wayar, ta sake narkewa tana cewa
"Baka shigo ciki ba? Issa baya nan ne? Kayi horn ze buÉ—e maka Get ya shogar dakai palour kafin na fito"
"He isn't here, oh kamar gashi nan wani Buzu ko? ya buÉ—e Get É—in bari na shigo"
" Saurayin ya sake FaÉ—a kafin ya katse wayar.
Hajiya ta sake bata hannu suka kashe tana cewa
"Wai, Allah ya taimakemu, maza kije ki ƙara turare, duba ɗakina akwai wannan Disaina da kike nacin na baki na gurin Yayanki ki ɗauka, bari na duba abincin idan sun kammala"
"An gama kumai har na shirya a Try kaowa kawai za'ayi" Inji Hajiya ƙarama
"Yauwa yar gari, jeki to kar yayita zama Allah ya bada sa'a" cewar Binta. Hajiya ƙarama ta wuce ɗaki ta ƙaro turare kamar yanda Binta tace ta fito tana takun yauƙi Albarkatun jikinta na motsawa danma kayan jikin nata sun matseta kam hakan ya rage musu samun damar rangaji yanda ya kamata.
Yanda Yaran Alhaji Audu Maza suke Dogaye ginannu idan ka cire Ahmad daya ɗauki Jikin Aisha bashida ƙiba sam haka beyi irin tsahonsu ba to Matan ma duk haka suke dogaye masu cikakken jiki, Allah ya taimake su da ƙira mai kyau ta jiki data fuska musamman da dukansu se akayi katari suka ɗauko fuskar Dada, Farare tas ɗin cikinsu Amina, Aslmaiyya da Hajiya ƙarama da yan Biyun Hajiya Rabi Baba Bilki takance kamanninsu kwabo da kwabo da Dadarsu.
"Yauwa, saura kuma ki sake maimaita abinda kikayi wancan karon kika saka yayi fushi, kina kallo dai har dubuta dari Turai ta damfareni, koda yake kwalliya ta biya kuɗin sabulu tunda an janyoshi yazo, soyayyar nan ta zamani ke sekace ba wayayya ba da ita ake kama samarin nan, banda abinki waye ze kwasheki haka siɗan ba tareda ya tabbatar kin iya kalar soyayyar da yake da buƙata ba, yar rungumar nan da kis ne dai Allah na tuba ai ba wani abu bane, ban dai ce kije ki buɗe kafa ba ki saka mu shiga uku kuma kuyi a hankali Alhaji ma sama ze iya saukowa kowan...."
"Hajiya!" YAKUBU da ke cin abincinsa tun shigarta be tanka maganar da sukeyi ba ya kira sunanta cikin ɗaga murya me kama da tsawa dan a firgice daga ita har Hajiya ƙaramar suka kalleta kowacce na tsammanin da ita yake. Farantin gabansa ya ture ya miƙe tsaye fuskar sa tamkar zatayi aman bacin ran daya turnuƙeshi lokaci daya.
Ya nuna Hafsatu da yatsa yana cewa
"Ashe abinda ake faÉ—a akanki gaskiya ne? Iskancin da aka ce kinayi dagaskene saboda kin shahara yanzu har cikin gidan ubanki kika kawo saurayi zakuyi iskanci?" Kai ta shiga girgiza masa tanaja baya domin Yakubu bashida daÉ—i, ba su ba uwar data haifeshi ma shakkarsa takeyi dan Lamarinsa me girma ne. Hajiya Binta ta dake tana hararar sa tace
"Kai bana son ɗiban Albarka, a gidan uwar masu faɗar aka ganta tana iskancin? Koda uban wani tayi a cikinsu da har suke bayar da shaida? Bakaji me nake faɗa bane? Ce mata nake fa ta saki jiki dashi ita ai gida huma ce duk samarin da kake gani suna zuwa suna tafiya ai ƙin basu fuska takeyi shi yake korarsu. Shifa wannan ɗin in gaya maka, Yaron Alhaji Mudi Tanko ne tsohon Senet piresiden kuma yanzu haka takarar gwamna yake a Garinsu, can kwanaki bana muku zancen sa ba har yazo sau ɗaya shine ya tafi be sake dawowa ba? Ai in gaya maka wannan shashashar yarinyar ce ta kusa kwafsa mana, wai fa ɗaukarta yayi sukaje Otal ya kama Ɗaki, daga cewa su shiga ciki shikenan ta gudo wai har da ce masa ita ba yar iska bace se kace yace mata wata tsiyar ze mata idan suka shiga. Shiko yayi fushi ya tafi, dakyar fa yanzu seda na baiwa Turai dubu ɗari ta kaiwa Malaminta akayi aiki akansa shine fa ya zo yanzu, faɗan da nake mata kenan kar a maimaita ta wnacan karon a samu a kamashi a hannu ya fito ayi zancen Auren nan masu yi mun dariya su sha kunya suji da ƙaryar sarauta suzo suga Arziƙi a inda yake dan duk na samu labarim gidansu ba ƙaramar wadaƙa ubansu yakeyi idan ya tashi Aurar da Yara ba".
