Sashe 53
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Indai nagarta kike nema a aure to tana gurin Ahmad, idan kuma soyayya da ƙyaleƙyalen rayuwa ce ki auri Jay kuma na tabbatar duk abinda kike hasashen samunsa a gurinsa idan kin bawa Ahmad dama se yayi miki fiye da haka".
Ta isa gaban Baffa tana sunkuyar da kai daga gefe ta tsugunna dan tana hangen hararar da Umma ke aika mata ta hasken farin wata da fitilar data kunna musu a tsakar gidan.
"Mamana na kiraki ne saboda ina so na ji abinda yake a ranki, dukda kwanaki munyi magana amma yanzu ina so ki sake faÉ—amun gaskiyar abinda kikeji game da Ahmad" Baffa ya faÉ—a yana gyara zama. Ta kalli Umma ta sunkuyar da kai, Baffah yace
"Ruƙayya ɗan bamu guri mana"
"Aiko ina nan Malam bazan shiga cikin zafi saboda maganarku ba" Umma ta bashi amsa, yayi murmushi yace
"To ki dena kallonta kar shakkarki tasa ta faÉ—i ba abinda yake cikin zuciyarta ba"
"Uhm" kawai Umma tace ta juya kai. Seda ya sake maimaitawa Fatima tambayar kafin cikin rawar murya tace
"Tsakani da Allah ni Baffah ina kallon Ahmad ne kawai a matsayin Yaya, tsayin lokacin nan nayi masa hannunka me sanda saboda kirkinsa ya wuce na buÉ—e baki nace masa bana sonsa, shi da kansa ya sani tunda yana faÉ—ar haka..."
"Tambayarki kawai nayi me kikeji game dashi a zuciyarki ba wai dogon bayani ba" Baffah ya katseta. Ta duƙar da kai cikin ƙaramin sauti tace
"Banajin komai game dashi Baffah"
"Bakya sonsa so irin na aure kenan?" Baffah ya tambayeta yana tsareta da ido kanta na ƙasa amma taji tasirunsu a jikinta, zuciyarta taki ta tsinke hawaye ya taho mata, daga can ƙasan ranta tana jin tamkar tamkar bata kyauta ba, to amma ya zatayi da muradin tata zuciyar? Idan ta haƙura ta karɓi Ahmad tasan dashi da ita zasu ƙare rayuwarsu ne cikin ƙunci saɓanin haka gara tayi musu gata kowa ya nemi rayuwar da zata dace da muradinsa.
"Banajin sonsa a zuciyata Baffah" ta faɗa cikin rawar murya kafin kuka ya ƙwace mata. Umma ta saki ƙwafa tace
"Munafuka, ai bakiyi kuka ba tukunna, ranar kuka tana tafe"
"Haba Ruƙayya, wannan wace irin magana ce haka? Ya zaki ce mata ranar kuka tana tafe baki fa kikeyi mata?"
"To Malam ina kukan daɗi takeyi yanzu ta yaudari bawan Allah ta ɓata masa lokaci shekara uku yana hidima damu da ita sannan rana tsaka tazo tace bata sonsa wani can daban take so? Ai wlh ko ban faɗa ba haƙƙin Ahmad seya bibiyeta, akan me bata sonsa tsayin lokacin nan bata fito ta faɗa ba? Idan da shegiyar ƙaryarta tace nauyinsa takeji mu ta faɗa mana kota faɗawa yan uwanta ko ƙawayenta mana? Ba zata aureshi ba shekara uku ta barshi yana mana bauta har idan ka hana ya zagaye yaje ya kai mata makaranta ta karɓe suturu da manyan wayar da take riƙewa da ya ruɗo mata wanda take Ƙulafucin Son duk waya ke yi mata su ba Ahmad ɗin bane? Sannan yanzu tazo tace bata sonsa to nidai babu hannuna a ciki ba za'ayi wannan abin kunyar dani ba wlh kuma tunda biye mata zakayi kuje can ku ƙarata Allah ya taimaka" Umma ta tattari kayanta ta shige ɗakin da tace da bazata shiga ba saboda zafi.
