Sashe 48
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hajiya ta harari Alhaji Babangida, koda ta girme shi amma shakkarsa takeyi ta san ko shi Alhajin yana bashi darajar kasancewarsa Ɗa na fari a gidan, maganar Hassan ce tasa tayi kasaƙe tana kallonsa. Naziru ya zaburo masa yana cewa
"Ka kira sunana kai tsaye ka dena wani kwane kwane, kuma na auri yar Tiktok É—in koda abinda zakayi akai?"
"Yi shiru da bakinka Naziru barni dashi" Hajiya ta gyara zamanta taci gaba da cewa
"Yanzu kai Hassan tsabar baka da kunya ana maganar matar aure me Asali da tushe daga babban gida har ka saka baki? Koda yake kana da hujjar bin bayan Al'amarin, tunda uwarku ta auru a matsayinta na Tubabbiyar Karuwa ai dole kace wannan ma ba......"
Tsawar da Hussaini ya daka mata me kama da saukar Aradu ta saka sauran maganganun bakinta maƙalewa. Cikin yanayin da yake nuna ƙololuwar ɓacin ransa dan hatta da jijiyoyin kansa daya sha askin Skin sun fito ruɗu ruɗu haka idonsa ya rikiɗa yayi jajir ya nuna ta yana cewa
"Akul Binta, duk abinda kike ji dashi ya tsaya kan waÉ—anda kika raina karki yi kuskuren sako mahaifiyarmu a shirginki domin yanzu ba da bace idan kuma ba haka ba...."
"Idan ba haka ba me zakayi?" Alhaji Zakariyya ya diro gabansa kamar wanda aka harbo da kwari da baka yana huci, Hajiya da tsoron Hussainin ya cikata jikinta har ɓari yake ta ja hannunsa Zakariyyah tana cewa
"Barshi Ubana kasan É—an hau ne"
"Ki ƙyaleni Hajiya ku kuke nuna kuna tsoronsa a gidan nan idan zafin kai da ƙwaya yake ji dasu shi ƙaramin ƙwarone kansa baze ɗauki ko rabin chajin da nakeyi ba an faɗa ance Yayan Tubabbiyar Karuwa kayi abinda zak...."
Marin da Hussanin ya ɗaukeshi da shi irin me jirkita ƙwaƙwalwar nan ya sakashi wuntsilawa gefe dafe da fuska yana raba idon, Hajiya Binta ta fasa ihu tayi kansa ganin yanda yake zare ido kamar tunaninsa ya kauce, a fusace shi kuma Naziru ya cakumi kwalar Hussanin ya kai masa naushi a fuska yana cewa
"Wlh baka mari banza ba sena rama masa" kafin kace me dambe ya sarƙe a tsakaninsu kowanne ya shiga kaiwa ɗan uwansa mugun hari da yake jikinsu iri ɗaya ne, dukkaninsu sangangan suke irin jikin Audu Bechi wannan ya ƙarawa Damben nasu armashi dan kowa ya gagara kai ɗan uwansa ƙasa amma dai Hussainin yafi kai hari a zuciye.
Ahmad, Momy da Dr Hassan ne suka shiga ƙoƙarin raba su sauran jama'ar falon kuwa seka rantse a Tv suke kallon wannan Al'amari babu wanda ma ya motsa balle ya kai agaji sema tattare ƙafafunsu da sukayi dan kar a faɗo musu. Hajiya na gefen Alhaji Zakariyyah dake kururuwa kamar mace sakamakon yanda Marin ya shammaceshi ya shige shi dagaske ga haƙorinsa ɗaya daya turguɗe a ƙasa, ihu Hajiyar take itama tana Zagin Hussaini, jafa'in duniya babu wanda bata janyo masa ba dashi da Hassan ɗinsa harda uwarsu dake can gida bata san wainar da ake toyawa ba ta karɓi rabonta se abi da Hajiyar ta manta ne bata ambata ba.
