Sashe 36
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ikon Allah" ta fada a zuciyata bangare daya kuma haushin wai girlfriend É—insa da taji ya ce ya kamata har bata san sanda bakinta ya furta
"Oh saboda nayi kama da Ex Girlfriend É—inka yasa ka kulani kenan?"
"Ko ɗaya, sanda nake tare da ita ma she was the one pushing the relationship and i supported her just because she was nice, Zoya was the most beautiful soul i have ever met in my life tana da kirki na ƙarshe ta so ni she really wanted to marry me kuma ko ni i lokacin idan da zanyi aure it will be her but unfortunately she lost her life in a plane crash ta tafi ganin Mamanta a Iran from London bata da lafiya tafiyan da bata dawo na kenan sukayi hatsari shekara biyu kenan and since then i remain single".
Ita da kanta ta yarda akwai mutanen da kirkinsu yake sakawa dole kayi mu'amala dasu kamar Ahmad, ta kwatanta a ranta ace shi ya mutu, irin yanda taji yasa tayi saurin kawar da tunanin daga raita
Washe gari dakyar ta iya tashi baccin da bata samu isashshe ba, sun daÉ—e suna magana da Jay a waya sannan data kwanta ta kasa bacci tayita bitar hirar da sukayi. Shida da rabi ta idar da sallah tana Azkar ya sake kiranta ta É—aga fuskarta da murmushin da batasan ma tanayi ba suka gaisa.
"Zan fita ne nace bari na fara kiran Baby na naji ya ta tashi, or you are still in bed?" Ya faɗa salonsa dake kassarata. A shagwaɓe tace
"Aa na tashi nayi sallah Azkar nakeyi yanzu".
"Kinyi mana addu'a ko?" Ya tambayeta ta É—aga kai kamar tana gabansa se ya sake cewa
"Zan fita Training ki kula da kanki i will call you when I'm back ok?"
"Allah ya kaimu" ta bashi amsa a sanyaye dan se taji bata so ya ajiye wayar. Be sake magana ba ya kashe tana ajiyeta kiran Ahmad ya shigo seda ta harari wayar kafin ta ansa.
AHMAD
Yana zaune a gefen gadonsa, shigowarsa kenan daga masallaci tun Asuba kwana yayi da tunaninta, tunda ya farka da Asubar yaso ya kirata amma ya daure ya bari gari yayi haske.
"Fatima, meya samu wayarki jiya taƙi shiga na kira yafi sau goma?" Ya faɗa bayan data ɗaga wayar. Muryarta a kumbure kamar me bacci alhalin haushine ya cikata tace
"Bacci nayi da wuri, kuma ban sani ba ta shiga DND se yanzun dana tashi na cire".
"Haba nayi mamaki duk hankali na kuma ya tashi amma yanzu na samu nutsuwa tunda lafiya kike, ya school É—in toh?" Ya faÉ—a har yana sauke ajiyar zuciya se kuma tausayinsa ya kamata wato So Jarabtace wanda Allah ya dorawa kaÉ—ai yasan wahalarsa gashi itama idan batayi da gaske ba tana neman afkawa komar wanda ze wahalar da ita.
Ta miƙe tana ninke sallaya tace masa
"Lafiya lau nake, ya hanya? Kun koma Kano ko can kuka kwana?"
"A cikin Kano mukayi sallar Magriba ma" ya bata amsa ta haye gadonta tana cewa
"Masha Allah kunyi sauri gaskiya toh sannunka"
"Yawwa kema sannunki" daga nan suka É—anyi shiru se ya sake cewa
"Bari na barki zaki koma bacci ko yau weekend nima cikin gidan zan shiga na gaida Momy se na dawo na kwanta an jima idan Allah ya kaimu zanje gurin Baffa kina da saƙo ne?"
"Aa, babu" ta bashi amsa se yace
"Toh shikenan ki kwanta we talk later"
"Bye" daga haka ta kashe wayar taja bargo dan bacci be isheta ba Badar ta fincike tana cewa
"Gidan uwar wa kika tafi jiya har sha biyu wayarki kuma bata shiga?"
