Sashe 59
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sanda yaje ɗaki ya tarar Ahmad har yayi bacci, tun daya sahalewa kansa waccen mayyar yake bacci sosai da kuwa seya raba dare yana tsammatar kiranta kuma ba zata kira ba. Ya gama abinda zeyi ya kwanta sedai bacci ya gagara zuwar masa. Tunani kala kala suka addabeshi, laifin da Afeeyah ta masa na boye masa tana da wani bayan shi amma a yanzu damuwar Hajiya ta shafe wannan. Ta yaya ze sanar da saɓanin abinda take hasashe kuma irin abinda yasan zata gwammaci jin komai dashi wato ace shi Jafar data ciwa burin duniya kan matar auransa take zakwaɗin zuwan lokaci se kurum taji akasin abinda take buri wato dai a maimakon taji za'a tafi gidan Tayis Ac sama da ƙasa se a shige Lokon Alfindiki gidan laka shi ya tabbatar yar Bakamiken da Yah Ahmad ya kwaso in ba'ayi wasa ba tafi Afeeyah galihu.
Wannan al'amarin kacokan yana ganin ishara ce Allah ya gwada musu daga shi har Hajiyar, dukda shi bece ya tsani Talaka ba kuma be taɓa inkarin cewar baze auri ɗiyar Talaka ba ta yuwu izgilancin daya ke yiwa Ahmad ne kan zuciyarsa bata san abinda ya kamata dashi ba duk matan Kano ya rasa wadda ze so se yar Bakanike se gashi ubangiji ya masa talala ya jefashi a komar wadda yake ga nata uban ko Tartibiyar Sana'a bashi da ita.
Ya shafa ƙeya jin a garin lissafi ya sake tafka wata ɓaranɓaramar, ya za'ayi kai tsaye ya yanke Babanta bashida sana'a dame yake ciyar dasu sedai in ɓarawo ne ko ɗan Maula irin Babansu Anty Rabi.
"Allah na tuba" ya faÉ—a a fili jin shaiÉ—an na sake ingizashi izgilancin nasa na neman tsallakawa kan Baban Hajiya Rabi kuma.
"Meya faru?" Ahmad da yayi juyi a bacci ya tambayeshi, bashi da nauyin bacci ko yaya akayi magana yanaji.
"Zancen zuci ne ya fito fili, sorry na tasheka" Jay ya faɗa yana gyara kwanciya Ahmad ma baccinsa ya koma ya barshi yana cigaba da saƙa da warwara. Yayi tunanin ya ɓoye wa Hajiya Asalin Afeeyah ayi komai a sirrance tunda dai yasan Baba Alƙali baze kware masa baya ba, shima kuma Alhajin ko ya samu labari baze sake Ƙaiƙayin bakin gayawa Hajiyar ba dan silar na Ahmad har yau be gama komawa daidai maganganun da Yayansa suka sossoka masa ba basu gama sakinsa ba to amma kuma hakan bashida Fa'ida, duk yanda akayi daga baya magana seta fasu kuma abinda Hajiyar zatayi ta yuwu seya zarce wanda zatayi idan tasan komai tun daga mafari. Ko bayan wannan ma shi baze yarda ya gina wata mu'amala tasa da ƙarya ko yaudara ba musamman maganar aure, to shi yaya zeyi yanzu? Yana son Afeeyah so me tsanani cewar ya rabu da ita bama abu ne me yuwuwa ba to ya kuma zeyi da mahaifiyarsa da a duniya babu abinda ta tsana irin Talaka da Talauci??