Afeeyah na durƙushe gaban Baffah tana kuka kamar ranta ze fita, yayi shiru ya rasa abin faɗi. A sanyaye yace mata
"Kiyi shiru ki saurareni". Ta tsagaita da kukan amma ba gaba É—aya ba. Baffa yace
"A matsayina na Mahaifinki ina da ikon da zanyi miki zaɓin Mijin aure na kuma tursasaki koda bakya so domin Addini ne ya bani damar hakan se dai kuma kema a matsayinki na Ya ba baiwa ba kina da damar da ki kawo naki zaɓin idan har beci karo da Addini ko shari'a ba za'a barki dashi. Auren dole bashi da fa'ida Fatima, yanda na baiwa yar uwarki dama ta kawo zaɓin aurenta kema na baki. Nayi tsammanin lokacin da kika ɗauka tareda Ahmad alamune na cewar kun Aminta da juna, Karatunki da kike da ƙulafuci a tsammatata shine abinda yasa kuka tsahirta tado da zancen aure har se zuwa kin gama.
Baki taɓa nuna wata alama ko faɗi da baki cewar bakya sonsa ba dukda Mahaifiyarku da Yayarki suna yawan kawo mun ƙorafin yanda kike mu'amalantarsa basa jin daɗin hakan, nakanyi miki uzurin yanayin halayyarki ta kasancewarki mutum mara sakewa da mutane sosai ban taɓa tsammatar rashin So ko gamsuwa dashi ne yasa kikeyin hakan ba me yasa kikayi ƙwaron baki ki barshi tsayin wannan lokacin se yanzu da Aski yazo gaban goshi zakice kin fasa baki ganin hakana matsayin cutarwa?" Baffah ya ƙarasa yana tsareta da ido.
Taja hanci, fuskar nan har tayi Jaa kafin tace
"Wlh Baffah nauyi da kunyarsa nakeji shi yasa na kasa faÉ—a masa da baki amma na nuna masa duk wata alama data kamata ace ya gane"
"Da kika ga alamar be gane ba, ko kuma ya gane amma ya cigaba da dagewa domin ya gwada sa'arsa tunda har kika tabbatar bakya ra'ayinsa seki cire wani nauyi ko kunya a gefe ki sanar masa ko ki sanarwa wani ya gaya masa" Baffah ya faÉ—a a É—an fusace. Ta sake rushewa da kuka yayi tsaki yace
"Yanzu da wace fuska kike so na kalli yaron nan? Ni kike so na gaya masa bakyason sa kenan ko wa?"
"Ni Baffah.. Ni wlh ban..." Ta shiga in ina tana kuka ta kasa haÉ—a maganar. Baffah ya ajiye numfashi, gaba É—aya ta jefashi a tsaka mai wuya ya rasa abinda zeyi seya nisa yace mata
"Shi wanda kike so É—in wanene? Kuma É—an gidan wanene?"
"Sunansa Jafar, Ɗan ƙwallo ne, Mahaifansa duka yan Kano ne amma shi a Turai yake can yake sana'arsa" ta bashi amsa cikin sauri ya kalleta kafin ya sake tambayar s ina suka haɗu nan ma ta gaya masa. Yayi shiru na tsayin lokaci, zuciyarta ta shiga tsinkewa dalilin shirun nasa. Shidai shine me bayar da auranta, idan be amince da wannan batu ba to fa ko zata mutu tilas ta haƙura da Jafar.
Ba kalar Addu'ar da batayi a zuciyarta ba a lokacin can Baffah ya nisa yace
"Ahmad yaron kirki ne Afeeyah, babu uban da zeso ya rasa nagartaccen siriki irinsa" batasan sanda santsin bakinta ya jata tace masa
"Wlh shima Jafar É—in yanada nagarta dan baka sanshi bane" takaici ya saka Baffah yin murmushi kafin yace
"Ki gaya masa yazo ina son ganinsa gobe".
