Sashe 66
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Toh Allah ya bashi lafiya, se a sanarwa uwarsa ai" Alhajin ya bashi amsa, se yaji abin wani banbara kwai ba yanda Alhajin ya saba ruwa da tsaki a lamarin Yayan Hajiya ba, koda yake daman ko a cikinsu basu fiya jituwa da Jafar ɗinba saboda rikici da taurin kansa sak irin na Alhajin ne dukda yanda Hajiya take so ya zama yafi kowa shiga jikinsa amma abin yaci tura shiyasa take baƙin ciki da shirin da sukeyi da Ahmad a yanzu. Daya gayawa Hajiya kuka ta ringa zundumawa harda tumami a Ƙasa tana kiran ta shiga uku ta lalace shike nan magauta sunci galaba akanta. Ta tattara ta tafi Asibiti can ta tare ita da jama'arta da surukanta data ringa wa waya tana gaya musu suzo an jefe Jay gashi kwnace magashiyyan a gadon Asibiti, Turai ta tafi mata tambaya dan su binciko wanda ya taɓa Jafar ɗin, Momy da Anty sunje sun dubashi da daddare se sannan Ahmad ya koma saboda Hajiya da take a gurin tana ta faɗar maganganu akansa, Alhaji ne yace shi yaje ya kwana da Jafar ita da jama'arsa kowa ya watse ya koma gida. Daze tafi ya tafi masa da wayarsa wadda yaga Missed calls ɗin Afeeyah sunfi Ashirin ga messages nan birjik na ban haƙuri akan laifin da besan me ta masa ba.
Ya jefa wayar a Aljihu, besan password É—insa ba daya buÉ—e wayar ya kirata ya sanar mata abinda yake faruwa kodan hankalinta ya kwanta. Yana dabda shiga Asibitin ta sake kira ya amsa cikin nutsuwarsa yayi sallama.
FATIMA
Tana shiga cikin gida kaitsaye É—akinta ta shige tana jiyo Umma da Baffah suna magana Baffa yana cewa
"Wlh Ruƙayya ban taɓa zaton haka zanji nauyin yaron nan ba, badan fa ya rigada ya ganni ba juyawa nayi niyyaryi amma babu dama"
Umma tayi shewa tace
"Malam, ai baka ma soma jin kunya ba se ranar daya fahimci yaudarar daka shirya masa kaida yarka, billahillazi in bakayi wasa ba seka gagara fita na wasu kwanaki saboda zancen mutane da nunaka da za'a ringayi". Sama sama take jiyo mahawarar Baffa da Umman, ta zauna kan katifa tana dafe da ƙirjiz seda ta nutsu kafin ta latsa kiran layin Jay tana so taji ina ya tsaya tunda Allah ya taimaka ta sallami Ahmad yanzu se yazo. Wayar ta ƙaraci ringing be amsa ba ta sake kira nan ma dai shiru seta ajiye a zuwan ko yana hanya idan ya iso ze kirata amma shiru shiru har sha ɗaya babu Jay babu dalilinsa kuma be biyo kiranta ba zuwa sannan kuma hankalinta idan yayi dubu ya tashi to me ya faru? Kar dai yazo ya ganta tareda Ahmad shiyasa yayi zuciya ya tafi kuma yaƙi amsa wayarta.
Data sake kira tana fara ringing aka katse, cikin sauri ta sake gwada kiran a zatonta ko garin ya amsa ne ya katse ita bama zata iya jira ya kirata ba sedai a karo na biyun aka shaida mata wayar a kashe take. Ta kwanta lamo hawaye na zubowa daga idonta, rejecting yayi kuma ya kashe wayar dan karta dameshi ta tannata yazo ya ganta tareda Ahmad kenan.
