← Book details Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 71

Sashe 26

Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Kar dai fa Aljanin darene yazo mata? Mutumin data haɗu dashi jiya kwana tayi tana mafarki dashi kuma ta tashi cikin wannan yanayin karfa da gaske Aljanine? kai Innalillahi taga ta kanta ita Afeeya ina ta kwaso Aljanu ta shiga uku" ta raya a zuciyata kafin ta sake yunƙurawa tana tattare rigarta a ranta ta Ƙudurce tana yin sallah zata kira Ummanta ta faɗa mata tun wuri, bata taɓa irin mafarkin ba se yau gara ta faɗa mata koma menene a tareshi tun kafin ya aureta ta shiga uku.

Seda na sauka daga gadon ta kalli shimfiɗar stain ɗin jini da ta gani ya sakata sakin ƙaffaffar ajiyar zuciya saboda ganin wani abu daban ba yanda tayi tunani ba. Towel ta ɗauka ta wuce wanka da Ruwan Badar tana jin tana zaginta amma ban tanka ba. Seda ta kintsa kainta kafin ta cire bedsheet din ta kama inda ya baci ta wanke a baza daman yau zasu haɗa wanki, takwas saura suka fita class bayan sun karya har sannan kuma jikinta a sanyaye yake idan na tuna mafarkin jiyan se taji Zuciyarta ta buga kuma wani abun mamaki sukayi waya da Umma da Baffa amma ta kasa faɗa mata kamar yanda tayi niyya, abin ne da nauyi kawai Anty Sauda zata kira to ta faɗa mata.

A Ajin ma bata da wani kuzari da kuzari Malamin da kansa seda ya tambayeta lafiya take tace kanta ne yake ciwo. Malamin na fita Class Rep É—insu ya tsallaka sit É—in da suke, ta kwantar da kanta a kan Desk suka gaisa da Badar da Yusuf ta harari Sahid dan basa shiri kafin ya kalleta yace
"Whitey (haka yan class É—in suke kiranta ko Afee whitey saboda haskenta) I have been looking for you since yesterday"

Ba tare data É—ago ba tace masa
"Ya akayi?" Dan Sahid akwai dan banzan surutu shima da gulmar tsiya
"Wani mutumi ne, I mean one guy asked me about you yesterday and i told him every detail i know har layinki na bashi, Afee you don do good catch i swear, from his looks gayen nan is Rich, his face looks familiar to me but i couldn't figure out inda na sanshi" Sahid ya fada. Badar ta harareshi tace
"Haka ka iya kai dai ka zama kamar wani kawali kullum cikin haÉ—a yammata da Samari", hausar bata bawai yana jinta dakyau bane Banufe ne dan haka ya kalli Yusuf da suke tare yace

"What is Kalali? Because i know Badariyya, when ever she speak big big Hausa word she is up to no good" dukda yanda nake jina amma seda nayi dariyar maganarsa Yusuf yace
"Tana nufin you are a good match maker"
"Ehen" Sahid din ya sake fada da alamar be yadda da abinda ya fada ba amma se ya maida hankali kaina yana cewa
"He gave 100$"
"Kaji daɗi" Afeeya ta faɗa tana miƙewa saboda cikinta daya hautsina, tsallakesu tayi ta fita da sauri can gurin fanfo tana zuwa ta shiga sheƙa Amai masu wucewa suna binta da sannu. Kamar ta kunno ciwo tana gama aman marata ta riƙe ita da bata Mp se gashi ta gagara tashi tsaye daga gurin seda Badar tazo ta ɗagata.

"Muje Hostel kawai daman baki da lafiya amma kika fito?" ta faɗa suna tafiya a hankali. Yusuf ne ya kaisu har gaban Amina a motarsa kafin suje ta galabaita juye juye kawai take a cikin motar na azaba dakyar ta iya fita ai kuwa nan gurin Security ta kwanta tana kuka shaɓe shaɓe kamar wadda zata haihu, abinda bata sababa, bata taɓa experiencing ciwon Mara ba se lokacin shiyasa take jinsa wani sabon abu kamar zata maɗe.
aka daka saboda ciwo.

"Sannu Afeeya me yake damunta?" Anty Amina daya daga cikin matan security da mmsuke mutunchi dasu ta tambayi Badar,
"Inaga zazzaɓi ne" Badar ta bata amsa Afeeya ta nuna musu mararta da hannu, cikin tausayawa Anty Aminan tace
"Wayyo sannu, daure ku ƙara ciki se kisha ruwan zafi da pain relief, Allah ya kawo Afuwa"

"Kuje kuyi aure yara kun zauna kuna fama da ciwo" Ɗaya matar ta ɓaro maganar, Badar ta Anty Amina suka kamata ganin an fara taruwa akana kallonta wasu na cewa Aljanu takeyi. A common room suka ajiyeta ta kasa zama kan kujera se a ƙasa ta kwanta tana cigaba da murƙususu, ashe haka Matan suke ji amma ta ringa cewa Bafar raguwa idan tana ciwon Mara yau gashi Allah ya kamata itama kamar fa an hura mata wuta takeji a gurin wannan abu da akwai Azaba.

Ta fi awa a gurin kafin ciwon ya lafa mata lokacin har gashin kanta seda ya hargitse kamar wadda tayi naƙuda. A duddƙe ta ringa tafiya har sukaje ɗaki, duk wanda Badar ta gayawa abinda yake damunta se yayi dariya kafin ya mata sannu dan haka take musu. Sururat ta haɗa mata ruwa me zafi takai mun banɗaki kafin ta fito Badar ta haɗa mata shayi me kauri ta gyara mata gado, kamar wata sarauniya haka suke lelenta suna mata iskanci kuma, tasha Paracetamol ta kwanta bacci ya kwasheta wata Jalalar Mutumin ya sake diro mata a mafarki amma ba irin na daren jiya ba.