Bacci ɓarawo ne yayi nasarar sace shi da Asuba kuwa ya farka da ciwon kai dan be daɗe da baccin ba Ahmad ya tashe shi Asuba tayi ga tunani daya raba dare yanayi. Be iya dogon zaman lazumin da Ahmad yake tilasta masa yi ba idan yazo gida ya bi lafiyar gado saboda bacci da ciwon da kansa yake masa, lura da kamar baya jin daɗi dan har idanunsa sun nuna hakan yasaka Ahmad be matsa masa ba shidai yaci gaba da jan carbinsa. Tun jiya yake fama da faɗuwar gaba daya rasa ta mecece ga tunanin Fatima daya masa sauƙi kwana biyu ya juyo dan seda yayi dagaske jiya kafin ya iya dakatar da kansa daga kiranta. Tunda Baba Alƙali ya shaida masa Baffah yace su dakata da zuwa daga nan ya sare daga lamarinta ya tabbata ya rasata kenan tun sannan kuma ya tilasta kansa haƙuri da al'amuranta, ko dar beji sonta ya ragu a ransa ba amma ya taushi zuciyarsa ta karɓi ƙaddarar cewa Fatima ba matarsa bace, yana tsaka da jinyar zuciyarsa kuma sabon abu ya fara bijiro masa daga jiya zuwa yau ɗin tamkar ana masa kiranye haka yakejin so me zafi yana Azalzakar zuciyarsa, kasa dakatar da kansa yayi yabi umarnin zuciyarsa ya cire wayarsa dake jikin chaji ya doka mata kira.
FATIMA
Tana kwance kan abin sallah wand kusan akansa ta kwana, tun bayan da Umma ta gama soka mata maganganu jiya ta shiga ɗaki ta ringa kuka, Allahn daya jarabci zuciyarta da soyayya shi kaɗai yasan halin da take ciki se Baffah da ya tausaya mata yake ƙoƙarin ganin ta samu cikar muradinta badan haka tasa zuciyar taso ba Umma kuwa ta juya zuciyarta baibai taƙi fahimtarta ta yaya zatace ta zare hannunta daga Al'amuranta? Tana fatan ace barazana takeyi mata saboda ta fasa abinda tayi niyya dan in da gaskene ina zata kama tayaya ma koda ace burinta ya cika na zama matar Jay zata samu farin ciki da nutsuwa alhalin Ummanta tana fushi da ita??
Haka ta raba dare tana koke koke daga ƙarshe taci galaba akan shaiɗanin da yake neman nesantata daga neman ɗauki gurin ubangijinta ta fita tayo Alwala ta ringa jera salloli, a baya koda babu yawa takan tashi tayi sallah ta kaiwa Allah kokenta da buƙatunta amma tun da suka fara raba dare suna zuba sharafin soyayya da Jay shaiɗan yayi kinini ya samu abinda yake so. Sanda ya kamata ta tashi tayi sallolin se baccin da batayi da wuri ba da gajiyar data kwasa a yinin su danneta, sallar Asuba ita da take tashin yan ɗakinsu ya zama yanzu ita ake tashi duk free time da take zama ta jaddada kusancinta da mahaliccinta soyayyar Jay ta cinye yau da duniyar ta mata zafi ta ko ina gashi take karɓa dole ta fuskanci mai duka ta kai amsa kukanta.
A baya takan yawaita addu'ar neman zaɓin Allah a cikin lamuran rayuwarta gaba ɗaya, yanda Ahmad ya kasa samun matsuguni a zuciyarta duk kuwa da tarin kyawawan halayensa yasa kawai ta yankewa ranta ba Alkhairinta babe shiyasa ubangiji be haɗa zuciyoyinsu guri guda ba, da Jay ya afko mata yanda ya shiga ranta farat ɗaya nan kuma ta yanke shine cikar burin datake jira Allah ya aiko mata. Bata nemi zaɓin Allah ba kawai ta yanke shiɗinne kamar yanda bata nema akan Ahmad ba ta yanke bashi bane.