Cikin tsananin murna da zumuÉ—in hango nasara muraran tace
"Bayanan Baffah, ranar Lahadin nan ze dawo kuma daman yace da ya dawo zezo ya gaisheku".
"Fatima!" Baffah ya ambaci Asalin sunanta da kakkausar murya, murnar data fara ta datse, tsoro da fargaba suka maye gurbinta dalilin tun tashinta ba zata ce ga rana É—aya da Baffah ya kirata da Fatima ba kuma da kakkausan sauti irin wannan. Baffan yaci gaba da magana cikin muryar gargaÉ—i da nuna tabbacin abinda yake magana akai.
"Ranar Lahadi kikace ze dawo ƙasar nan, tsakanin Lahadi zuwa Juma'a ki tabbatar ki fitar da ranar daze zo ni dashi mu gana. Ba zan tursasaki ki auri abinda bashi ne muradin zuciyarki ba, zan binciki ko wanene wanda kike so ɗin amma ki sani muddin naci karo da wani abu dangane dashi da beyi mun ba ba zan sake zama dake ko neman shawararki ba, Ahmad shine zaɓin da zuciyata ta aminta dashi kuma shi zanaura miki".
Kwana tayi tana juyayin maganar Baffah a zuciyarta. Tana jiyo sababin da Umma ta ringayi bayan tashinta daga gurinsa tana tambayarsa kenan ya goya mata baya? Me ze cewa Ahmad?
"Na sani Ahmad yaro ne hankali da nutsuwa, shi rabon aure dana haihuwa basa canzuwa, wani baya auranmatar wani kamar yanda hausawa sukace MATAR MUTUM Kabarinsa, hikimar zancen shine ba'a binne wani mutum cikin kabarin wani kamar yanda wani baze zarga igiyar auransa kan macen dake ɗauke da igiyoyin wani kafin shi ba. Muyi mata addu'a, wannan gaɓar itace gaɓa mafi muhimmanci a rayuwar Mace, idan tayi dacen abokin zama na gari rayuwarta ta inganta haka zalika idan akayi rashin dace rayuwa ta shiga wani hali ina roƙonki da ki tattare duk wani fushi naki ki ajiye shi a gefe kiyi mata addu'a itace abinda tafi buƙata yanzu dama da zagi da hantarar da kikeyi mata.
Tun a daren ta sanar da Jay,
"Wannan shine first Agenda na, neman auranki is number one on my to do list dana sauka a Nigeria, ina fatan Allah yasa nayiwa Baffanki, karyace baze bawa mutum irina auranki ba kinsan fa akwai mutane da yawa da suka ce Ball ba sana'a bace ba, da akwai Friend ɗina da aka hana aure Baban yarinyar da yake so yace bashida sa'a and haka ya haƙura ya auri wata" inji Jay daga nan suka cigaba da shirye shiryen yanda abubuwa zasu kasance musu.
Da sukayi waya da Badar ma ta gaya mata abinda Baffa yace,
"Allah ya zaɓa miki mafi Alkhairi Afeeyah" Badar ta faɗata amsa mata da cewar
"Amin idan da gaske kikeyi"
"Uhm Afeeyah kenan, a bazanji tsoronki in fasa cewa mi dai nafi sonki da Ahmad ba kuma ko Baffan har ransa yafi son Ahmad kawai ya baki damarki ne kuma da kina da tunani seki haƙura kawai ki bi abinda yake so" Badar ta sake faɗi ƙit kuwa ta kashe wayarta dan bata son abinda ze canza mata mood ɗinta na farin cikin dawowar Jay.
A gidan Anty Sauda ta shirya tarbarsa, ya sanar mata ya sauka Kano da ranar Litinin zuwa Yamma zeje ya ganta dan baze iya sake kwana guda a Naija ba tare da yaga fuskarta ba. Tsabar takaicin rawar jikin da takeyi Anty Sauda ficewa tayi daga gidan ta barta da masu aiki suna tayata, sanda ta dawo kuwa gani tayi kamar an canza gidan, tana tsammanin har bango Afeeyah ta wanke mata yau ko ina yayi haske ga ƙamshi kamar gidan sabuwar Amaryar Kanuri.
