← Book details Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 63 OF 71

Sashe 63

Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Shikenan ki shiga ciki, bari na sake trying number Jafar idan yazo se ki leƙo ku gaisa ko yayane dan Allah kinga babu daɗi ace yazo kuma baku haɗu ba"
"Tam" ta bashi amsa tana ƙoƙarin juyawa ciki Baffa ya iso gurin, yanda kasan wanda yaga wani da suke wasa ɓuya haka ya sauke ido ƙasa ya kasa kallon Ahmad shi kuma cikin girmamaqar daya saba yi masa ya durƙusa ya shiga gaishe shi ya wuce ciki ya barsu a tsaye.

"Kinga yau kuma Baffah surukuta yakeyi dani daga fara maganar auranmu dukda ma yace a bashi sati huɗu zeyi musu magana" Ahmad ya faɗa bayan da Baffah ya shige ciki, batace masa kamai ba se dafe dafenkai da yamutsar data cigaba da yi hakan ya tuna masa da ciwon da tace yana mata yace ta shiga gida ta wuce har sannan dafe da kai yana binta da sannu. Seda ta shige kafin ya sake ciro waya ya shiga kiran Jay a sannan kuma aka ce masa Call waiting tana dab da tsinkewa ya ɗaga muryarsa tamkar wanda yake maye ko cikin wani shauƙi yace
"I'm sorry Yah Ahmad kuka ta saka mun ni kuma banma san yanda akayi ba kawai na ganni a ƙofar gidansu".

Ahmad ya buÉ—e baki kamar yana gabansa yace
"Tafiya kayi, kuma kake cemun baka san yanda akayi ka ganka a gidansu ba ko saboda ka raina wayo ai shikenan ita kuma motar tana ina toh?"
"I'm coming back to pick you" Jay ya sake faÉ—a da muryar da tafi ta farko zama wata iri, Ahmad yace
"Zan hau Napep, and abinda zance maka kaji tsoron Allah kabar koma menene kake aikatawa a inda kake"
"Thanks" Jay ya amsa shi kafin ya katse wayar ya bar Ahmad da waya a kunne cikin mamaki. Wato saurin da yakeyi kenan so yake yaje ya taɓa yar mutane, kenan Jafar be bar halayyarsa ba har akan macen da yake iƙirarin yana so ze aureta seya gwada mummunar ɗabi'arsa kenan? Tunanin daya ringa masa yawo akai.

Ya aje wayar cikin rashin jin daɗin abin ga ciwon kan daya tasowa Fatima a gefe duk suka dagula masa lissafi suka kore farin cikin daya ke ciki a daren. Titi ya fita ya tare Adaidaita da ze kaishi gida, da ace yasan gidan su Budurwar Jafar ɗin can zeje da ace kuma ya san abinda zeje aikatawa kenan da be barshi ya tafi shi kaɗai ba, dole ma ya kaiwa Baba Alƙali ƙarar Jay akan ire iren abubuwan nan da yake aikatawa, idan aure yake so yayi kawai Ƙila ya shiga hankalinsa ya dena wannan shirmen.

A ɓangaren Jay kuwa tafiya ya ringayi a motar ba tareda yasan inda ya nufa ba, seda yayi tafiya me nisa ya bi titin bypass kamar me shirin tafiya Bechi a daren seda ya wuce guraren cunkoson mutane kafin ya samu gefen titi ya gangara ya tsaya ba tareda ya kashe motar ba yayi parking kawai ya kwantar da kansa akan steery. Ya kasa relating abu, Fatiman Yah Ahmad itace Afeeyarsa, Afeeyarsa ita ce Fatiman Yah Ahmad a garin yaya? Ya akayi haka ta faru? Tunani ya shigayi na haɗuwarsa da Afeeyah har zuwa yau, babu wata kafa ko siga da zata saka ya zargi wani abu akanta, babu abinda be sani akanta ba amma koda wasa zuciyarsa bata taɓa kwatanta cewar zata iya zama ita ce Fatiman Yah Ahmad ba, abinda yake so ya fahimta yanzu shin Coincidence ne ko kuma Set up plan?