Ance ba'ayin aure salin alin amma kuma bata tsammaci auran da ze saka ta samu tangarɗa da iyayenta ba ze zamo Alkhairi a rayuwarta ta yaya ma haka zata faru?? Umma tace ta zare hannu a al'amarinta ta ina zata ga haske a gidan Jay?? Toh amma idan ta haƙura dashi yaya rayuwarta zata kasance? Ta tabbatar babu ita babu farin ciki a gidan auran da ba Jay bane ze kasance Mamallakinta, shi take So, shi zuciyarta ta aminta dashi amma kuma Albarkar iyayenta nada muhimmanci da tasiri a cikin rayuwar da zata gabatar tare dashi.
Ta ringa jera sallah tana kuka wiwi tareda kwashe mintoci masu yawa a sujjadarta tana kaiwa Allah kokenta da neman agajinsa a wannan siraɗi da take kai, seda taji sallar Asuba kafin bacci ya kwasheta bata jima ba cikin baccin ta ringajin ƙarar wayarta data ajiye dabda kanta bayan ta duba lokaci kafin baccin ya kwasheta. Tayi firgigit ta farka, mafarki take wai Jay yazo a fusace ya ɗaga hannu ze kwasa mata mari be kai ga aiwatar da nufinsa ba ta farka tana zare ido, akan me Jay ze mareta a mafarki? Koda yake da fushinta ya tafi jiya ƙila ya huce ne shine ma yake kiranta yanzu da wannan tunanin ta janyo wayar da azama ta duba.
Sunana Ahmad ta gani da manyan baƙi suna yawo a kan wayar, ta ringa maimaita sunan a ranta tamkar ranar ta fara ganin kalmar.
"Allah ka haskamun abinda yafi zama Alkhairi a rayuwata, Allah karkasa aurena ya zama silar gamuwata da mahaifana" Addu'ar data ringa nanatawa a sujjadarta tana bin bayanta da sunayen Allah tsarkaka tare da cikakken yaƙinin samun biyan buƙata. Ahmad da ta manta rabon da suyi magana a waya dashi tun kafin dawowar Jay kamar tun ranar da Anty Sauda ta tilasta mata kiransa ta bashi haƙuri shine yake kiranta yau da farar safiyar nan?
A maimakon ta amsa wayar se kawai ta kifeta ta fashe da kuka kamar wadda aka mara ta ringayi harda shashsheƙa shi kuwa kamar yasan meke faruwa ya ringa kira har seda ta amsa ba tareda ta bar kukan da takeyi ba.
AHMAD
A gigice ya miƙe tsaye bayan da Fatima ta amsa wayarz kira uku ya mata kafin ta amsa ana huɗun ya raya a ransa bacci takeyi amma kuma abinda yakeji a ransa game da ita yasa ya kasa haƙura da kiran har seda ta amsa.
"Lafiya Fatima, meya sameki? Meya faru kike kuka?" Ya jera mata tambayoyi a rikice, daga can gefen ta sake kecewa da kukan daya fi na farko ba tareda ta bashi amsa ba, ya wuce ya buÉ—e wardrobe inda Jallabiyyunsa suke yake dubawa da alamu ya manta da wata a jikinsa saboda ruÉ—ewa
"Dan girman Allah ki faÉ—amun meya faru? Me yasa kike irin wannan kukan?" Ya sake faÉ—i yana zaro riga ya shiga kici kicin sakata akan ta jikinsa.
"Bani da lafiya, ƙirjina ciwo yakeyi" ta faɗa tana jan numfashi kamar zata shiɗe, yaja salati ya dire kafin ya saki rigar hannunsa ya nufi ƙofa se kuma ya dawo da sauri ya shiga jijjiga Jay da tun fara wayar daya ambaci sunanta ya kasa kunne yana jinsa dan baccin nasa beyi nisa ba.
"Meye kuma?" Ya faɗa yana miƙa kamar sannan ya tashi. Ahmad ya latse wayar ya kashe kafin yace masa
"Ka tashi muje, Fatima ce bata da lafiya"
"Alhamdulillahi Allah yasa ta mutu kowa ya huta" Jay ya faɗa kafin ya juya abinda ya kwanta harda jan Duvet ya rufe har kansa. Ahmad yayi kasaƙe yana kallonsa kafin kuma ya tuna abinda yake gabansa ya sauke ajiyar zuciya me ƙarfi ya fice.