Momy ta kalli Alhaji Audu dake zaune akan kujera tamkar gunki cikin kuka tace
"Kana kallo Alhaji, jira kake se ɗaya ya kashe ɗaya kafin ka tsawatar musu? Wannan shine daidaiton da kake fatan samuwarsa cikin zuri'arka? Anya kuwa Alhaji ka shiryi tarar da ubangijinka cikin salama kamar yanda kowanne musulmi yake fata?" Tana gama faɗar haka cikin kuka ta fice daga falon, a bakin ƙofa taci karo da yayansu Mata a tsaitsaye cikin tashin hankali. Hajiya ƙarama datafi kusa da ita tacewa
"Kira Babanku Alƙali ki gaya masa yazo babu lafiya a gidan nan" ta shige cikin gida tabar Hajiya ƙarama na ƙoƙarin kiran Baba Alƙali amma sau biyu wayar na suɓuce mata saboda yanda jikinta yake rawa daƙyar ta iya danna kiran.
Momy kuwa harta isa ɗakinta hawaye be tsaya mata ba, ba kuma tasan ranar da zata dena zubar dasu ba hawayen baƙin ciki, takaici da dana sanin auran wannan mutumin da sam bata san me zata kirashi ba. Son zuciyane ko kuwa tsabar ƙin Allah ya saka Alhajin yin abubuwan da yakeyi bata sani ba amma koma menene ta tabbata muddin be tuba ya gyara alaƙarsa da Ahalinsa ba ya mutu a haka tabbas baze kwanta cikin salama a Kabarinsa ba.
A can falon kuwa Hussaini ya mazge Hassan ɗinsa daya cukumi cikinsa yana ƙoƙarin janyeshi kafin ya kaiwa Ahmad ƙafa amma ya goce ba shiri suka matsa daga rabon damben suka barsu zuwa sannan Hussainin keda nasara dan ya kai Naziru ƙasa ya masa lilis har ya kai baya iya maida martani se Ƙoƙarin kare kansa kawai yake amma Hussaini be haƙura ba yaci gaba da jibgarsa kamar Allah ya aiko shi. Dama ce irin wadda ya daɗe yana fatan samu da ze huce kaɗan daga irin takaicin da Hajiya Binta da Yayanta suka ƙunsa musu a rayuwa. Lokacin yarinta tsoron hukuncin da Alhaji zeyi musu da izayar da zasu sha a hannun Hajiyar tasa yake haƙura idan zuciyarsa ta raya masa daya jibgi yayanta in suka musu abu, yasha ya kwatanta ya dake sun in yaso ya gudu ya bar gidan amma yasan Hassanbaze yarda ya bishi ba, saboda shi ya shanye duk wani wulaƙanci a gidan yanzu kuwa Allah ya bashi damar da duk wanda yace ze shigarwa Nazirun seya haɗa dashi ya zane.
Seda Hussani gama yayiwa Nazirun casar gero kafin Allah ya bawa Alhaji Audu ikon yunƙurawa daga zaunen da yake tamkar wanda ya tafi hutu wata duniyar na wucin gadi ya dawo haka ya shiga jan numfashi kamar me Asthma. Ahmad yayi kansa yana cewa
"kun gani ko ku bari idan ba kashe shi kuke so kuyi ba".
Hussaini daya gama aikin Allah ya tsugunna ya É—auki Agogon Azurfarsa daya tsinke a garin dambe bayan daya gaji da jibgar Naziru ya kalli Ahmad yace
"Toh ya mutu mana, dama wa rayuwarsa ta dama bare idan ya mutu yayi baƙin ciki? Ƙilan ku da su daya ɗauka Yaya ya fifitasu akan kowa sune zasu shiga uku duk ranar da aka ce babu shi" sannan ya kalli Hajiya Binta da idanunsa da suka koma abin tsoro yace
"Nan gaba idan wani daga cikin marasa kunyar Yayanki yayi niyyar tsoma baki a sabgata ki gargaÉ—eshi, idan ba haka ba zanci gaba da nuna muku abun da ÆŠan Tubabbiyar karuwa ze iya aikatawa" yana gama faÉ—ar haka ya fice daga falon a fusace fuuuu kamar kububuwa.