Arashine ko ita ta shirya komai ta haɗa soyayyarsa data Ɗan uwansa mafi soyuwa a gareshi guri ɗaya? Idan shiri ne menene ribarta akanyin haka? Me suka mata data zaɓi hukunta zukatansu da hukunci mafi muni irin wannan?
Yana buƙatar sanin amsar waɗannan tambayoyin kafin sanin abin da zeyi a gaba.

Wani abu yakeji a zuciyarsa, ya zarce ya ce zafi yakeji ko ciwo koma menene besan me ze kirashi ba. Ta yaya za'ayi suyi tarayya cikin Son abu ɗaya shida Yah Ahmad? Tilas wannan ya kasan ce shiri dukda ya sani Allah babu yanda baya sanya Al'amura su kasance amma yana da yaƙinin ubangiji baze tagayyara zumunchin da yake tsakaninsa da Yah Ahmad.

Ya saka hannun akan fuskarsa yana goge danshin dayaji yana bin kuncinsa, shi kansa yayi mamakin kansa Hawaye ne wanda fitarsa ke cakuɗe da dalilai da yawa, Allah ya sani be taɓa jin son wata Mace a duniya irin yanda yakeji akan yarinyar nan ba, zuwansa Kaduna gurin Anty Ummu Yayar Hajiya Binta yaje saboda a kaf dangin mahaifiyarsa ita kaɗaice yake da tabbacin zata iya tarar gaban Hajiyar ta feɗe mata gaskiya komai ɗacinta kuma itace yake da yaƙinin zata bashi goyon baya akan auran Afeeyah. Hajiya Ummu ta goyi bayansa dukda ta jinjina Al'amarin domin burin Hajiya sananne ne ga kowa akan sa. Kowa yasan tanadin da take dashi akan Matar auransa. Ita kanta Hajiya Ummun yarta Samiha ta soshi kuma da ace yana da ra'ayin auran Zumunchi daya auri Samiha kodan Anty Ummun amma haka Hajiya ta shafawa idonta kwalli ta manta cewar Ummu ce ta saki Nono ta kama a gaban kowa tace me uban Samiha yake dashi da zata haɗa surukuta da yarsa?

Abinda Anty Ummu ta fara masa bayan daya mata bayanin komai tace "Allah ne ya kama Binta, burin data ci akanka baze zamo gaskiya ba, kanaji ko Jafar idan har kana son wannan yarinyar kar kaji komai kar kuma wani abu ya baka tsoro ka tafi kanka tsaye ka nemi auranta. Karka bi takan Binta ko Mahaifinku domin bakin ganga ne se yanda ta kaɗashi ka tafi kai tsaye ka samu Alƙali nasan in sha Allahu zeyiwa duk wata ɓaraka da ka iya tasowa togaciya tunda wuri, kuskuren da Ahmad yayi kenan amma tunda Alƙali ya karɓi maganar wa ka sake jin yace wani abu akai?"

"Amma Mama Ina tsoron Abinda Hajiya zata yi idan taji maganar nan daga baya shiyasa nake tunanin ki fara sanar mata a lallaɓata harta amince da kanta sannan" Jay ya faɗa, Hajiya Ummu tace
"Jafar kenan, shawara dai kake nema a gurin kuma na baka, wlh tallahi badai Bintar dana sani ce zata amince da maganar nan da kazo da ita ba, tunda dai ba abune daya saɓawa shari'a kake shirin aikatawa ba magana ce ta aure, idan kuma daman ba son yarinyar kakeyi ba to kaitsaye ka janye kawai karma ka janyo wani abin kace nace ka jawowa yarinya suna zaune lafiya da iyayenta Jarabar Binta ta dirar musu, kaje ka samu Alƙali shi ze san duk ta yanda ze biyowa abun" Abinda Hajiya Ummu ta gaya masa kenan, Daya sake nuna mata hoton Afeeyah data buƙata bayan ta gani tace masa