Dake safiya ce ko bakwai batayi kuma ana hutun makaranta dan haka babu cinkoso akan titi nan da nan ya isa unguwarsu Fatima. Ko buɗe ɗe ƙofa basuyi ba ko kuma sakayota akayi oho ya niyyata ze buga kenan ya hango Baffah yana tahowa da carbi a hannunsa da alama sannan ya fito daga masallaci.
Wannan al'amarin kacokan yana ganin ishara ce Allah ya gwada musu daga shi har Hajiyar, dukda shi bece ya tsani Talaka ba kuma be taɓa inkarin cewar baze auri ɗiyar Talaka ba ta yuwu izgilancin daya ke yiwa Ahmad ne kan zuciyarsa bata san abinda ya kamata dashi ba duk matan Kano ya rasa wadda ze so se yar Bakanike se gashi ubangiji ya masa talala ya jefashi a komar wadda yake ga nata uban ko Tartibiyar Sana'a bashi da ita.
Ya shafa ƙeya jin a garin lissafi ya sake tafka wata ɓaranɓaramar, ya za'ayi kai tsaye ya yanke Babanta bashida sana'a dame yake ciyar dasu sedai in ɓarawo ne ko ɗan Maula irin Babansu Anty Rabi.
"Allah na tuba" ya faÉ—a a fili jin shaiÉ—an na sake ingizashi izgilancin nasa na neman tsallakawa kan Baban Hajiya Rabi kuma.
"Meya faru?" Ahmad da yayi juyi a bacci ya tambayeshi, bashi da nauyin bacci ko yaya akayi magana yanaji.
"Zancen zuci ne ya fito fili, sorry na tasheka" Jay ya faɗa yana gyara kwanciya Ahmad ma baccinsa ya koma ya barshi yana cigaba da saƙa da warwara. Yayi tunanin ya ɓoye wa Hajiya Asalin Afeeyah ayi komai a sirrance tunda dai yasan Baba Alƙali baze kware masa baya ba, shima kuma Alhajin ko ya samu labari baze sake Ƙaiƙayin bakin gayawa Hajiyar ba dan silar na Ahmad har yau be gama komawa daidai maganganun da Yayansa suka sossoka masa ba basu gama sakinsa ba to amma kuma hakan bashida Fa'ida, duk yanda akayi daga baya magana seta fasu kuma abinda Hajiyar zatayi ta yuwu seya zarce wanda zatayi idan tasan komai tun daga mafari. Ko bayan wannan ma shi baze yarda ya gina wata mu'amala tasa da ƙarya ko yaudara ba musamman maganar aure, to shi yaya zeyi yanzu? Yana son Afeeyah so me tsanani cewar ya rabu da ita bama abu ne me yuwuwa ba to ya kuma zeyi da mahaifiyarsa da a duniya babu abinda ta tsana irin Talaka da Talauci??
Bacci ɓarawo ne yayi nasarar sace shi da Asuba kuwa ya farka da ciwon kai dan be daɗe da baccin ba Ahmad ya tashe shi Asuba tayi ga tunani daya raba dare yanayi. Be iya dogon zaman lazumin da Ahmad yake tilasta masa yi ba idan yazo gida ya bi lafiyar gado saboda bacci da ciwon da kansa yake masa, lura da kamar baya jin daɗi dan har idanunsa sun nuna hakan yasaka Ahmad be matsa masa ba shidai yaci gaba da jan carbinsa. Tun jiya yake fama da faɗuwar gaba daya rasa ta mecece ga tunanin Fatima daya masa sauƙi kwana biyu ya juyo dan seda yayi dagaske jiya kafin ya iya dakatar da kansa daga kiranta. Tunda Baba Alƙali ya shaida masa Baffah yace su dakata da zuwa daga nan ya sare daga lamarinta ya tabbata ya rasata kenan tun sannan kuma ya tilasta kansa haƙuri da al'amuranta, ko dar beji sonta ya ragu a ransa ba amma ya taushi zuciyarsa ta karɓi ƙaddarar cewa Fatima ba matarsa bace, yana tsaka da jinyar zuciyarsa kuma sabon abu ya fara bijiro masa daga jiya zuwa yau ɗin tamkar ana masa kiranye haka yakejin so me zafi yana Azalzakar zuciyarsa, kasa dakatar da kansa yayi yabi umarnin zuciyarsa ya cire wayarsa dake jikin chaji ya doka mata kira.