Maganganun Hussaini sun daki ƙirjin Alhajin kamar shigar bullet, ya yunƙura cikin wani yanayi ya tashi tsaye dan bakinsa kamar an liƙe masa shi da glue yake ji yana tsayuwa akan ƙafafunsa jiri ya kwasheshi ya koma kan kujerar Yaraf kamar wata gingimemiyar giwa ta faɗi. Ahmad da Hassan suka rufu akansa, Hassan ɗin ya kalli Ahmad yace
"Riƙeshi, bari na ɗakko Kit ɗina a mota mu gani idan kuma babu hali mu wuce Asibiti dashi kawai" yana gama faɗar haka ya fice da gudu kamar yaro ya nufi motarsa.
Da wani irin yanayi Alhajin ya ringa kallon Yayansa Maza da suka fara miƙewa da ɗaɗɗaya suna barin falon harda masu sakin ƙananun tsuka dalilin ɓata musu lokaci da akayi da wannan wasan kwaikwayo da suka rigada suka saba dashi babu Wanda ya nuna damuwar cewa wai Mahaifinsa ne a wani yanayi da ko ba'a faɗa ba sunsan Hawan Jininsa ne ya tashi Allah ma ya taƙaita ba Paralysis ya samu ba irin wannan komawa da yayi ya faɗi akan kujera, wani abu ya tokarewa Alhaji Audu maƙoshi, hawaye ya ziraro a idanunsa abinda ya sake rikita Ahmad kenan a shekarunsa Talatin a Duniya sau ɗaya ya taɓa ganin ƙwalla a idon Mahaifinsa lokacin da aka kawo gawar Brigadier General Baballiya se yanzu kuma hawaye yake dagaske tabbas Al'amarin dake zuciyarsa ba ƙarami bane.
Yanda Dr Hassan ya dawo yaga Alhajin yasa yace kawai su kamashi a tafi Asibiti. Seda ya É—ura Ashar kafin su Salim suka saka hannu aka fita da Alhajin dan Manyan daman tun yana wajen yaga suna ta shigewa motocinsu suna jiran Iyalansu su fito su tafi, da alama Abincin da Hajiya tasa akayi zeyi bandaro dan zama beyi daÉ—in da har za'a jira cin abinci ba.
Hajiya ta ringa ihu kamar wadda ta shiga ƙaramin hauka, Ga Zakariyyah fuska harta suntume saboda haƙorin daya fita ba bisa ƙa'ida ba Naziru kuma na kwance numfashi ne kawai ya banbantashi da matacce Hussaini ya sauke masa duk wata giggiwa da yake fama da ita suma ɗin Dr Hassan ne yasa aka watsa su a mota duk suka rankaya a Asibitinsa. A hanya Ahmad ya kira Baba Alƙali yace masa yana tafe ya kusa isowa gidan Hajiya ƙarama ta kirashi se yace masa ai suna hanyar Asibiti be jira jin ba'asi ba yace ze same su acan domin yasan a runa.
Haka nan rana tsaka Audu ya tattaro irin wannan haɗuwar ba tareda yabi matakan da suka dace ba, zuri'ar da kowanne yake da wani fushi ko miki a zuciyarsa ta yaya zaka ce a lokaci gida zaka sasanta komai ka samu yanda kake so? Ya tabbatar wani abun akayi ko aka faɗa masa da ze saka jininsa ya hau tilas Allah dai ya taƙaita.
Emergency aka karɓi Alhaji Audu su Naziru ma aka watsa su inda ya kamata. Seda akayi stabilizing kowannensu kafin suka samu nutsuwar zuciya. Baba Alƙali ya ringa sababi kamar ya ari baki sanda Dr Hassan ya bashi taƙaitaccen labarin abinda ya faru.
"Ka kira Hussainin ka mai komai dare ya sameni a gida yau wane irin abu ne yake damunsa duk me ubanku ya muku ai baze canza masa suna ba ya za'ayi ya faɗa masa irin wannan maganar? Kai bama shi kaɗai ba gaba ɗayanku ku hallara ina son ganinku tunda naga alamar so kukeyi ku janyo mana abinda ze fi ƙarfin mu".