Yanda take maganar hankali kwance tamkar me faɗar wani abin Arziƙi, Yakubu yayi sakato yana kallonta a ransa kuwa kokwanto yakeyi akan Hajiyar ce ta haifi Hafsatu ko kuwa Riƙonta takeyi?
Anya uwa zata yiwa yarta irin wannan huÉ—ubar kuwa?
"Zatayi mana, mussamman uwa irin taku da take bautawa duniya da abinda yake cikinta" zuciyarsa ta bashi amsa. Seya ja numfashi ya furzar kafin ya zabura ya nufi ƙofa, cikin Hajiya ƙarama ya kaɗa, Hajiya kuwa yatsine fuska tayi tace
"Ke da Allah rabu dashi, ance masa bansan duk abinda sukeyi bane su? Duk fa haka suke lallatse yammatan suma suna basu kuÉ—i balle ke da Aurenki ma zeyi jeki abinki manta dashi kar kuma ko manta uar soyayyar nan da ake nunawa a fim irinta zaki masa kinji ki hargitsa masa tunani yayi maza maza ya turo azo ayi magana kar zancen Auran Aslamiyya ya riga naki tashi".
A saluɓe Hafsan ta fita duk karsashin da take dashi ya barta. A ƙofar fita daga ainahin cikin gidan taci karo da Ali Daya daga cikin Ma'aikatan gidan me kula da shuke shuke, da gudu ya taho badan ta matsa masa ba da tuni yayi tafiyar gari da ita.
"Yawwa Hajiya kiyi sauri, ga Alhaji Yakubu can yana dukan baƙonki" ya faɗa yana haki. Ƙirji ta dafe tana zaro ido daga inda take kuma tana iya jiyo ihun kukan data tabbatar na Abba Tee ne da kuma hargowar Yakubu yana faɗin
"Daga yau ka sake zuwa wani gida ka yi iskanci da ƙanwar wasu". Da gudu ta juya ciki tana kuka tana kiran Hajiya. Binta nacan tana gyara zaman kofunan da za'a kaiwa Baƙon tana kwararaqa me aikinta Ashar akan wai bata goge su dakyau ba so take yace musu ƙazamai sega Hafsa na kuka jage jage, bata ko iya sauraronta gaba daya ba tayi waje cikin tashin hankali tana kiran Yakubu.
Yakubu kuwa dukan Ɗa da Uba yakeyiwa saurayin Hafsatu ya fasa masa baki da hanci ga hauri yana kai masa a ƙafafu yana kiran seya karya su yaga da wanda ze ringa yawon iskancin Hajiya ta iso ta cakumeshi tana zaginsa se kuma ta saka kuka tana cewa
"Shikenan kaima an taɓa ka, nidai yanda naga ka fito ido a jirkice daman kamar wanda iska ta shafa nasan da walakin, ni aka tozarta a gidan nan ko? Anga Asirin da akayiwa Yata yaƙici kullum sababbin Manema take samu shine aka biyo ta wannan hanyar ko? To wlh mu zuba mu gani, bana Boka bana Malam amma ko wanene ya taɓani seyaji a jikinsa" se kuka wiwiwiwi. Ma'aikatan gidan gaba daya sukayi dafifi suna kallon ikon Allah, Drama a gidan dai ba sabon abu bace ta safe daban ta rana daban ba kuma sa gundira da tirka tirkan gidan domin kullum sabon abu suke gani. Audu da hayaniyar ta fito dashi ya isa gurin cikin dakakkiyar murya yake tambayar abinda ya faru se sannan kuma Abba Tee ya samu ya miƙe ya nuna Yakubu yace zasu gamu seya san shiya taɓa, Yakubu ya zabura ze sake damƙarsa ya taka ya gurin motarsa da sauri ya shige yana cigaba da faɗin
"We shall meet in court, zaka san ni ka daka se ka gane baka da wayo".
Cikin tsawa Audu ya bawa ma'aikatan umarnin su watse kowa ya juya gurin aikinsa. Ya kalli Hajiya dake kuka har sannan Hafsatu ta runguketa itama tana kukan kafin ya mayar da hankalinsa kan Yakubu yana tambayarsa meya faru? Waye wancan É—in kuma meya haÉ—a u harta kai ga duka? Kafin ya bashi sa Hajiya tayi zuruf tace
"Me kuwa ya haɗasu? Magautane sukayi masa turen Aljani haka kawai ya rufeshi da duka saurayin Hafsa ne fa, anga Allah ya fito mata da Miji na nunawa Sa'a shine aka bi yanda akayi shima aka koreshi kuma wlh ba'a taɓa banza ba ko wacece a cikin matanka tayi abin nan ta kwana da shirin zubin Adashi tayi ɗauka kuma dole, ka wuce kai kuma ka kwanta kana tsaye kana wa mutane muzurai ko Aljani ƙarƙuzu ne wlh sekaci ubanka sannan ka koma kan wadda ta aiko ka" ta faɗa tana aikawa da Yakubu wata harara me tafe da gargaɗi. Juyawar yayi kamar yanda tace ya fice daga gidan gaba ɗaya ita ma suka koma ciki da Hafsa dake kuka har sannan.