"Not this early Badar bacci nakeji" Afeeyah ta faɗa tana sake jan bargon da taga zata takurata ta sakar mata ta janyo Hijabin data cire ta ƙudunduna duk kuma tsiyar Badar bata kula taba dan ita idan taso bacci babu abinda yake hanatayi dan mutum yaga dama ya dakko police band ya kaɗa baccinta zatayi sanin haka itama yasa ta barnta ta koma nata gadon tana cigaba da mita kafin tayi shiru tayi bacci. Se bayan Azahar da tayi wanka tana shiryawa ta lura da aika aikar da sauro yayi mata zaman da tayi a waje jiya jikinta yayi Jaa duk inda ya ciza ya tashi, Maman Minal tace
"Yauma cikin flowers kika je yin waya ko? Waini Afeeya wa kika samu da ba zakiyi magana dashi a É—akin nan ba se kinje cikin sauro?"
"Bari na dawo ke kaɗai zan bawa labari Anty Zahra tunda mutane yanzu kowa boye sirrinsa yake" ta faɗa tana hararar Badar ta gefen ido, ta aje turaren hannunta da take fesawa ta kwaɓe
fuska tace
"Nasan idan kuka sani sena tsani kaina saboda tsokanarku duk na gama cika baki wlh So be kyauta mun ba wlh".
Suna class Jay ya kirata lokacin wayar na hannun Badar ta shiga Ig tana duba styles na É—inkin da zasuyi da bikin Anty Yusra.
Ta miƙa mata wayar ta ɗaga ƙasa ƙasa tace masa
"I'm in class zan kiraka in mun fita" ta kashe.
"Waye kuma Jay kika samu?" Badar ta tambayeta bayan ta maida mata wayar, tayi fari da ido nace
"New catch, a big fish"
"Yaushe kika zama Money monger Afee?" Ta faÉ—a tana kallonta, Afeeyah ta zare ido tace
"Daga cewa Big Fish? To na janye ni ba abinda nake nufi kenan ba matsayinsa nake kwatanta miki, Professional footballer ne a Arsenal yake wasa ma"
Seta kalleta da sauri tace
"You mean JAY? No you must be kidding, Afeeyaj a ina ma ze ganki yana UK kina Nigeria? bama wannan ba JAY fa Afee, yes i know you are Beautiful, kin kai a soki but JAY noooo. A yanda nake jin labarinsa he can't date Nigerian girl Hausa for that matter. Shifa ko yammatan da ake ganinsa dasu se kin kallesu kin sake, irin models din nan ne da zakiga kamar su suka yi kansu sedai idan wani ne yake so ya yaudareki da sunansa dan ko a IG kika duba accounts masu sunansa sunfi dubu ma".
Kasaƙe tayi tana kallonta, koda ba laifinta bane gaskiya duk wanda tacewa JAY dai na Arsenal take waya dashi kallon batasan me take cewa ba zeyi mata amma dukda haka se tace mata
"Toh Badar ina shi Bahaushene me yasa za'ayi mamaki idan yaso Bahaushiya kuma lower class irina?"
"Yes Bahaushene Dan Kano nema aka ce amma abinda nake so ki duba shifa babban Celebrity ne, koda yake ke ba sabgar Ball kika sani ba amma da keda kanki idan aka ce miki shine sekin ƙaryata. Kamar fa kice min Messi ya kiraki ne ko Ronaldo".
Maganar Badar ɗin ta sakata tunani domin abinda ta faɗi yakan iya zama gaskiya tunda dai ita ba sanin wancan Jay na gaskiya tayi ba haka kuma wannan sau ɗaya ta ganshi sedai tabbas akwai kamanceceniya a tsakaninsu to amma menene ribarsa idan yayi mata ƙarya da sunan wanda ba shine ba?
"Dubo mun picture É—insa na gani indai shine zan gane" ta faÉ—awa Badar, seta kalleta kafin tayi dariya da alama cewar da tayi idan ta ganshi zata gane ne ya saka Badar dariyar.i
"Ashe kun haÉ—u face to face ma? ko hoto ya turo miki?" Tayi mata tambayar da sigar rainin hankaki ita kuma Innocently tace mata
"A school É—in nan fa muka haÉ—u Badar ranar Monday da ace kina nan kema da kin ganshi na fito zan tafi class da safe ya tareni kuma shine wanda Sahid yace ya bawa number ranar da muna tare dake".
