← Book details Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 68 OF 71

Sashe 68

Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Bayan ya gama abinda yakeyi ya hau gado ya kunna Wifi ya shiga WhatsApp, status É—insa yayi updating da 'found a new love'. Badan yayi blocking Afeeyah ba tun a ranar zata gani, Ahmad ne ya fara buÉ—ewa ya masa replay da
"Who is the new catch"
"Some one that i deserve, and she deserves me" ya maida masa. Se Ahmad ya kirashi ta WhatsApp ɗin dan tunda ya tafi kamar yanda sukayi zato ta nan suke magana yaƙi kunna wayarsa.

"Jay dagaske kake ka haƙura da yarinyar nan wai?"
"Dagaske mana Yah Ahmad kasan dai sau É—aya nake so kuma if i hate something and turned my back against it i never go back to it" ya bashi amsa. Ahmad yayi murmushi yace

"Amma ko, da zan baka shawara da nace kayi haƙuri indai abinda ze iya gyaruwa ne tsakaninku ka gyara saboda i can tell you truly love that girl Afeeyah dan ban taɓa ganinka a irin yanayin da soyayyarta ta sakaka ba, kaga koda kake ganin kamar bani da zuciya akan Fatima ba haka bane ba, Ina sonta ne jikina da zuciyata ba zasu taɓa samun nutsuwa da wata mace ba bayan ita shiyasa nake jure komai saboda na sameta"

"Yanzu a baka zaɓi ni ko ita wanne zakayi choosing?" Jay ya tambayeshi, yayi murmushi yace
"Kai jinina ne ita kuma rayuwata ce"
"Ita zaka zaɓa kenan?" Jay ya sake tambaya Ahmad yace
"Aa, rayuwa ba zatayuwu ba seda jini yana kwaranya a jikin mutum kaga kenan ku É—in dafe kuke da rayuwata, rasa É—aya daga cikinku tamkar rasa nine"

"Yanzu kenan ba zaka iya sadaukar mun da soyayyarta ba idan na buƙata?" Jay ya sakeyi masa tambayar da se bayan ta fito yayi nadamar yinta. Ahmad yayi shiru har ya fara zaton ko wayar ta katsene kafin kuma yaji yace
"Zan kwanta cikin salama bayan na mutu idan har ka kasance kaine zaka maye gurbina ka tarairayi iyalina, amma fa dukda haka nasan se nayi kishi, amma karka sake faÉ—ar haka Alhalin ina raye amma da gaske kakeyi ko wasa wannan maganar?" Ahmad ya tambayeshi. Kamar wanda ake ingizawa Jay ya sake cewa

"Idan da gaske nakeyi zaka iya barmun ita?"
"Ta yaya wannan zazzafar Ƙiyayyar zata rikiɗa ta koma soyayya har ta samar da kyakykyawan yanayi na kwanciyar hankali a zaman aure? Kaifa kace ka tsaneta kamar mutuwarka" Ahmad ya sake bauɗewa daga daga barin bashi amsar abinda ya buƙata, cikin yanayi kamar na ƙufula Jay yace

"Toh ai baka amsa mun tawa tambayarba" se Ahmad ya saki sanyayyan murmushi yace
"Babu abinda bazan iya sadaukar maka ba Ƙanina amma ina son Fatima sedai son da nakeyi mata be kai wanda nake maka ba dan haka indai ita ce burinka zan bar maka ita". Da saurin gaske Jay yace

"Wasa nakeyi, kawai so nakeyi na gwada tsakanin nida ita wa kafi so amma Allah ya kiyaye me zanyi da wannan yarinyar? Ya za'ayi ma naso abinda kake so? Ai ko ina sonta na gane tilas na haƙura bazan taɓa takarar wani abu a rayuwar duniya da kai ba ko menene koda rayuwata zata salwanta a dalilinsa zan haƙura na bar maka shi".

Sukayi shiru na wani lokaci, a zuciyar Ahmad lissafi yake dalilin daya kawo Jay ya soko wannan maganar? Zancen Afeeyarsa sukeyi me yasa ze kawo maganar ya bar masa Fatima kuma? Shi ya kasa tattara abubuwan ma ya gane me suke nufi. Jay kuwa sake auna nauyin soyayyar da Ahmad yakeyiwa Fatiman yake a zuciyarsa, idan har ya zama silar rabashi da ita beyi masa Adalci ba amma be cancanci Azzalumar mace irinta ba mara tsoron Allah muguwa, Allah kaÉ—ai yasan dalilin wannan haÉ—i.

"Yau na haÉ—u da matata" Jay ya katse musu shirun, Ahmad yace
"Uhm, da wurwuri haka?"
"Dama ya kamata ace ita ce, rabon na sja wahala ne yasa na barta kuma yanzu Allah ya sake dawomun da ita cikin rayuwata bazan bari kuma ta kufcemun ba"
"Ikon Allah, ita kuma wacece ita?"
"Fatiyyah Mu'az" ya bashi amsa, Ahmad ya maimaita sunan da alama so take ya tuna koya santa can kuwa yace

"Fatiyyah Fatiyyah dai? Daman kuna tare har yanzu? I thought ma tayi aure itama kamar Maryam?"