Ta isa gaban Baffa tana sunkuyar da kai daga gefe ta tsugunna dan tana hangen hararar da Umma ke aika mata ta hasken farin wata da fitilar data kunna musu a tsakar gidan.
"Mamana na kiraki ne saboda ina so na ji abinda yake a ranki, dukda kwanaki munyi magana amma yanzu ina so ki sake faÉ—amun gaskiyar abinda kikeji game da Ahmad" Baffa ya faÉ—a yana gyara zama. Ta kalli Umma ta sunkuyar da kai, Baffah yace
"Ruƙayya ɗan bamu guri mana"
"Aiko ina nan Malam bazan shiga cikin zafi saboda maganarku ba" Umma ta bashi amsa, yayi murmushi yace
"To ki dena kallonta kar shakkarki tasa ta faÉ—i ba abinda yake cikin zuciyarta ba"
"Uhm" kawai Umma tace ta juya kai. Seda ya sake maimaitawa Fatima tambayar kafin cikin rawar murya tace
"Tsakani da Allah ni Baffah ina kallon Ahmad ne kawai a matsayin Yaya, tsayin lokacin nan nayi masa hannunka me sanda saboda kirkinsa ya wuce na buÉ—e baki nace masa bana sonsa, shi da kansa ya sani tunda yana faÉ—ar haka..."
"Tambayarki kawai nayi me kikeji game dashi a zuciyarki ba wai dogon bayani ba" Baffah ya katseta. Ta duƙar da kai cikin ƙaramin sauti tace
"Banajin komai game dashi Baffah"
"Bakya sonsa so irin na aure kenan?" Baffah ya tambayeta yana tsareta da ido kanta na ƙasa amma taji tasirunsu a jikinta, zuciyarta taki ta tsinke hawaye ya taho mata, daga can ƙasan ranta tana jin tamkar tamkar bata kyauta ba, to amma ya zatayi da muradin tata zuciyar? Idan ta haƙura ta karɓi Ahmad tasan dashi da ita zasu ƙare rayuwarsu ne cikin ƙunci saɓanin haka gara tayi musu gata kowa ya nemi rayuwar da zata dace da muradinsa.
"Banajin sonsa a zuciyata Baffah" ta faɗa cikin rawar murya kafin kuka ya ƙwace mata. Umma ta saki ƙwafa tace
"Munafuka, ai bakiyi kuka ba tukunna, ranar kuka tana tafe"
"Haba Ruƙayya, wannan wace irin magana ce haka? Ya zaki ce mata ranar kuka tana tafe baki fa kikeyi mata?"
"To Malam ina kukan daɗi takeyi yanzu ta yaudari bawan Allah ta ɓata masa lokaci shekara uku yana hidima damu da ita sannan rana tsaka tazo tace bata sonsa wani can daban take so? Ai wlh ko ban faɗa ba haƙƙin Ahmad seya bibiyeta, akan me bata sonsa tsayin lokacin nan bata fito ta faɗa ba? Idan da shegiyar ƙaryarta tace nauyinsa takeji mu ta faɗa mana kota faɗawa yan uwanta ko ƙawayenta mana? Ba zata aureshi ba shekara uku ta barshi yana mana bauta har idan ka hana ya zagaye yaje ya kai mata makaranta ta karɓe suturu da manyan wayar da take riƙewa da ya ruɗo mata wanda take Ƙulafucin Son duk waya ke yi mata su ba Ahmad ɗin bane? Sannan yanzu tazo tace bata sonsa to nidai babu hannuna a ciki ba za'ayi wannan abin kunyar dani ba wlh kuma tunda biye mata zakayi kuje can ku ƙarata Allah ya taimaka" Umma ta tattari kayanta ta shige ɗakin da tace da bazata shiga ba saboda zafi.