Data fara dariya har seda hankalin Lecturer ya dawo kansu duk aka juya ana kallonsu babu ɓata lokaci kuwa ya korasu waje kuma har sannan ba wai ta bar dariyar bane guri ma ta samu ta zauna tana ci gaba da abarta dan harga Allah abin na Afeeyah mugun bata dariya yayi, Jay Afeeyah zatace ta gani a cikin ABU Zaria? Jay ne ze shigo Zaria ba tareda garin ya girgiza ba? Da ace Afeeyah na kallon Ball ko ta taɓa nuna ra'ayi akan Jay Footballer da se tace tsabar yanda ta kwallafa rai akansa ne har yasa ya fara mata gizo amma yanzu ta tabbatar wani ne yake so yayi mata wasa da hankali amma ya akayi har Afeeyah tayi falling wa cheap trick kamar wannan da sauri haka?
"Bana son iskanci Badar me kika daukeni ne?" Afeeyah ta faÉ—a a fusace se Badar ta nuna ta tace
"Da alama zaman da kikayi a waje kwana biyu kinyi gamo dan wannan maganar da kike batayi kama data me cikakken hankali ba". Ran Afeeyah ya ɓaci ta hayayyaƙo mata tace
"Wato kin gama akan Ahmad yanzu kuma kin samu sabo ko? Wani Badar me kika É—aukeni ne? Alfarma maza sukeyi mun su soni ko kuwa ban kai macen da za'a ce ana so ba?".
Kafin ta bata amsa Sahid ya kwaso da gudu kamar wani ƙaramin yaro har yana ture waɗanda suke fitowa daga class ɗin alamar an gama lecture ya tsaya a gabansu yana haki yace
"Afeeya i have been looking for you all round the school, na yesterday i remember where i know that Guy's face from, he is JAY Afeeya the great JAY of Gunners was in front of me but i couldn't recognised him God i was so stupid, definetly my village people are behind this misfortune but still I'm lucky and I'm happy that i gave him your number i hope he called? If yes please Afeeya do me this favour of introducing me to him as his ride or die fan wallahi....."
"Sahid haba mana ya isa" ta dakatar gashi ganin maganar bata da alamar ƙarewa s zuba yake kamar wanda kanda ya ƙone, a fusace ta sake maida kallonta kan Badar dan ta ƙarasa zazzaga mata abinda ke ranta rungunar da tayi mata tareda fasa ihu kamar zata toshe mata kunne bata ko damu da a waje suke ba ta shiga tsalle tama kasa magana kamar wata wawiya se ihu takeyi.
"Oh saboda nayi kama da Ex Girlfriend É—inka yasa ka kulani kenan?"
"Ko ɗaya, sanda nake tare da ita ma she was the one pushing the relationship and i supported her just because she was nice, Zoya was the most beautiful soul i have ever met in my life tana da kirki na ƙarshe ta so ni she really wanted to marry me kuma ko ni i lokacin idan da zanyi aure it will be her but unfortunately she lost her life in a plane crash ta tafi ganin Mamanta a Iran from London bata da lafiya tafiyan da bata dawo na kenan sukayi hatsari shekara biyu kenan and since then i remain single".
Ita da kanta ta yarda akwai mutanen da kirkinsu yake sakawa dole kayi mu'amala dasu kamar Ahmad, ta kwatanta a ranta ace shi ya mutu, irin yanda taji yasa tayi saurin kawar da tunanin daga raita
Washe gari dakyar ta iya tashi baccin da bata samu isashshe ba, sun daÉ—e suna magana da Jay a waya sannan data kwanta ta kasa bacci tayita bitar hirar da sukayi. Shida da rabi ta idar da sallah tana Azkar ya sake kiranta ta É—aga fuskarta da murmushin da batasan ma tanayi ba suka gaisa.
"Zan fita ne nace bari na fara kiran Baby na naji ya ta tashi, or you are still in bed?" Ya faɗa salonsa dake kassarata. A shagwaɓe tace
"Aa na tashi nayi sallah Azkar nakeyi yanzu".
"Kinyi mana addu'a ko?" Ya tambayeta ta É—aga kai kamar tana gabansa se ya sake cewa
"Zan fita Training ki kula da kanki i will call you when I'm back ok?"
"Allah ya kaimu" ta bashi amsa a sanyaye dan se taji bata so ya ajiye wayar. Be sake magana ba ya kashe tana ajiyeta kiran Ahmad ya shigo seda ta harari wayar kafin ta ansa.
AHMAD
Yana zaune a gefen gadonsa, shigowarsa kenan daga masallaci tun Asuba kwana yayi da tunaninta, tunda ya farka da Asubar yaso ya kirata amma ya daure ya bari gari yayi haske.