"
"Nima dai haka na gani Alƙali, ni daga yin abu dan Allah da zuciya ɗaya nace a shirya taron nan ya janyo yayansa a jiki su samu daidaito amma kaga yanda abu ya ƙare dana sani bance ayi ba haka kawai wannan la'anannen yaron ya cutar mun da yaya ya barsu da jinya" Hajiya Binta ta faɗa. Alƙali ya kalleta, cikin tsanin fushi yace
"Ka kira sunana kai tsaye ka dena wani kwane kwane, kuma na auri yar Tiktok É—in koda abinda zakayi akai?"
"Yi shiru da bakinka Naziru barni dashi" Hajiya ta gyara zamanta taci gaba da cewa
"Yanzu kai Hassan tsabar baka da kunya ana maganar matar aure me Asali da tushe daga babban gida har ka saka baki? Koda yake kana da hujjar bin bayan Al'amarin, tunda uwarku ta auru a matsayinta na Tubabbiyar Karuwa ai dole kace wannan ma ba......"
Tsawar da Hussaini ya daka mata me kama da saukar Aradu ta saka sauran maganganun bakinta maƙalewa. Cikin yanayin da yake nuna ƙololuwar ɓacin ransa dan hatta da jijiyoyin kansa daya sha askin Skin sun fito ruɗu ruɗu haka idonsa ya rikiɗa yayi jajir ya nuna ta yana cewa
"Akul Binta, duk abinda kike ji dashi ya tsaya kan waÉ—anda kika raina karki yi kuskuren sako mahaifiyarmu a shirginki domin yanzu ba da bace idan kuma ba haka ba...."
"Idan ba haka ba me zakayi?" Alhaji Zakariyya ya diro gabansa kamar wanda aka harbo da kwari da baka yana huci, Hajiya da tsoron Hussainin ya cikata jikinta har ɓari yake ta ja hannunsa Zakariyyah tana cewa
"Barshi Ubana kasan É—an hau ne"
"Ki ƙyaleni Hajiya ku kuke nuna kuna tsoronsa a gidan nan idan zafin kai da ƙwaya yake ji dasu shi ƙaramin ƙwarone kansa baze ɗauki ko rabin chajin da nakeyi ba an faɗa ance Yayan Tubabbiyar Karuwa kayi abinda zak...."
Marin da Hussanin ya ɗaukeshi da shi irin me jirkita ƙwaƙwalwar nan ya sakashi wuntsilawa gefe dafe da fuska yana raba idon, Hajiya Binta ta fasa ihu tayi kansa ganin yanda yake zare ido kamar tunaninsa ya kauce, a fusace shi kuma Naziru ya cakumi kwalar Hussanin ya kai masa naushi a fuska yana cewa
"Wlh baka mari banza ba sena rama masa" kafin kace me dambe ya sarƙe a tsakaninsu kowanne ya shiga kaiwa ɗan uwansa mugun hari da yake jikinsu iri ɗaya ne, dukkaninsu sangangan suke irin jikin Audu Bechi wannan ya ƙarawa Damben nasu armashi dan kowa ya gagara kai ɗan uwansa ƙasa amma dai Hussainin yafi kai hari a zuciye.
Ahmad, Momy da Dr Hassan ne suka shiga ƙoƙarin raba su sauran jama'ar falon kuwa seka rantse a Tv suke kallon wannan Al'amari babu wanda ma ya motsa balle ya kai agaji sema tattare ƙafafunsu da sukayi dan kar a faɗo musu. Hajiya na gefen Alhaji Zakariyyah dake kururuwa kamar mace sakamakon yanda Marin ya shammaceshi ya shige shi dagaske ga haƙorinsa ɗaya daya turguɗe a ƙasa, ihu Hajiyar take itama tana Zagin Hussaini, jafa'in duniya babu wanda bata janyo masa ba dashi da Hassan ɗinsa harda uwarsu dake can gida bata san wainar da ake toyawa ba ta karɓi rabonta se abi da Hajiyar ta manta ne bata ambata ba.