Afeeyah na durƙushe gaban Baffah tana kuka kamar ranta ze fita, yayi shiru ya rasa abin faɗi. A sanyaye yace mata
"Kiyi shiru ki saurareni". Ta tsagaita da kukan amma ba gaba É—aya ba. Baffa yace
"A matsayina na Mahaifinki ina da ikon da zanyi miki zaɓin Mijin aure na kuma tursasaki koda bakya so domin Addini ne ya bani damar hakan se dai kuma kema a matsayinki na Ya ba baiwa ba kina da damar da ki kawo naki zaɓin idan har beci karo da Addini ko shari'a ba za'a barki dashi. Auren dole bashi da fa'ida Fatima, yanda na baiwa yar uwarki dama ta kawo zaɓin aurenta kema na baki. Nayi tsammanin lokacin da kika ɗauka tareda Ahmad alamune na cewar kun Aminta da juna, Karatunki da kike da ƙulafuci a tsammatata shine abinda yasa kuka tsahirta tado da zancen aure har se zuwa kin gama.
Baki taɓa nuna wata alama ko faɗi da baki cewar bakya sonsa ba dukda Mahaifiyarku da Yayarki suna yawan kawo mun ƙorafin yanda kike mu'amalantarsa basa jin daɗin hakan, nakanyi miki uzurin yanayin halayyarki ta kasancewarki mutum mara sakewa da mutane sosai ban taɓa tsammatar rashin So ko gamsuwa dashi ne yasa kikeyin hakan ba me yasa kikayi ƙwaron baki ki barshi tsayin wannan lokacin se yanzu da Aski yazo gaban goshi zakice kin fasa baki ganin hakana matsayin cutarwa?" Baffah ya ƙarasa yana tsareta da ido.
Taja hanci, fuskar nan har tayi Jaa kafin tace
"Wlh Baffah nauyi da kunyarsa nakeji shi yasa na kasa faÉ—a masa da baki amma na nuna masa duk wata alama data kamata ace ya gane"
"Da kika ga alamar be gane ba, ko kuma ya gane amma ya cigaba da dagewa domin ya gwada sa'arsa tunda har kika tabbatar bakya ra'ayinsa seki cire wani nauyi ko kunya a gefe ki sanar masa ko ki sanarwa wani ya gaya masa" Baffah ya faÉ—a a É—an fusace. Ta sake rushewa da kuka yayi tsaki yace
"Yanzu da wace fuska kike so na kalli yaron nan? Ni kike so na gaya masa bakyason sa kenan ko wa?"
"Ni Baffah.. Ni wlh ban..." Ta shiga in ina tana kuka ta kasa haÉ—a maganar. Baffah ya ajiye numfashi, gaba É—aya ta jefashi a tsaka mai wuya ya rasa abinda zeyi seya nisa yace mata
"Shi wanda kike so É—in wanene? Kuma É—an gidan wanene?"
"Sunansa Jafar, Ɗan ƙwallo ne, Mahaifansa duka yan Kano ne amma shi a Turai yake can yake sana'arsa" ta bashi amsa cikin sauri ya kalleta kafin ya sake tambayar s ina suka haɗu nan ma ta gaya masa. Yayi shiru na tsayin lokaci, zuciyarta ta shiga tsinkewa dalilin shirun nasa. Shidai shine me bayar da auranta, idan be amince da wannan batu ba to fa ko zata mutu tilas ta haƙura da Jafar.
Ba kalar Addu'ar da batayi a zuciyarta ba a lokacin can Baffah ya nisa yace
"Ahmad yaron kirki ne Afeeyah, babu uban da zeso ya rasa nagartaccen siriki irinsa" batasan sanda santsin bakinta ya jata tace masa
"Wlh shima Jafar É—in yanada nagarta dan baka sanshi bane" takaici ya saka Baffah yin murmushi kafin yace
"Ki gaya masa yazo ina son ganinsa gobe".
Cikin tsananin murna da zumuÉ—in hango nasara muraran tace
"Bayanan Baffah, ranar Lahadin nan ze dawo kuma daman yace da ya dawo zezo ya gaisheku".
