Sashe 65
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Toh ya kukayi da ita Fatiman? Babanta yace a bashi sati huÉ—u me tace maka akan hakan?"
"Bamuyi maganar ba Momy amma daman Baban nata yace ai wanda zasu karɓi auran ne basa nan shiyasa yace a basu lokaci amma ko ɗazu ma mun haɗu yace yana gaishe ku"
"Toh muna amsawa, ya kamata dai a fara abinda ya kamata dai toh, bari kaga wasu Atamfofi ɗazu *UMMU-MAHEER 07061838488* ta turasu a group ɗinta *BUYERS BATIK/ALIZA BATIK* ne kyau garesu quality kuwa ba'a magana gasu unique designs babban abin da yake burgeni dasu seka gama yayin Atamfar nan baka ci karo da me irinta a gari ba gasu basa koɗewa sedai ka gaji ka bayar kai *BUYERS BATIK* fa ta haɗu" ta ƙarasa tana miƙa masa wayar.
Ba wani sanin kan Atamfa yayi ba dan yafi ganin kyan Lace shi a jikin Fatima nema Atamfar take burgeshi amma yana ganin *BUYERS BATIK* ɗin ta tafi da imaninsa. Ya ringa scrolling yana duba designs ɗin da duk babu na banza a ciki, harya hasaso su jikin Fatima dan kalolin duka zasu karɓeta. Ya maida wayar yana cewa
"Amma sunyi kyau Momy"
"Ƙwarai ma kuwa, guda nawa za'a ɗauka?" Momy ta tambayeshi se yace
"Ki zaɓi wanda kike so se ki ɗaukarwa Maimuna ma nawace?" Ya mayar mata cikin rashin fahimtar inda zancenta ya dosa. Ta harareshi tace
"Tun yaushe muka zaɓi tamu, maganar lefenka nakeyi guda nawa za'a saka ko kuwa seta ƙare sannan?" Se ya hau shafa kai irin na yaji kunya kafin yace
"Ai duk sunyi kyau ma"
"Se a saka duka design goma ce" daga nan suka cigaba da tattaunawa wanda duk maganar auransa Momyn take sako masa.
Jay kuwa bayan sun isa falon Hajiya kwanciya yayi akan kujera tana ta aikin mita ta tafi can kitchen ɗinsu na baya inda suke hura Itacen da ita ta saka dole ake amfani dashi ta samo garwashi a cikin kasko. Tsabar magana tana zuba maganin a wutar seda hayaƙi ya turniƙeta ta fara tuttula tari har bata san sanda ta ture kaskon nata ba gaushin ya zube Allah ya rufa asiri akan Tiles ne carpet ba. Kansa kamar ze tsage masa haka ya tashi ya ɗakko ruwa ya kashe garwashin ya bawa Hajiyar tashi bata daddara ba faɗi tajeyi
"Shikenan ashe ba kai kaÉ—ai sukayi galaba akanka ba harda ni"
"Dan girman Allah Hajiya ki bari, ni lafiyata ƙalau na gaya miki gajiya nayi kawai bacci bake da buƙatar nayi yanzu" yanda yayi maganar ya saka Hajiya binsa da kallo shi kuma jin bata ce komai ya juya yana tafiya daƙyar saboda yanda zuciyarsa tayi masa nauyi Hajiyar kuma bata dakatar dashi ba. Kan gado ya kwanta ya rufe idonsa, wayarsa ta shiga ƙara a Jikinsa yaji cewar itace. Wani ɓari na zuciyarsa na rasa masa ya amsa ya tambayeta dalilinta na aikata musu abinda tayi inda ɗayan yayi galaba ta hanyar hanshi amsa wayar. Jin muryarta a yanzu babu abinda ze ƙara masa se baƙin ciki da damuwa. Har yanzu gani yakeyi kamar bada gaske bane, dukda a zahiri yaga komai ba gaya masa akayi ba amma so yakeyi ya ƙaryata hakan ya cewa zuciyarsa ba gaskiya bane ko kuma komai be faru ba.
Idanunsa suka sauka kan wayar Ahmad da yake chaji ya yunƙura daƙyar ya ɗaukota kansa na sara masa kamar ze tsage biyu. Number wayarta ya shiga dialing yana fatan ya zaman babu ita a wayar sedaj yana saka 0803 numbarta ce ta farko data zo a suggested contacts ga sunan da Ahmad ya mata saving dashi FATIMA da manyan baƙi se Jan Emoji me alamar zuciya a gaba. Ya runtse idonsa da ƙafin ya buɗe WhatsApp a hankali ya ringa bin chats ɗinsu kamar mr bitar karatu yana cike guraben maganganunta da ire iren daɗaɗan kalaman da take amfani dasu gurin magana dashi wanda saɓanin haka chat ɗin nata da Ahmad babu wani armashi balle soyayya a ciki. Ya ga hotunanta da basu da yawa idan aka haɗa da wanda ta tura masa shi daga haɗuwarsu zuwa yau ɗin, wato yarinyar first class maƙaryaciya ce, ma ha'inciya kuma Azzaluma.