"Fatima, meya samu wayarki jiya taƙi shiga na kira yafi sau goma?" Ya faɗa bayan data ɗaga wayar. Muryarta a kumbure kamar me bacci alhalin haushine ya cikata tace
"Bacci nayi da wuri, kuma ban sani ba ta shiga DND se yanzun dana tashi na cire".
"Haba nayi mamaki duk hankali na kuma ya tashi amma yanzu na samu nutsuwa tunda lafiya kike, ya school É—in toh?" Ya faÉ—a har yana sauke ajiyar zuciya se kuma tausayinsa ya kamata wato So Jarabtace wanda Allah ya dorawa kaÉ—ai yasan wahalarsa gashi itama idan batayi da gaske ba tana neman afkawa komar wanda ze wahalar da ita.
Ta miƙe tana ninke sallaya tace masa
"Lafiya lau nake, ya hanya? Kun koma Kano ko can kuka kwana?"
"A cikin Kano mukayi sallar Magriba ma" ya bata amsa ta haye gadonta tana cewa
"Masha Allah kunyi sauri gaskiya toh sannunka"
"Yawwa kema sannunki" daga nan suka É—anyi shiru se ya sake cewa
"Bari na barki zaki koma bacci ko yau weekend nima cikin gidan zan shiga na gaida Momy se na dawo na kwanta an jima idan Allah ya kaimu zanje gurin Baffa kina da saƙo ne?"
"Aa, babu" ta bashi amsa se yace
"Toh shikenan ki kwanta we talk later"
"Bye" daga haka ta kashe wayar taja bargo dan bacci be isheta ba Badar ta fincike tana cewa
"Gidan uwar wa kika tafi jiya har sha biyu wayarki kuma bata shiga?"
"Not this early Badar bacci nakeji" Afeeyah ta faɗa tana sake jan bargon da taga zata takurata ta sakar mata ta janyo Hijabin data cire ta ƙudunduna duk kuma tsiyar Badar bata kula taba dan ita idan taso bacci babu abinda yake hanatayi dan mutum yaga dama ya dakko police band ya kaɗa baccinta zatayi sanin haka itama yasa ta barnta ta koma nata gadon tana cigaba da mita kafin tayi shiru tayi bacci. Se bayan Azahar da tayi wanka tana shiryawa ta lura da aika aikar da sauro yayi mata zaman da tayi a waje jiya jikinta yayi Jaa duk inda ya ciza ya tashi, Maman Minal tace
"Yauma cikin flowers kika je yin waya ko? Waini Afeeya wa kika samu da ba zakiyi magana dashi a É—akin nan ba se kinje cikin sauro?"
"Bari na dawo ke kaɗai zan bawa labari Anty Zahra tunda mutane yanzu kowa boye sirrinsa yake" ta faɗa tana hararar Badar ta gefen ido, ta aje turaren hannunta da take fesawa ta kwaɓe
fuska tace
"Nasan idan kuka sani sena tsani kaina saboda tsokanarku duk na gama cika baki wlh So be kyauta mun ba wlh".
Suna class Jay ya kirata lokacin wayar na hannun Badar ta shiga Ig tana duba styles na É—inkin da zasuyi da bikin Anty Yusra.
Ta miƙa mata wayar ta ɗaga ƙasa ƙasa tace masa
"I'm in class zan kiraka in mun fita" ta kashe.
"Waye kuma Jay kika samu?" Badar ta tambayeta bayan ta maida mata wayar, tayi fari da ido nace
"New catch, a big fish"
"Yaushe kika zama Money monger Afee?" Ta faÉ—a tana kallonta, Afeeyah ta zare ido tace
"Daga cewa Big Fish? To na janye ni ba abinda nake nufi kenan ba matsayinsa nake kwatanta miki, Professional footballer ne a Arsenal yake wasa ma"
Seta kalleta da sauri tace
"You mean JAY? No you must be kidding, Afeeyaj a ina ma ze ganki yana UK kina Nigeria? bama wannan ba JAY fa Afee, yes i know you are Beautiful, kin kai a soki but JAY noooo. A yanda nake jin labarinsa he can't date Nigerian girl Hausa for that matter. Shifa ko yammatan da ake ganinsa dasu se kin kallesu kin sake, irin models din nan ne da zakiga kamar su suka yi kansu sedai idan wani ne yake so ya yaudareki da sunansa dan ko a IG kika duba accounts masu sunansa sunfi dubu ma".