"Nop batayi ba, we met not so long ago"
"Ayyah tana France kenan?" Ahmad ya tambayeshi, se yayi jumm daya tuna ashe ya kusa ya kwafsa kafin yace
"Eh, Aa, a Abuja muka haÉ—u kafin na wuce ai ta koma Nigeria ta gama karatunta"
"Allah ya tabbatar da Alkhairi" inji Ahmad da sam be gane kan Jay ba.

Washe gari yaje gidansu Fatiyyah kamar yanda yayi mata Alƙawari, Mamanta, Babanta da duka siblings nata sun sanshi sun kuma saba tun a lokacin da suke tare dan haka da yaje normal suka gaisa sukayi hira da Mamanta kafin ta basu guri. Sister ta ce ta ɗaukesu video a wayarsa da Fatiyyan ta karɓa ta bata sanda suka fito rakashi. Fatiyyan da kanta ta shiga tiktok tayi uploading video da Caption ɗin ~FATIYYAHJAY~, shi bema san dashi ba se bayan daya koma Hotel ya kunna router yaga messages ɗin friends ɗinsa da suka sanshi da Fatiyyan a da, kowa tambayar da yake masa "sun dawo tare ne?" Wasu suce they will make a perfect couple. Daman be bi takan comments na tiktok ɗin ba shiyasa ma bega saƙon Afeeyah ba dan normally idan yayi posting turning off comments yakeyi saboda bashida lokacin dubawa, washe gari ya koma France yayi resuming field har sannan kuma zuciyarsa ba'a sake take ba.

Mixed feeling yake dashi akan Afeeyah, Soyayyar da yake mata na neman ta hana tsanarta daya fara tun usuli cigaba dayin tasiri a ransa. Sabon babin da suka buɗe na Ƙauna da Fayiyyah ne yake ɗebe masa kewa. Fatiyyah na sonsa, so na gaske, a gefensa zece yana sonta amam ko rabin yanda yakejin Afeeyah har a yanzu cikin zuciyarsa bata kamo ba amma kuma yana jin a ransa ze iya auranta yanzu musamman da yake neman ruwan kashe gobara shiyasa yake iyakar ƙoƙari gurin ganin ya maida mata da kwatankwacin soyayyar da take gwada masa. Abu guda da yake haɗa shi da Fatiyyah rawar kanta kuma tun asali abinda yayiwa tarayyarsu tasgaɗo kenan yar gata ce da bata san komai ba se a tattalata a jiyar da ita daɗi, irin soyayyar da sukayi da Afeeyah wadda da acw a baya ne ko wani ya gani yana kalarta cewa zeyi baƙauye ne a yanzu ita yake muradi a gurin Fatiyyan sedau wayewarta tayi yawa nata salon soyayyar na manyan yara ne masu buɗaɗɗun ido irin wadda take burgeshi a da kenan yanzu kuma soyayya me tafe da sirkin kunya data ɗanɗana a baya ita yake muradin sake samu amma Yah Ahmad ya yi masa tsakani da ita.

A ta gefen gidan Alhaji Audun Bechi kuwa rayuwa ce take ta gurgurawa yau fari gobe baƙi, Malam Hafizu ya cika maganarsa kamar yanda yace a bashi sati huɗu shida kansa ya kira Baba Alƙali ya shaida amsa ya shirya suna iya zuwa sannan. Da Alƙalin ya gayawa Alhaji Audu se cewa yayi ba za'aje ba, wai yar ta gwal ce da har se ya bawa mutane lokaci sanda yaga dama sannan za'aje neman auranta?

"Kota zubardaji ce ba Gwal ba wannan ba matsalarka vace ba, ma'aurin yace yaji ya gani seka kawo idanu ka zuba yanda ka sabayi a lamarin auran sauran yarorinka, karka cusa bakinka ciki muddin ba Alkhairi zaka saka musu ba" Alƙali ya dakatar dashi. Alhaji Audu yace
"Nifa kawai auran yarinyar be kwantamun a zuciya ba, tunda yana jin maganarka ka bashi baki ya nemi wata ga yayan manyan mutane nan yan Asali ko yaushe ne seda Alhaji Madari yamun maganar yarsa yace ko shi ko Jafaru..."
"Ai kasan shi Jafaru uwarsa ma ta isheka shiyasa ba zaka somo dashi ba wannan kuma daya zama karkatacciyar kukar kowa me daɗin hawa dole ka nemi hanashi abinda yake so. Ni daman na daɗe da sanin bawai Binta ce kaɗai shaiɗaniya ba, hali ne ya tarar da hali kaida itan shiyasa zamanku yayi tsayi.. To ni duk ba wannan ba, zancen muhalli a ina zauna?" Cewar Baba Alƙali.

Alhajin Bechi ya karkace yace
"Yanzu Ahmad kake tambayar i

FATIMA
Kafin cikar wa'adin da Baffah ya yanka ta tattara ta koma makaranta kowa ya ganta seya tambayi me yake damunta se tace musu rashin lafiya tayi saboda yanda ta fita a hayyacinta kana ganinta kasan bata da nutsuwa sam. A bakin Anty Sauda taji cewar Baffah ya kira Kawun Ahmad kamar yanda ya roƙi su bashi sati huɗu lokaci ya cika kuma ya gama uzurin da yake a gabansa yanzu dan haka duk sanda suka shirya suna iya suje.
Chapter 68 · 0% Book details