Ya tuna wayarsu ta farko data tambayeshi ko shikaɗai Jay ɗan Nigeria dayake ƙwallo, me yasa tun a sannan be taɓa hasaso cewar ita ce ba?
Maida masa da wayar yayi jikin chaji ya kwanta rubda ciki ya danne kansa da pillow. So be kyauta musu ba daga shi har Yah Ahmad su rasa wadda zasu so se wannan Azzalumar mara tsoron Allah. Shi ya gama tabbatarwa ma da tasan su, tasan gidansu ɗaya shirya komai tayi ya kuma godewa Allah daya saka ya ganota tunda wuri kafin tayi nasarar karya zuciyar ɗan uwansa da babu komai cikinta face tarin Alkhairi da son kyautata mata. Yana jin Ahmad ya shigo lokacin kuma wayarsa ta sake ɗaukan ƙara a karo na babu Adadi amma be amsa ba se Ahmad ne daya shigo ya janyo wayar daga gefen kansa inda ya ajiyeta yana cewa
"Na gaya maka ka dena aje waya kusada kanka idan zakayi bacci bakaji kuma duk wannan ƙarar yanzu se kace baka ji ba toh Afeeyah ce kar gobe kazo kana mun kukan ta ƙi amsa wayarka".
Da hannu yaja wayar ya latseta gaba ɗaya ta mutu ba tareda ya amsa ba, Ahkad yayi sororo yana kallonsa, da kuma ya tuna ba matsalarsa bace se yaci gaba da abinda yakeyi ya gama yayi shirin kwanciya yabi lafiyar Gado. Zafin jikin Jay daya matseshi ne ya farkar dashi daga bacci dan shi bashida nauyin bacci ko kaɗan, ya taɓa Jay ɗin, zazzaɓi ne rau a jikinsa har numfashinsa hucin zafi yake fitarwa amma bacci yake wanda da gani bana daɗi bane. Ruwa ya samo me madaidaicin sanyi da ƙaramin Towel ya jiƙashi ya fara shafa masa a fusak, Jay ya saki ajiyar zuciya ya buɗe ido daƙyar ya kalli Ahmad ɗin kafin ya lumshe su. Da taimakon ruwan daya shafa masa da Maganin daya saka ya tashi yasha a lokacin zafin jikin ya ragur masa se Azababben ciwon kai da yakeji kamar ƙwayoyin idonsa zasu fito, kafin safiya ya fita hayyacinsa Idonsa yayi Jajir ga jijiyoyi a goshinsa kamar zasu faso su fito, yanda jikinsa ke karkarwar sanyi bayan yayiwo Alwala ya saka Ahmad dakatawa sukayi sallah a ɗakin sannan ya kamashi suka fita a duku dukun suka tafi Asibiti.
"Wai me ya same ka? Lafiya kau muka rabu jiya meya sameka a can in da kaje kuma?" Ahmad ya tambayeshi. Cikin dauriya yace masa
"Inaga Malaria ce, kwana biyu sauro ya cije ni"
"Sedai a gidansu Afeeyan ka kwaso Malaria dan mudai gidanmu babu sauro, kafin kazo seda akayi fumigation kuma still kullum se an saka magani, kuma Malaria ce zata kwantar da mutum haka lokaci ɗaya? Zamuje Asibiti dai koma menene yake damunka da baka so na sani zasu gayamun" Ahmad ya faɗa, shidai Jay be sake ce masa komai ba fama yake da jinyar fili data zuciya, abune goma da Ashirin yayi masa rubdugu lokaci ɗaya. Yarinyar daya ɗora dukkan buri da tanadinsa akanta, Macen da yake So tamkar ransa, da ita yake fatan ƙare rayuwarsa lokaci daya ta rikiɗa ta dawo Macen daya fi tsana a duniya, tun saninsa da ita yake jin ƙinta tun kafin ya ganta yasan wacece ita, abinda tayi musu a yanzu ya sake linka tsana da ƙiyayyarta me tsanani a zuciyarsa. Ya gane dalilin daya saka jininsa da ita a matsayin budurwar Ahmad ya ƙi haɗuwa, Soyayyar da sukayi a rashin sani wannan ya karɓeta a matsayin sakayyar abinda yake gayawa Ahmad dalilin soyayya da ita, Ubangiji ne ya nuna masa isharar cewa shi yake ƙunsa So a zuciyar bayinsa bawai yin kan mutum bane ba amma ya tsinewa dalilin zuwansa Zariya da har yayi silar haɗuwarsa da wannan Annamimiyar yarinyar me suffar salihai.