Na daÉ—e sosai tana bacci har gurin qarfe biyun rana kafin ta farka ta ji daÉ—in jikinta se abinda ba'a rasa ba. Kamar me ciki ta seda ta sakeyin Amai kafin tayi tsarki da ruwa me dumi sosai ta canza pad ta koma É—aki tana tafiya salaf salaf kamar waddata fito daga Labour room.

"Abin nema ya samu" Ummi ta faÉ—a ta harareta kafin ta zauna kan Gadon Maman Minal tana cewa
"Tun jiya Ummi daga zuwa Lecture baki kwana a nan ba?"
"Bayan na fito daga lectures ne na hadu da Surayya shine kawai na bita City tunda yau banida lecture, yanzu ma motar bati na samu shiyasa na taho da wuri" Ummin ta bata amsa kan tabi Cousin É—inta city gidan Antynta.

Afeeya ta kalleta badan ta yarda Zaria City tasan baze wuce yawonta na banza ta tafi ba. Ummi bataji ko kadan, ta santa tare sue a English da zasu shiga Level 3 É—in nan ta bari ta koma Library science saboda rashin mayar da hankali ana nema a koreta, party da clubbing a Zaria babu inda bata sani ba yanzun a hakan ma ta rage ne zama dasu suna matseta dole ta rage wasu abubuwan da wuya ta fita ta kwana a waje duk yawonta zata dawo Hostel.

"Wlh gidan su Surayya naje idan ma baki yarda na kirata yanzu kiji da kunnenki" ta katsewa Afeeya shirun da tayi dason wanke kanta. Wayar Afeeya ta fara ringing akan gado ta É—akkota tana cewa
"To me kikaji nace Ummi? Duk ma abinda mutum yayi ai dan kansa me kyau ko mara kyau zaka tarar da sakamakonka me sonka ne yake damuwa da abinda kakeyi har yake so ka hau hanyar daidai". Ahmad ne yake kiran kafin ta answer ta ktase se lokacin taga missed call daya mata kafin wannan kiran.

Wani kiran ya sake shigowa, ta É—aga yana narke murya dan bata so wayar tayi nisa.
"Fatima kin tashi? Ya jikin?" Ya faÉ—a cikin kulawa, ta kwanta tana cewa
"Da sauƙi, ka kira aka ce ina bacci ne?"
"No, dana kira baki É—aga ba i called Badar ita ta gaya mun bakya jin dadi ta barki kina bacci i hope you are feeling better now? Kodai zakuje hospital ne kira Ilyas ya kaiku?" Ya sake tambayata a tausashe, a maimakon taji daÉ—in kulawar tasa ma haushi yake bata ya fiya sanyi da yawa ta muskuta tana cewa
"Nafa samu sauƙi kuma nasha magani, Ilyas na zata ya bar Zaria ai"
"No yana nan be samu sun canza masa din ba so kuma ma saura two months ya gama shiyasa ya haƙura" (cousin ɗinsa ne yaron sister Momy da yake Internship a Shika Asibiti).

"Ayya Allah ya bada sa'a, ya kake? Abujan? Yaushe zaka dawo?"
"Are you missing me?" Ya faÉ—a yana sakin murmushi najin daÉ—i yau Fatima ta tambayeshi wani abu daya shafeshi, kunya ta kamata tayi murmushin ita ma amma bata ce komai ba yaci gaba da cewa
"Se Thursday In sha Allah, kina zumuÉ—in ki ganni ne?"

"Uhm" kawai tace, cikin tsokana yace mata
"Da gobe fa zan taho, sena haɗu da wata yar farar Yarinya me irin zubinki, ita take so ta riƙeni na kasa tahowa".

Ba wani son sa take ba ba amma se da zuciyarta ta sosu da abinda ya faɗa kishi ya taso mata, a ƙufule tace
"Kace kayi budurwa yar Abuja yar gidan masu kuɗi" yanda tayi maganar ita kantaseda ta idar ta fahimci muryar da tayi amfani da ita tayi kauri da yawa ta kuma bayyana kishin daya taso mata ƙarara. Dariya sosai Ahmad yayi tayi shiru kunya da takaicin kanta suka rufeta, seda yayi me isarsa kafin yace
"Ashe dai Fatima na kishina haka? Gaskiya naji daÉ—i".

Bata sake ce masa komai ba ya gama surutansa tana ji ganin ta ƙi bashi amsa yasa ya canza akalar maganar da cewa
"Haka kawai Tuwo nake sha'awar ci da Miyar Kuka, kamar na tafi Kano yau ma nake ji"

"Ikon Allah Tuwo kuma ka rasa wacce miya seta kuka?" Ta faɗa cikin mamaki dan zata iya cewa a matasa dai shine mutum na farko data taɓajin yana son Miyar kuka, Yah Malam dinsu cewa yayi ganyen bishiyar Aljanu ne tsaɓar hatsabibanci irin na mata suka mayar dashi abinci shiyasa duk me yawan cinsa kwakwalwarsa toshewa take saboda sharri.

"Kuka dai da kika sani, ni ai idan kina so ki burgeni to ki bani abincin gargajiya amma fa with a touch of modernity bawai kuma ayi abu babu sha'awa ba, irinsu dambu, Akubus, Fate, ÆŠanwake babu wanda bana ci kuma a kowanne lokaci zan iya ci be it safe, rana dare duk zan iya cinsu musamman idan an shiryashi ya dace da lokacin".
Chapter 26 · 0% Book details