Momy ta kalli Alhaji Audu dake zaune akan kujera tamkar gunki cikin kuka tace
"Kana kallo Alhaji, jira kake se ɗaya ya kashe ɗaya kafin ka tsawatar musu? Wannan shine daidaiton da kake fatan samuwarsa cikin zuri'arka? Anya kuwa Alhaji ka shiryi tarar da ubangijinka cikin salama kamar yanda kowanne musulmi yake fata?" Tana gama faɗar haka cikin kuka ta fice daga falon, a bakin ƙofa taci karo da yayansu Mata a tsaitsaye cikin tashin hankali. Hajiya ƙarama datafi kusa da ita tacewa
"Kira Babanku Alƙali ki gaya masa yazo babu lafiya a gidan nan" ta shige cikin gida tabar Hajiya ƙarama na ƙoƙarin kiran Baba Alƙali amma sau biyu wayar na suɓuce mata saboda yanda jikinta yake rawa daƙyar ta iya danna kiran.
Momy kuwa harta isa ɗakinta hawaye be tsaya mata ba, ba kuma tasan ranar da zata dena zubar dasu ba hawayen baƙin ciki, takaici da dana sanin auran wannan mutumin da sam bata san me zata kirashi ba. Son zuciyane ko kuwa tsabar ƙin Allah ya saka Alhajin yin abubuwan da yakeyi bata sani ba amma koma menene ta tabbata muddin be tuba ya gyara alaƙarsa da Ahalinsa ba ya mutu a haka tabbas baze kwanta cikin salama a Kabarinsa ba.
A can falon kuwa Hussaini ya mazge Hassan ɗinsa daya cukumi cikinsa yana ƙoƙarin janyeshi kafin ya kaiwa Ahmad ƙafa amma ya goce ba shiri suka matsa daga rabon damben suka barsu zuwa sannan Hussainin keda nasara dan ya kai Naziru ƙasa ya masa lilis har ya kai baya iya maida martani se Ƙoƙarin kare kansa kawai yake amma Hussaini be haƙura ba yaci gaba da jibgarsa kamar Allah ya aiko shi. Dama ce irin wadda ya daɗe yana fatan samu da ze huce kaɗan daga irin takaicin da Hajiya Binta da Yayanta suka ƙunsa musu a rayuwa. Lokacin yarinta tsoron hukuncin da Alhaji zeyi musu da izayar da zasu sha a hannun Hajiyar tasa yake haƙura idan zuciyarsa ta raya masa daya jibgi yayanta in suka musu abu, yasha ya kwatanta ya dake sun in yaso ya gudu ya bar gidan amma yasan Hassanbaze yarda ya bishi ba, saboda shi ya shanye duk wani wulaƙanci a gidan yanzu kuwa Allah ya bashi damar da duk wanda yace ze shigarwa Nazirun seya haɗa dashi ya zane.
Seda Hussani gama yayiwa Nazirun casar gero kafin Allah ya bawa Alhaji Audu ikon yunƙurawa daga zaunen da yake tamkar wanda ya tafi hutu wata duniyar na wucin gadi ya dawo haka ya shiga jan numfashi kamar me Asthma. Ahmad yayi kansa yana cewa
"kun gani ko ku bari idan ba kashe shi kuke so kuyi ba".
Hussaini daya gama aikin Allah ya tsugunna ya É—auki Agogon Azurfarsa daya tsinke a garin dambe bayan daya gaji da jibgar Naziru ya kalli Ahmad yace
"Toh ya mutu mana, dama wa rayuwarsa ta dama bare idan ya mutu yayi baƙin ciki? Ƙilan ku da su daya ɗauka Yaya ya fifitasu akan kowa sune zasu shiga uku duk ranar da aka ce babu shi" sannan ya kalli Hajiya Binta da idanunsa da suka koma abin tsoro yace
"Nan gaba idan wani daga cikin marasa kunyar Yayanki yayi niyyar tsoma baki a sabgata ki gargaÉ—eshi, idan ba haka ba zanci gaba da nuna muku abun da ÆŠan Tubabbiyar karuwa ze iya aikatawa" yana gama faÉ—ar haka ya fice daga falon a fusace fuuuu kamar kububuwa.
Maganganun Hussaini sun daki ƙirjin Alhajin kamar shigar bullet, ya yunƙura cikin wani yanayi ya tashi tsaye dan bakinsa kamar an liƙe masa shi da glue yake ji yana tsayuwa akan ƙafafunsa jiri ya kwasheshi ya koma kan kujerar Yaraf kamar wata gingimemiyar giwa ta faɗi. Ahmad da Hassan suka rufu akansa, Hassan ɗin ya kalli Ahmad yace
"Riƙeshi, bari na ɗakko Kit ɗina a mota mu gani idan kuma babu hali mu wuce Asibiti dashi kawai" yana gama faɗar haka ya fice da gudu kamar yaro ya nufi motarsa.