Asibitin Dr Hassan ya kaishi, basu tarar dashi ba se Dr Michel da yayi night duty shine ya dubashi. Ahmad yana waje yana jiransu dan daya shigar dashi fitowa yayi ya basu privacy. A ciki bayan Dr ya gama auna Bp sa saboda ciwon kai da yake shi yake damunsa kuma ido da fuskarsa ma sun nuna hakan. Cikin tsanaki ya kalleshi yace
"Bp ka yayi high sosai also rate na heart beat naka ya zarce misali me yake damuka?"
"Forget about it Dr, kawai ka bani necessary assistance and please don't tell anyone about it ka cewa Yah Ahmad Malaria ne yake damuna" Jay ya faɗawa Dr Michel, Dr ya zura masa ido ya buɗe baki da niyyar sake masa magana Jay ya haɗa hannaye biyu alamar roƙo yace
"Please, do me this favor"
"Fine amma dole koma menene ka cireshi daga ranka saboda lafiyarka ta daidaita ka sani this will not be good for your career and..."
"I know Dr i will try my best" ya sake katse shi. Dr ya girgiza kai kafin ya danna Ƙararrawar kiran Nurse se gata ta shigo. Paper daya rubuta prescription wa Jay ya bata ta tafi ta haɗa komai ta kai ɗakin da zasuyi admitting nasa zuwa Bp ya daidaita sannan ta koma ta gaya masa. Da kansa ya kamashi suna fita Ahmad ya tayashi har zuwa ɗakin, ruwa ya saka masa wanda ya zuba Allurai a ciki harda ta bacci babu daɗewa kuwa bacci yayi gaba dashi. Cikin damuwa Ahmad ya shiga tambayar Dr me ya samu Ƙaninsa yace masa Malaria ce. Ganin ya samu bacci yasa ya koma gida, Alhaji ya fara sanarwa Jay bashida lafiya yana Asibiti
"Bamuyi maganar ba Momy amma daman Baban nata yace ai wanda zasu karɓi auran ne basa nan shiyasa yace a basu lokaci amma ko ɗazu ma mun haɗu yace yana gaishe ku"
"Toh muna amsawa, ya kamata dai a fara abinda ya kamata dai toh, bari kaga wasu Atamfofi ɗazu *UMMU-MAHEER 07061838488* ta turasu a group ɗinta *BUYERS BATIK/ALIZA BATIK* ne kyau garesu quality kuwa ba'a magana gasu unique designs babban abin da yake burgeni dasu seka gama yayin Atamfar nan baka ci karo da me irinta a gari ba gasu basa koɗewa sedai ka gaji ka bayar kai *BUYERS BATIK* fa ta haɗu" ta ƙarasa tana miƙa masa wayar.
Ba wani sanin kan Atamfa yayi ba dan yafi ganin kyan Lace shi a jikin Fatima nema Atamfar take burgeshi amma yana ganin *BUYERS BATIK* ɗin ta tafi da imaninsa. Ya ringa scrolling yana duba designs ɗin da duk babu na banza a ciki, harya hasaso su jikin Fatima dan kalolin duka zasu karɓeta. Ya maida wayar yana cewa
"Amma sunyi kyau Momy"
"Ƙwarai ma kuwa, guda nawa za'a ɗauka?" Momy ta tambayeshi se yace
"Ki zaɓi wanda kike so se ki ɗaukarwa Maimuna ma nawace?" Ya mayar mata cikin rashin fahimtar inda zancenta ya dosa. Ta harareshi tace
"Tun yaushe muka zaɓi tamu, maganar lefenka nakeyi guda nawa za'a saka ko kuwa seta ƙare sannan?" Se ya hau shafa kai irin na yaji kunya kafin yace
"Ai duk sunyi kyau ma"
"Se a saka duka design goma ce" daga nan suka cigaba da tattaunawa wanda duk maganar auransa Momyn take sako masa.