Tsohuwar wayar dayace ta dena amfani da ita ta ɗauka ta saka sim ta kunna Data, WhatsApp ta shiga dan ta duba ko yana online bata tsaya duba duk saƙonnin da suke ta tuntuɗowa ba ta wuce kan number sa. Mamaki ya kamata ganin Dp sa ya sauka sannan babu about hakan kuma tasan yana nufin yayi blocking nata kenanseta saki wayar a Ƙasa ta rushe da kuka, Umma na tsakar gida tana tattare kaya saboda hadari daya taso har an fara iska ta jiyo kukan nata da sauri ta leƙa ɗakin,
"Lafiyarki Afeeyah? Kukan me kikeyi me ya sameki?" Umma ta tambayeta. Cikin kukan tace mata
"Jafar ne Umma" Umman taja wani shegen tsaki ta sakar mata labule ta cigaba da abinda takeyi ranta na suya, idan ta buɗe baki zagi zata zunduma mata shiyasa tayi shiru. Afeeyah tasha kuka ta gode Allah a daren kafin safiya ta ɗora da kiran layin Jay da jera masa Texts na ban haƙuri da rantsuwar duk abinda ya gani yake tunani ba gaskiya bane ba amma shiru kamar an shuka dusa be amsa kira ko guda ba haka be bata amsa ba. Zazzaɓi ne da ciwon kan gaske itama ya lafketa haka ta wuni a ɗaki Umma bata bi ta kanta ba seda Allah ya taimaketa Anty Sauda taje ita ta bata abinci da magani tasha harta samu ƙarfin cigaba da kiran Jay ɗin. Kiran ƙarshe da tayi shine Ahmad ya amsa, ta saki ajiyar zuciya me ƙarfi sanda taga sakanni sun fara tafiya.
Muryar Ahmad me sanyi ta ratsa kunnenta, ba muryar Jay bace seda ta zare wayar ta duba dan ta tabbatar da wata kirane taga number Jay ce. Cikin muryarta data dashe dalilin kuka ta amsa sallamar kafin tace
"Dan Allah Jafar fa? Yana kusa?"
"Bashida lafiya yana kwance a Asibiti" Ahmad ya bata amsa, a rikice tace
"Yaushe? Meya sameshi? Wane Asibiti yake?"
"Relax, malaria ce inaga sauron gidanku ne basu san baƙo ba suka cijeshi, yanzu zan shiga gurinsa zan bashi wayar seya kiraki ok?" Ahmad ya faɗi. Ta sake sauke ajiyar rai, muryar kama take mata da ta Ahmad amma babu dalilin da ze sanya Ahmad ya samu wayar Jay
"Nagode toh ina jira" ta faɗi kafin ta sauke wayar ta doka tagumi tana jiran taga an kira kamar yanda yace, tunani take tana ƙarfafawa kanta guiwa dukda hankalinta ya tashi dajin bashida lafiya, ta yuwu ma beje ba jiyan ba ganinta da Ahmad bane ya ɓata masa rai, ƙila ma ko be hau Online bane shi yasa taga kamar yayi blocking nata a WhatsApp amma ba haka bane. Shiru tana ta tunani har minti kusan ashirin ya wuce ba'a kira ba kamar yanda wanda ya amsa wayar ya ce mata ze kai masa yanzu se kawai ta yanke shawarar ta sake kira kodan taji ya jikinsa da kuma abinda yake damunsa.
AHMAD
Sau biyu kenan da yake jin muryar budurwar Jay tamkar ta Fatima, daya isa ɗakin ya tarar da Manager shi tareda sauran jama'arsa wannan tasa be bashi wayar ba ya ajiye masa ita kawai akan Drawer ya fita zuwa gurin Dr Hassan, Jay kuwa bayan ya sallami baƙinsa ya ɗauki wayarsa da through out yau be riƙe ta ba. Missed calls ɗinta ya fara gani, wani abu ya soki ransa, daga safiyar zuwa yanzu yayi ƙoƙarin ganin ya rage damuwarta a ransa, a maimakon matsantawa kansa da son gano dalilinta na aikata musu wannan abun seya mayar da hankali gurin tunanin ta yanda ze hukuntata dan ba zata ci banza ba tilas ya maida mata da mugun nufinta akansu. Tunaninsa ɗaya yanda Ahmad ze karɓi Al'amarin idan ya sanar masa, baze bari taci gaba da cutar da shi ba daga ƙarshe ta karya masa zuciya tamkar yanda tayi masa.
Shi yana da taurin ran da ze shanye damuwarta amma baya tsammanin Yah Ahmad ze iya, he is so much into the girl.
"Kaima kana sonta" zuciyarsa ta raya masa, se yayi saurim kawar da tunanin daga ransa domin shine rauninsa. Allah ya sani yana Son ta, so na gaskiya saboda Allah badan wani abu ba amma kuma kash koda ace babu wata manufa game dasu a ranta, ya zama ace abinda ya faru Arashine daga Allah tilas shi ze haƙura da ita domin Ahmad ya rigashi zuwa gurin kai ko ba haka ba ko da ace tasa ce Yah Ahmad yace yana so ze bar masa. Ringing da wayar ta fara ya katse masa tunani, yana kallo harta katse kafin ta sake kira yayi adding nata to blocklist, a fili yake so ya wanke ta, face to face yake so ya warware mata komai ta yanda zata fi ji a jikinta.