FATIMA
Tana kwance kan abin sallah wand kusan akansa ta kwana, tun bayan da Umma ta gama soka mata maganganu jiya ta shiga ɗaki ta ringa kuka, Allahn daya jarabci zuciyarta da soyayya shi kaɗai yasan halin da take ciki se Baffah da ya tausaya mata yake ƙoƙarin ganin ta samu cikar muradinta badan haka tasa zuciyar taso ba Umma kuwa ta juya zuciyarta baibai taƙi fahimtarta ta yaya zatace ta zare hannunta daga Al'amuranta? Tana fatan ace barazana takeyi mata saboda ta fasa abinda tayi niyya dan in da gaskene ina zata kama tayaya ma koda ace burinta ya cika na zama matar Jay zata samu farin ciki da nutsuwa alhalin Ummanta tana fushi da ita??
Haka ta raba dare tana koke koke daga ƙarshe taci galaba akan shaiɗanin da yake neman nesantata daga neman ɗauki gurin ubangijinta ta fita tayo Alwala ta ringa jera salloli, a baya koda babu yawa takan tashi tayi sallah ta kaiwa Allah kokenta da buƙatunta amma tun da suka fara raba dare suna zuba sharafin soyayya da Jay shaiɗan yayi kinini ya samu abinda yake so. Sanda ya kamata ta tashi tayi sallolin se baccin da batayi da wuri ba da gajiyar data kwasa a yinin su danneta, sallar Asuba ita da take tashin yan ɗakinsu ya zama yanzu ita ake tashi duk free time da take zama ta jaddada kusancinta da mahaliccinta soyayyar Jay ta cinye yau da duniyar ta mata zafi ta ko ina gashi take karɓa dole ta fuskanci mai duka ta kai amsa kukanta.
A baya takan yawaita addu'ar neman zaɓin Allah a cikin lamuran rayuwarta gaba ɗaya, yanda Ahmad ya kasa samun matsuguni a zuciyarta duk kuwa da tarin kyawawan halayensa yasa kawai ta yankewa ranta ba Alkhairinta babe shiyasa ubangiji be haɗa zuciyoyinsu guri guda ba, da Jay ya afko mata yanda ya shiga ranta farat ɗaya nan kuma ta yanke shine cikar burin datake jira Allah ya aiko mata. Bata nemi zaɓin Allah ba kawai ta yanke shiɗinne kamar yanda bata nema akan Ahmad ba ta yanke bashi bane.
Ance ba'ayin aure salin alin amma kuma bata tsammaci auran da ze saka ta samu tangarɗa da iyayenta ba ze zamo Alkhairi a rayuwarta ta yaya ma haka zata faru?? Umma tace ta zare hannu a al'amarinta ta ina zata ga haske a gidan Jay?? Toh amma idan ta haƙura dashi yaya rayuwarta zata kasance? Ta tabbatar babu ita babu farin ciki a gidan auran da ba Jay bane ze kasance Mamallakinta, shi take So, shi zuciyarta ta aminta dashi amma kuma Albarkar iyayenta nada muhimmanci da tasiri a cikin rayuwar da zata gabatar tare dashi.