Jay kuwa bayan sun isa falon Hajiya kwanciya yayi akan kujera tana ta aikin mita ta tafi can kitchen ɗinsu na baya inda suke hura Itacen da ita ta saka dole ake amfani dashi ta samo garwashi a cikin kasko. Tsabar magana tana zuba maganin a wutar seda hayaƙi ya turniƙeta ta fara tuttula tari har bata san sanda ta ture kaskon nata ba gaushin ya zube Allah ya rufa asiri akan Tiles ne carpet ba. Kansa kamar ze tsage masa haka ya tashi ya ɗakko ruwa ya kashe garwashin ya bawa Hajiyar tashi bata daddara ba faɗi tajeyi
"Shikenan ashe ba kai kaÉ—ai sukayi galaba akanka ba harda ni"
"Dan girman Allah Hajiya ki bari, ni lafiyata ƙalau na gaya miki gajiya nayi kawai bacci bake da buƙatar nayi yanzu" yanda yayi maganar ya saka Hajiya binsa da kallo shi kuma jin bata ce komai ya juya yana tafiya daƙyar saboda yanda zuciyarsa tayi masa nauyi Hajiyar kuma bata dakatar dashi ba. Kan gado ya kwanta ya rufe idonsa, wayarsa ta shiga ƙara a Jikinsa yaji cewar itace. Wani ɓari na zuciyarsa na rasa masa ya amsa ya tambayeta dalilinta na aikata musu abinda tayi inda ɗayan yayi galaba ta hanyar hanshi amsa wayar. Jin muryarta a yanzu babu abinda ze ƙara masa se baƙin ciki da damuwa. Har yanzu gani yakeyi kamar bada gaske bane, dukda a zahiri yaga komai ba gaya masa akayi ba amma so yakeyi ya ƙaryata hakan ya cewa zuciyarsa ba gaskiya bane ko kuma komai be faru ba.
Idanunsa suka sauka kan wayar Ahmad da yake chaji ya yunƙura daƙyar ya ɗaukota kansa na sara masa kamar ze tsage biyu. Number wayarta ya shiga dialing yana fatan ya zaman babu ita a wayar sedaj yana saka 0803 numbarta ce ta farko data zo a suggested contacts ga sunan da Ahmad ya mata saving dashi FATIMA da manyan baƙi se Jan Emoji me alamar zuciya a gaba. Ya runtse idonsa da ƙafin ya buɗe WhatsApp a hankali ya ringa bin chats ɗinsu kamar mr bitar karatu yana cike guraben maganganunta da ire iren daɗaɗan kalaman da take amfani dasu gurin magana dashi wanda saɓanin haka chat ɗin nata da Ahmad babu wani armashi balle soyayya a ciki. Ya ga hotunanta da basu da yawa idan aka haɗa da wanda ta tura masa shi daga haɗuwarsu zuwa yau ɗin, wato yarinyar first class maƙaryaciya ce, ma ha'inciya kuma Azzaluma.
Ya tuna wayarsu ta farko data tambayeshi ko shikaɗai Jay ɗan Nigeria dayake ƙwallo, me yasa tun a sannan be taɓa hasaso cewar ita ce ba?
Maida masa da wayar yayi jikin chaji ya kwanta rubda ciki ya danne kansa da pillow. So be kyauta musu ba daga shi har Yah Ahmad su rasa wadda zasu so se wannan Azzalumar mara tsoron Allah. Shi ya gama tabbatarwa ma da tasan su, tasan gidansu ɗaya shirya komai tayi ya kuma godewa Allah daya saka ya ganota tunda wuri kafin tayi nasarar karya zuciyar ɗan uwansa da babu komai cikinta face tarin Alkhairi da son kyautata mata. Yana jin Ahmad ya shigo lokacin kuma wayarsa ta sake ɗaukan ƙara a karo na babu Adadi amma be amsa ba se Ahmad ne daya shigo ya janyo wayar daga gefen kansa inda ya ajiyeta yana cewa
"Na gaya maka ka dena aje waya kusada kanka idan zakayi bacci bakaji kuma duk wannan ƙarar yanzu se kace baka ji ba toh Afeeyah ce kar gobe kazo kana mun kukan ta ƙi amsa wayarka".