Haka yayi jinyar kwana biyu aka sallameshi kullum a Asibitin Hajiya da jama'arta suke wuni tamkar wani biki se dare Ahmad kuma yaje ya kwana dashi. A taƙin kwanaki biyun yayi rama fuskarsa kuma ta gagara ɓoye abinda yake ransa amma se yake boyewa da sunan ciwo. Kwanansa biyu da dawowa gida ya fara shirin komawa France. Da niyyar sati huɗu yazo gida, sati huɗun da yake cewa kafin cikarsu za'a ɗaura musu Aure da Afeeyah se gashi komai ya canza ko cikakken sati biyu beyi ba yana cewa ze koma. Hajiya daman cewa tayi gara ya tafi, Turai tace anyi Ƙaiƙayi koma kan masheƙiya shiyasa ma ya samu sauƙi ya tashi saboda an san ko an bashi magani ko hayaƙi bayi zeyi ba se aka masa aikeb kai tsaye wai Malam ya saka hadimansa sun saka maganin a jikinsa.
Ahmad ne kaɗai ya damu da konawar da zeyi domin ya gagara yarda wai Malaria ce take damun Jafar, akwai wani abu daya ɓoye masa kuma ya gagara tambayarsa kamar yanda shima Jay ya kasa furta masa abinda yake ci masa zuciya. Yayi Ƙoƙarin magana da Ahmad tun yana Asibiti, ya tambayeshi kan yanzu ace masa Fatima yaudararsa takeyi bayanshi da akwai wani da take kulawa kuma shi take so yaya zeji?
"Already na sani, bayan ni da akwai wani da take tare dashi kuma shi take so bani ba, ya ci ace na haƙura da ita Jafar, amma na kasa. Ni da kaina bansan irin son da nakewa yarinyar nan ba kawai dai ina cigaba da addu'a idan rabo na ce Allah ya bani idan ba tawa bace Allah ya musanya mun da wadda ta fita Alkhairi" amsar da Ahmad ya bashi kenan data sanyaya masa jiki tasa kuma ya fasa faɗa masa gaskiyar abinda ya faru to ta ina ma ze fara? Ya Ahmad zeji? Se kawai ya shanye damuwarsa shi kaɗai ya kuma cigaba da addu'ar Allah ya tarwatsa tarayyar su da Ahmad domin ita ba Alkhairi bace a rayuwarsu.
Ranar talata data kama saura kwanaki biyu Jay ya wuce Baba Alƙali ya kirashi akan yaje gida ya same shi yana son magana dashi. Shi kaɗai ya tafi yauma daman Ahmad baya nan ya tafi Jigawa inda yake noman shinkafa dan da tare ma zasuje Hajiya ta hanashi binsa.
Ya jefa wayar a Aljihu, besan password É—insa ba daya buÉ—e wayar ya kirata ya sanar mata abinda yake faruwa kodan hankalinta ya kwanta. Yana dabda shiga Asibitin ta sake kira ya amsa cikin nutsuwarsa yayi sallama.
FATIMA
Tana shiga cikin gida kaitsaye É—akinta ta shige tana jiyo Umma da Baffah suna magana Baffa yana cewa
"Wlh Ruƙayya ban taɓa zaton haka zanji nauyin yaron nan ba, badan fa ya rigada ya ganni ba juyawa nayi niyyaryi amma babu dama"
Umma tayi shewa tace
"Malam, ai baka ma soma jin kunya ba se ranar daya fahimci yaudarar daka shirya masa kaida yarka, billahillazi in bakayi wasa ba seka gagara fita na wasu kwanaki saboda zancen mutane da nunaka da za'a ringayi". Sama sama take jiyo mahawarar Baffa da Umman, ta zauna kan katifa tana dafe da ƙirjiz seda ta nutsu kafin ta latsa kiran layin Jay tana so taji ina ya tsaya tunda Allah ya taimaka ta sallami Ahmad yanzu se yazo. Wayar ta ƙaraci ringing be amsa ba ta sake kira nan ma dai shiru seta ajiye a zuwan ko yana hanya idan ya iso ze kirata amma shiru shiru har sha ɗaya babu Jay babu dalilinsa kuma be biyo kiranta ba zuwa sannan kuma hankalinta idan yayi dubu ya tashi to me ya faru? Kar dai yazo ya ganta tareda Ahmad shiyasa yayi zuciya ya tafi kuma yaƙi amsa wayarta.