Ta ringa jera sallah tana kuka wiwi tareda kwashe mintoci masu yawa a sujjadarta tana kaiwa Allah kokenta da neman agajinsa a wannan siraɗi da take kai, seda taji sallar Asuba kafin bacci ya kwasheta bata jima ba cikin baccin ta ringajin ƙarar wayarta data ajiye dabda kanta bayan ta duba lokaci kafin baccin ya kwasheta. Tayi firgigit ta farka, mafarki take wai Jay yazo a fusace ya ɗaga hannu ze kwasa mata mari be kai ga aiwatar da nufinsa ba ta farka tana zare ido, akan me Jay ze mareta a mafarki? Koda yake da fushinta ya tafi jiya ƙila ya huce ne shine ma yake kiranta yanzu da wannan tunanin ta janyo wayar da azama ta duba.
Sunana Ahmad ta gani da manyan baƙi suna yawo a kan wayar, ta ringa maimaita sunan a ranta tamkar ranar ta fara ganin kalmar.
"Allah ka haskamun abinda yafi zama Alkhairi a rayuwata, Allah karkasa aurena ya zama silar gamuwata da mahaifana" Addu'ar data ringa nanatawa a sujjadarta tana bin bayanta da sunayen Allah tsarkaka tare da cikakken yaƙinin samun biyan buƙata. Ahmad da ta manta rabon da suyi magana a waya dashi tun kafin dawowar Jay kamar tun ranar da Anty Sauda ta tilasta mata kiransa ta bashi haƙuri shine yake kiranta yau da farar safiyar nan?
A maimakon ta amsa wayar se kawai ta kifeta ta fashe da kuka kamar wadda aka mara ta ringayi harda shashsheƙa shi kuwa kamar yasan meke faruwa ya ringa kira har seda ta amsa ba tareda ta bar kukan da takeyi ba.
AHMAD
A gigice ya miƙe tsaye bayan da Fatima ta amsa wayarz kira uku ya mata kafin ta amsa ana huɗun ya raya a ransa bacci takeyi amma kuma abinda yakeji a ransa game da ita yasa ya kasa haƙura da kiran har seda ta amsa.
"Lafiya Fatima, meya sameki? Meya faru kike kuka?" Ya jera mata tambayoyi a rikice, daga can gefen ta sake kecewa da kukan daya fi na farko ba tareda ta bashi amsa ba, ya wuce ya buÉ—e wardrobe inda Jallabiyyunsa suke yake dubawa da alamu ya manta da wata a jikinsa saboda ruÉ—ewa
"Dan girman Allah ki faÉ—amun meya faru? Me yasa kike irin wannan kukan?" Ya sake faÉ—i yana zaro riga ya shiga kici kicin sakata akan ta jikinsa.
"Bani da lafiya, ƙirjina ciwo yakeyi" ta faɗa tana jan numfashi kamar zata shiɗe, yaja salati ya dire kafin ya saki rigar hannunsa ya nufi ƙofa se kuma ya dawo da sauri ya shiga jijjiga Jay da tun fara wayar daya ambaci sunanta ya kasa kunne yana jinsa dan baccin nasa beyi nisa ba.
"Meye kuma?" Ya faɗa yana miƙa kamar sannan ya tashi. Ahmad ya latse wayar ya kashe kafin yace masa
"Ka tashi muje, Fatima ce bata da lafiya"
"Alhamdulillahi Allah yasa ta mutu kowa ya huta" Jay ya faɗa kafin ya juya abinda ya kwanta harda jan Duvet ya rufe har kansa. Ahmad yayi kasaƙe yana kallonsa kafin kuma ya tuna abinda yake gabansa ya sauke ajiyar zuciya me ƙarfi ya fice.
Dake safiya ce ko bakwai batayi kuma ana hutun makaranta dan haka babu cinkoso akan titi nan da nan ya isa unguwarsu Fatima. Ko buɗe ɗe ƙofa basuyi ba ko kuma sakayota akayi oho ya niyyata ze buga kenan ya hango Baffah yana tahowa da carbi a hannunsa da alama sannan ya fito daga masallaci.