"Niko kamar nasan fuskar nan a wani guri" a lokacin yace mata
"Nafa tura miki hotonta kwanaki can Mama" ya faÉ—a seta jijjiga kai tace
"Tabbas na tuna, gata tabarakalla, Allah yasa yanda take da kyaun fuska haka zuciyarta take" nana suka Ƙarƙare daita bayan ta sake jaddada masa yaje ya samu Baba Alƙali kaitsaye kar yabi ta kan Hajiyarsu, daga can ya wuce Abuja gidan Hafsatu kashe tata wutar, maganganun data zayyana masa na kalar zaman da takeyi da Abban se yaji ashe ko rabi Hajiya bata sani ba, ta bashi tausayi matuƙa duk son zuciyar Hajiya nata suka ja mata, samarin Arziƙi tayi su amma ita da uwarta suka raina musu Ajawali, shi shafaffe da mai da yayi daidai da ra'ayinsu gashi nan tun ba'aje ko ina ba tana kuka da data sanin auransa, gara Hajiya raba baƙin cikin akeyi da ita, ita da take zaune dashi take kwasar kashinta a hannu ita take da abin faɗa. Daya tariyo gidan Naziru, da matarsa ta rufin asiri gashi nan ya tattago matar Jaraba irin wadda Hajiyar take so shi kuma tana gasa masa Aya a hannu, Yakubu ma dai sammakal wata yar gidan da Tarbiyya bata wadata ba ya kwaso yar masu kuɗi yan boko ranar nan yana ji suka kwaso rigima wai bata iya sallah ba daga ya mata magana yace a gidan ba'a sakata Islamiyyah ba ta kira Babanta tana kuka tace ya zage shi tas yace musu kafirai uban yazo yayi tijara a tsakar gidan Alhaji Audu akayi sa'a dai baya nan Hajiyar ce ta fita tana bashi haƙuri duk suna ɗaki suka ƙi fita to irin auran da take so yayi shima kenan.

Bayan ya dawo ya ciza ya busa yaga dai shawarar Hajiya Ummu wadda kuma daman usulun abinda zuciyarsa ta ayyana masa kenan a matsayin mafita tilas ya aiwatar da hakan shine yaje ya samu Baba Alƙali ɗazun ya zayyane masa komai yace kuma ya kwantar da hankaliynsa ya tambayeshi ina ne gidansu yarinyar yace zeje yau ya karɓo full Address da sunan Mahaifinta akan haka suka rabu. Dalilinsa na ɓoyewa Ahmad komai akanta kuma kawai yana jin nauyin abubuwan daya masa akan Fatima, irin izgilancin daya masa na cewar ya rasa Macen da zeso a duniya se yar bakanike, duk matan da suke sonsa isassu bega matar aure ba se ita abin haushin ma tana wahalar dashi se gashi shima ya Ƙare da faɗawa tarkon yar Talaka liƙis da yake ganin kamar ma Mahaifin Fatiman Yah Ahmad ɗin zefi nata wadata, wannan tasa ya yanke hukuncin su tafi tare, yaga komai da idonsa idan yaso daga baya su tattauna domin yasan Yah Ahmad bazeyi judging nasa ba kamar yanda shi ya masa

Ashe shine babban gara a cikin wasan, shi yar bakanike ta ɗanawa mugun tarko ta kamashi kuma yanda ya kamata tayi wasa da hankalinsa. Abubuwa da yawa ne cikin al'amarin, ze tabbatar da Allah ne ya kama Hajiyarsa dashi kansa dumu dumu, rainin arziƙin da yayi musu ubangiji ya tabbatar masa da ba nan take ba, ba rashin wayon Ahmad bane ya saka soyayyarta tayi galaba akansa haka duk izza da jiji da kansa gashi nan ta haushi ta tattakeshi son ranta sannan Tozarcin da Hajiyarsa ta so yiwa Ahmad ne yayi waiwayi ya diro akansa, ina zata tsoma ranta da wannan abin kunyar idan taji labarin yar bakaniken data rainawa Ajawali tayi wasa da Zuciya da Ƙwaƙwalwar Jay da take ganin kaf zuri'ar Audu Bechi babu yashi?.
Chapter 63 · 0% Book details