Data sake kira tana fara ringing aka katse, cikin sauri ta sake gwada kiran a zatonta ko garin ya amsa ne ya katse ita bama zata iya jira ya kirata ba sedai a karo na biyun aka shaida mata wayar a kashe take. Ta kwanta lamo hawaye na zubowa daga idonta, rejecting yayi kuma ya kashe wayar dan karta dameshi ta tannata yazo ya ganta tareda Ahmad kenan.
Tsohuwar wayar dayace ta dena amfani da ita ta ɗauka ta saka sim ta kunna Data, WhatsApp ta shiga dan ta duba ko yana online bata tsaya duba duk saƙonnin da suke ta tuntuɗowa ba ta wuce kan number sa. Mamaki ya kamata ganin Dp sa ya sauka sannan babu about hakan kuma tasan yana nufin yayi blocking nata kenanseta saki wayar a Ƙasa ta rushe da kuka, Umma na tsakar gida tana tattare kaya saboda hadari daya taso har an fara iska ta jiyo kukan nata da sauri ta leƙa ɗakin,
"Lafiyarki Afeeyah? Kukan me kikeyi me ya sameki?" Umma ta tambayeta. Cikin kukan tace mata
"Jafar ne Umma" Umman taja wani shegen tsaki ta sakar mata labule ta cigaba da abinda takeyi ranta na suya, idan ta buɗe baki zagi zata zunduma mata shiyasa tayi shiru. Afeeyah tasha kuka ta gode Allah a daren kafin safiya ta ɗora da kiran layin Jay da jera masa Texts na ban haƙuri da rantsuwar duk abinda ya gani yake tunani ba gaskiya bane ba amma shiru kamar an shuka dusa be amsa kira ko guda ba haka be bata amsa ba. Zazzaɓi ne da ciwon kan gaske itama ya lafketa haka ta wuni a ɗaki Umma bata bi ta kanta ba seda Allah ya taimaketa Anty Sauda taje ita ta bata abinci da magani tasha harta samu ƙarfin cigaba da kiran Jay ɗin. Kiran ƙarshe da tayi shine Ahmad ya amsa, ta saki ajiyar zuciya me ƙarfi sanda taga sakanni sun fara tafiya.
Muryar Ahmad me sanyi ta ratsa kunnenta, ba muryar Jay bace seda ta zare wayar ta duba dan ta tabbatar da wata kirane taga number Jay ce. Cikin muryarta data dashe dalilin kuka ta amsa sallamar kafin tace
"Dan Allah Jafar fa? Yana kusa?"
"Bashida lafiya yana kwance a Asibiti" Ahmad ya bata amsa, a rikice tace
"Yaushe? Meya sameshi? Wane Asibiti yake?"
"Relax, malaria ce inaga sauron gidanku ne basu san baƙo ba suka cijeshi, yanzu zan shiga gurinsa zan bashi wayar seya kiraki ok?" Ahmad ya faɗi. Ta sake sauke ajiyar rai, muryar kama take mata da ta Ahmad amma babu dalilin da ze sanya Ahmad ya samu wayar Jay
"Nagode toh ina jira" ta faɗi kafin ta sauke wayar ta doka tagumi tana jiran taga an kira kamar yanda yace, tunani take tana ƙarfafawa kanta guiwa dukda hankalinta ya tashi dajin bashida lafiya, ta yuwu ma beje ba jiyan ba ganinta da Ahmad bane ya ɓata masa rai, ƙila ma ko be hau Online bane shi yasa taga kamar yayi blocking nata a WhatsApp amma ba haka bane. Shiru tana ta tunani har minti kusan ashirin ya wuce ba'a kira ba kamar yanda wanda ya amsa wayar ya ce mata ze kai masa yanzu se kawai ta yanke shawarar ta sake kira kodan taji ya jikinsa da kuma abinda yake damunsa.