Kasaƙe tayi tana kallonta, koda ba laifinta bane gaskiya duk wanda tacewa JAY dai na Arsenal take waya dashi kallon batasan me take cewa ba zeyi mata amma dukda haka se tace mata
"Toh Badar ina shi Bahaushene me yasa za'ayi mamaki idan yaso Bahaushiya kuma lower class irina?"
"Yes Bahaushene Dan Kano nema aka ce amma abinda nake so ki duba shifa babban Celebrity ne, koda yake ke ba sabgar Ball kika sani ba amma da keda kanki idan aka ce miki shine sekin ƙaryata. Kamar fa kice min Messi ya kiraki ne ko Ronaldo".
Maganar Badar ɗin ta sakata tunani domin abinda ta faɗi yakan iya zama gaskiya tunda dai ita ba sanin wancan Jay na gaskiya tayi ba haka kuma wannan sau ɗaya ta ganshi sedai tabbas akwai kamanceceniya a tsakaninsu to amma menene ribarsa idan yayi mata ƙarya da sunan wanda ba shine ba?
"Dubo mun picture É—insa na gani indai shine zan gane" ta faÉ—awa Badar, seta kalleta kafin tayi dariya da alama cewar da tayi idan ta ganshi zata gane ne ya saka Badar dariyar.i
"Ashe kun haÉ—u face to face ma? ko hoto ya turo miki?" Tayi mata tambayar da sigar rainin hankaki ita kuma Innocently tace mata
"A school É—in nan fa muka haÉ—u Badar ranar Monday da ace kina nan kema da kin ganshi na fito zan tafi class da safe ya tareni kuma shine wanda Sahid yace ya bawa number ranar da muna tare dake".
Data fara dariya har seda hankalin Lecturer ya dawo kansu duk aka juya ana kallonsu babu ɓata lokaci kuwa ya korasu waje kuma har sannan ba wai ta bar dariyar bane guri ma ta samu ta zauna tana ci gaba da abarta dan harga Allah abin na Afeeyah mugun bata dariya yayi, Jay Afeeyah zatace ta gani a cikin ABU Zaria? Jay ne ze shigo Zaria ba tareda garin ya girgiza ba? Da ace Afeeyah na kallon Ball ko ta taɓa nuna ra'ayi akan Jay Footballer da se tace tsabar yanda ta kwallafa rai akansa ne har yasa ya fara mata gizo amma yanzu ta tabbatar wani ne yake so yayi mata wasa da hankali amma ya akayi har Afeeyah tayi falling wa cheap trick kamar wannan da sauri haka?
"Bana son iskanci Badar me kika daukeni ne?" Afeeyah ta faÉ—a a fusace se Badar ta nuna ta tace
"Da alama zaman da kikayi a waje kwana biyu kinyi gamo dan wannan maganar da kike batayi kama data me cikakken hankali ba". Ran Afeeyah ya ɓaci ta hayayyaƙo mata tace
"Wato kin gama akan Ahmad yanzu kuma kin samu sabo ko? Wani Badar me kika É—aukeni ne? Alfarma maza sukeyi mun su soni ko kuwa ban kai macen da za'a ce ana so ba?".
Kafin ta bata amsa Sahid ya kwaso da gudu kamar wani ƙaramin yaro har yana ture waɗanda suke fitowa daga class ɗin alamar an gama lecture ya tsaya a gabansu yana haki yace
"Afeeya i have been looking for you all round the school, na yesterday i remember where i know that Guy's face from, he is JAY Afeeya the great JAY of Gunners was in front of me but i couldn't recognised him God i was so stupid, definetly my village people are behind this misfortune but still I'm lucky and I'm happy that i gave him your number i hope he called? If yes please Afeeya do me this favour of introducing me to him as his ride or die fan wallahi....."
"Sahid haba mana ya isa" ta dakatar gashi ganin maganar bata da alamar ƙarewa s zuba yake kamar wanda kanda ya ƙone, a fusace ta sake maida kallonta kan Badar dan ta ƙarasa zazzaga mata abinda ke ranta rungunar da tayi mata tareda fasa ihu kamar zata toshe mata kunne bata ko damu da a waje suke ba ta shiga tsalle tama kasa magana kamar wata wawiya se ihu takeyi.