Da hannu yaja wayar ya latseta gaba ɗaya ta mutu ba tareda ya amsa ba, Ahkad yayi sororo yana kallonsa, da kuma ya tuna ba matsalarsa bace se yaci gaba da abinda yakeyi ya gama yayi shirin kwanciya yabi lafiyar Gado. Zafin jikin Jay daya matseshi ne ya farkar dashi daga bacci dan shi bashida nauyin bacci ko kaɗan, ya taɓa Jay ɗin, zazzaɓi ne rau a jikinsa har numfashinsa hucin zafi yake fitarwa amma bacci yake wanda da gani bana daɗi bane. Ruwa ya samo me madaidaicin sanyi da ƙaramin Towel ya jiƙashi ya fara shafa masa a fusak, Jay ya saki ajiyar zuciya ya buɗe ido daƙyar ya kalli Ahmad ɗin kafin ya lumshe su. Da taimakon ruwan daya shafa masa da Maganin daya saka ya tashi yasha a lokacin zafin jikin ya ragur masa se Azababben ciwon kai da yakeji kamar ƙwayoyin idonsa zasu fito, kafin safiya ya fita hayyacinsa Idonsa yayi Jajir ga jijiyoyi a goshinsa kamar zasu faso su fito, yanda jikinsa ke karkarwar sanyi bayan yayiwo Alwala ya saka Ahmad dakatawa sukayi sallah a ɗakin sannan ya kamashi suka fita a duku dukun suka tafi Asibiti.
"Wai me ya same ka? Lafiya kau muka rabu jiya meya sameka a can in da kaje kuma?" Ahmad ya tambayeshi. Cikin dauriya yace masa
"Inaga Malaria ce, kwana biyu sauro ya cije ni"
"Sedai a gidansu Afeeyan ka kwaso Malaria dan mudai gidanmu babu sauro, kafin kazo seda akayi fumigation kuma still kullum se an saka magani, kuma Malaria ce zata kwantar da mutum haka lokaci ɗaya? Zamuje Asibiti dai koma menene yake damunka da baka so na sani zasu gayamun" Ahmad ya faɗa, shidai Jay be sake ce masa komai ba fama yake da jinyar fili data zuciya, abune goma da Ashirin yayi masa rubdugu lokaci ɗaya. Yarinyar daya ɗora dukkan buri da tanadinsa akanta, Macen da yake So tamkar ransa, da ita yake fatan ƙare rayuwarsa lokaci daya ta rikiɗa ta dawo Macen daya fi tsana a duniya, tun saninsa da ita yake jin ƙinta tun kafin ya ganta yasan wacece ita, abinda tayi musu a yanzu ya sake linka tsana da ƙiyayyarta me tsanani a zuciyarsa. Ya gane dalilin daya saka jininsa da ita a matsayin budurwar Ahmad ya ƙi haɗuwa, Soyayyar da sukayi a rashin sani wannan ya karɓeta a matsayin sakayyar abinda yake gayawa Ahmad dalilin soyayya da ita, Ubangiji ne ya nuna masa isharar cewa shi yake ƙunsa So a zuciyar bayinsa bawai yin kan mutum bane ba amma ya tsinewa dalilin zuwansa Zariya da har yayi silar haɗuwarsa da wannan Annamimiyar yarinyar me suffar salihai.
Asibitin Dr Hassan ya kaishi, basu tarar dashi ba se Dr Michel da yayi night duty shine ya dubashi. Ahmad yana waje yana jiransu dan daya shigar dashi fitowa yayi ya basu privacy. A ciki bayan Dr ya gama auna Bp sa saboda ciwon kai da yake shi yake damunsa kuma ido da fuskarsa ma sun nuna hakan. Cikin tsanaki ya kalleshi yace
"Bp ka yayi high sosai also rate na heart beat naka ya zarce misali me yake damuka?"
"Forget about it Dr, kawai ka bani necessary assistance and please don't tell anyone about it ka cewa Yah Ahmad Malaria ne yake damuna" Jay ya faɗawa Dr Michel, Dr ya zura masa ido ya buɗe baki da niyyar sake masa magana Jay ya haɗa hannaye biyu alamar roƙo yace
"Please, do me this favor"
"Fine amma dole koma menene ka cireshi daga ranka saboda lafiyarka ta daidaita ka sani this will not be good for your career and..."
"I know Dr i will try my best" ya sake katse shi. Dr ya girgiza kai kafin ya danna Ƙararrawar kiran Nurse se gata ta shigo. Paper daya rubuta prescription wa Jay ya bata ta tafi ta haɗa komai ta kai ɗakin da zasuyi admitting nasa zuwa Bp ya daidaita sannan ta koma ta gaya masa. Da kansa ya kamashi suna fita Ahmad ya tayashi har zuwa ɗakin, ruwa ya saka masa wanda ya zuba Allurai a ciki harda ta bacci babu daɗewa kuwa bacci yayi gaba dashi. Cikin damuwa Ahmad ya shiga tambayar Dr me ya samu Ƙaninsa yace masa Malaria ce. Ganin ya samu bacci yasa ya koma gida, Alhaji ya fara sanarwa Jay bashida lafiya yana Asibiti