AHMAD
Sau biyu kenan da yake jin muryar budurwar Jay tamkar ta Fatima, daya isa ɗakin ya tarar da Manager shi tareda sauran jama'arsa wannan tasa be bashi wayar ba ya ajiye masa ita kawai akan Drawer ya fita zuwa gurin Dr Hassan, Jay kuwa bayan ya sallami baƙinsa ya ɗauki wayarsa da through out yau be riƙe ta ba. Missed calls ɗinta ya fara gani, wani abu ya soki ransa, daga safiyar zuwa yanzu yayi ƙoƙarin ganin ya rage damuwarta a ransa, a maimakon matsantawa kansa da son gano dalilinta na aikata musu wannan abun seya mayar da hankali gurin tunanin ta yanda ze hukuntata dan ba zata ci banza ba tilas ya maida mata da mugun nufinta akansu. Tunaninsa ɗaya yanda Ahmad ze karɓi Al'amarin idan ya sanar masa, baze bari taci gaba da cutar da shi ba daga ƙarshe ta karya masa zuciya tamkar yanda tayi masa.
Shi yana da taurin ran da ze shanye damuwarta amma baya tsammanin Yah Ahmad ze iya, he is so much into the girl.
"Kaima kana sonta" zuciyarsa ta raya masa, se yayi saurim kawar da tunanin daga ransa domin shine rauninsa. Allah ya sani yana Son ta, so na gaskiya saboda Allah badan wani abu ba amma kuma kash koda ace babu wata manufa game dasu a ranta, ya zama ace abinda ya faru Arashine daga Allah tilas shi ze haƙura da ita domin Ahmad ya rigashi zuwa gurin kai ko ba haka ba ko da ace tasa ce Yah Ahmad yace yana so ze bar masa. Ringing da wayar ta fara ya katse masa tunani, yana kallo harta katse kafin ta sake kira yayi adding nata to blocklist, a fili yake so ya wanke ta, face to face yake so ya warware mata komai ta yanda zata fi ji a jikinta.
Haka yayi jinyar kwana biyu aka sallameshi kullum a Asibitin Hajiya da jama'arta suke wuni tamkar wani biki se dare Ahmad kuma yaje ya kwana dashi. A taƙin kwanaki biyun yayi rama fuskarsa kuma ta gagara ɓoye abinda yake ransa amma se yake boyewa da sunan ciwo. Kwanansa biyu da dawowa gida ya fara shirin komawa France. Da niyyar sati huɗu yazo gida, sati huɗun da yake cewa kafin cikarsu za'a ɗaura musu Aure da Afeeyah se gashi komai ya canza ko cikakken sati biyu beyi ba yana cewa ze koma. Hajiya daman cewa tayi gara ya tafi, Turai tace anyi Ƙaiƙayi koma kan masheƙiya shiyasa ma ya samu sauƙi ya tashi saboda an san ko an bashi magani ko hayaƙi bayi zeyi ba se aka masa aikeb kai tsaye wai Malam ya saka hadimansa sun saka maganin a jikinsa.
Ahmad ne kaɗai ya damu da konawar da zeyi domin ya gagara yarda wai Malaria ce take damun Jafar, akwai wani abu daya ɓoye masa kuma ya gagara tambayarsa kamar yanda shima Jay ya kasa furta masa abinda yake ci masa zuciya. Yayi Ƙoƙarin magana da Ahmad tun yana Asibiti, ya tambayeshi kan yanzu ace masa Fatima yaudararsa takeyi bayanshi da akwai wani da take kulawa kuma shi take so yaya zeji?
"Already na sani, bayan ni da akwai wani da take tare dashi kuma shi take so bani ba, ya ci ace na haƙura da ita Jafar, amma na kasa. Ni da kaina bansan irin son da nakewa yarinyar nan ba kawai dai ina cigaba da addu'a idan rabo na ce Allah ya bani idan ba tawa bace Allah ya musanya mun da wadda ta fita Alkhairi" amsar da Ahmad ya bashi kenan data sanyaya masa jiki tasa kuma ya fasa faɗa masa gaskiyar abinda ya faru to ta ina ma ze fara? Ya Ahmad zeji? Se kawai ya shanye damuwarsa shi kaɗai ya kuma cigaba da addu'ar Allah ya tarwatsa tarayyar su da Ahmad domin ita ba Alkhairi bace a rayuwarsu.
Ranar talata data kama saura kwanaki biyu Jay ya wuce Baba Alƙali ya kirashi akan yaje gida ya same shi yana son magana dashi. Shi kaɗai ya tafi yauma daman Ahmad baya nan ya tafi Jigawa inda yake noman shinkafa dan da tare ma zasuje Hajiya ta hanashi binsa.