"Fatima!" Baffah ya ambaci Asalin sunanta da kakkausar murya, murnar data fara ta datse, tsoro da fargaba suka maye gurbinta dalilin tun tashinta ba zata ce ga rana É—aya da Baffah ya kirata da Fatima ba kuma da kakkausan sauti irin wannan. Baffan yaci gaba da magana cikin muryar gargaÉ—i da nuna tabbacin abinda yake magana akai.
"Ranar Lahadi kikace ze dawo ƙasar nan, tsakanin Lahadi zuwa Juma'a ki tabbatar ki fitar da ranar daze zo ni dashi mu gana. Ba zan tursasaki ki auri abinda bashi ne muradin zuciyarki ba, zan binciki ko wanene wanda kike so ɗin amma ki sani muddin naci karo da wani abu dangane dashi da beyi mun ba ba zan sake zama dake ko neman shawararki ba, Ahmad shine zaɓin da zuciyata ta aminta dashi kuma shi zanaura miki".
Kwana tayi tana juyayin maganar Baffah a zuciyarta. Tana jiyo sababin da Umma ta ringayi bayan tashinta daga gurinsa tana tambayarsa kenan ya goya mata baya? Me ze cewa Ahmad?
"Na sani Ahmad yaro ne hankali da nutsuwa, shi rabon aure dana haihuwa basa canzuwa, wani baya auranmatar wani kamar yanda hausawa sukace MATAR MUTUM Kabarinsa, hikimar zancen shine ba'a binne wani mutum cikin kabarin wani kamar yanda wani baze zarga igiyar auransa kan macen dake ɗauke da igiyoyin wani kafin shi ba. Muyi mata addu'a, wannan gaɓar itace gaɓa mafi muhimmanci a rayuwar Mace, idan tayi dacen abokin zama na gari rayuwarta ta inganta haka zalika idan akayi rashin dace rayuwa ta shiga wani hali ina roƙonki da ki tattare duk wani fushi naki ki ajiye shi a gefe kiyi mata addu'a itace abinda tafi buƙata yanzu dama da zagi da hantarar da kikeyi mata.
Tun a daren ta sanar da Jay,
"Wannan shine first Agenda na, neman auranki is number one on my to do list dana sauka a Nigeria, ina fatan Allah yasa nayiwa Baffanki, karyace baze bawa mutum irina auranki ba kinsan fa akwai mutane da yawa da suka ce Ball ba sana'a bace ba, da akwai Friend ɗina da aka hana aure Baban yarinyar da yake so yace bashida sa'a and haka ya haƙura ya auri wata" inji Jay daga nan suka cigaba da shirye shiryen yanda abubuwa zasu kasance musu.
Da sukayi waya da Badar ma ta gaya mata abinda Baffa yace,
"Allah ya zaɓa miki mafi Alkhairi Afeeyah" Badar ta faɗata amsa mata da cewar
"Amin idan da gaske kikeyi"
"Uhm Afeeyah kenan, a bazanji tsoronki in fasa cewa mi dai nafi sonki da Ahmad ba kuma ko Baffan har ransa yafi son Ahmad kawai ya baki damarki ne kuma da kina da tunani seki haƙura kawai ki bi abinda yake so" Badar ta sake faɗi ƙit kuwa ta kashe wayarta dan bata son abinda ze canza mata mood ɗinta na farin cikin dawowar Jay.
A gidan Anty Sauda ta shirya tarbarsa, ya sanar mata ya sauka Kano da ranar Litinin zuwa Yamma zeje ya ganta dan baze iya sake kwana guda a Naija ba tare da yaga fuskarta ba. Tsabar takaicin rawar jikin da takeyi Anty Sauda ficewa tayi daga gidan ta barta da masu aiki suna tayata, sanda ta dawo kuwa gani tayi kamar an canza gidan, tana tsammanin har bango Afeeyah ta wanke mata yau ko ina yayi haske ga ƙamshi kamar gidan sabuwar Amaryar Kanuri.