Da wani irin yanayi Alhajin ya ringa kallon Yayansa Maza da suka fara miƙewa da ɗaɗɗaya suna barin falon harda masu sakin ƙananun tsuka dalilin ɓata musu lokaci da akayi da wannan wasan kwaikwayo da suka rigada suka saba dashi babu Wanda ya nuna damuwar cewa wai Mahaifinsa ne a wani yanayi da ko ba'a faɗa ba sunsan Hawan Jininsa ne ya tashi Allah ma ya taƙaita ba Paralysis ya samu ba irin wannan komawa da yayi ya faɗi akan kujera, wani abu ya tokarewa Alhaji Audu maƙoshi, hawaye ya ziraro a idanunsa abinda ya sake rikita Ahmad kenan a shekarunsa Talatin a Duniya sau ɗaya ya taɓa ganin ƙwalla a idon Mahaifinsa lokacin da aka kawo gawar Brigadier General Baballiya se yanzu kuma hawaye yake dagaske tabbas Al'amarin dake zuciyarsa ba ƙarami bane.
Yanda Dr Hassan ya dawo yaga Alhajin yasa yace kawai su kamashi a tafi Asibiti. Seda ya É—ura Ashar kafin su Salim suka saka hannu aka fita da Alhajin dan Manyan daman tun yana wajen yaga suna ta shigewa motocinsu suna jiran Iyalansu su fito su tafi, da alama Abincin da Hajiya tasa akayi zeyi bandaro dan zama beyi daÉ—in da har za'a jira cin abinci ba.
Hajiya ta ringa ihu kamar wadda ta shiga ƙaramin hauka, Ga Zakariyyah fuska harta suntume saboda haƙorin daya fita ba bisa ƙa'ida ba Naziru kuma na kwance numfashi ne kawai ya banbantashi da matacce Hussaini ya sauke masa duk wata giggiwa da yake fama da ita suma ɗin Dr Hassan ne yasa aka watsa su a mota duk suka rankaya a Asibitinsa. A hanya Ahmad ya kira Baba Alƙali yace masa yana tafe ya kusa isowa gidan Hajiya ƙarama ta kirashi se yace masa ai suna hanyar Asibiti be jira jin ba'asi ba yace ze same su acan domin yasan a runa.
Haka nan rana tsaka Audu ya tattaro irin wannan haɗuwar ba tareda yabi matakan da suka dace ba, zuri'ar da kowanne yake da wani fushi ko miki a zuciyarsa ta yaya zaka ce a lokaci gida zaka sasanta komai ka samu yanda kake so? Ya tabbatar wani abun akayi ko aka faɗa masa da ze saka jininsa ya hau tilas Allah dai ya taƙaita.
Emergency aka karɓi Alhaji Audu su Naziru ma aka watsa su inda ya kamata. Seda akayi stabilizing kowannensu kafin suka samu nutsuwar zuciya. Baba Alƙali ya ringa sababi kamar ya ari baki sanda Dr Hassan ya bashi taƙaitaccen labarin abinda ya faru.
"Ka kira Hussainin ka mai komai dare ya sameni a gida yau wane irin abu ne yake damunsa duk me ubanku ya muku ai baze canza masa suna ba ya za'ayi ya faɗa masa irin wannan maganar? Kai bama shi kaɗai ba gaba ɗayanku ku hallara ina son ganinku tunda naga alamar so kukeyi ku janyo mana abinda ze fi ƙarfin mu".
"
"Nima dai haka na gani Alƙali, ni daga yin abu dan Allah da zuciya ɗaya nace a shirya taron nan ya janyo yayansa a jiki su samu daidaito amma kaga yanda abu ya ƙare dana sani bance ayi ba haka kawai wannan la'anannen yaron ya cutar mun da yaya ya barsu da jinya" Hajiya Binta ta faɗa. Alƙali ya kalleta, cikin tsanin fushi yace