Sashe 69
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Anty Saudan dai ta sake shaida mata Ranar Juma'a yan gidansu Ahmad zasu zo, Ranar kwana tayi tana kuka har wani zazzaɓine ya sake saukar mata ta ringa sake gwada kiran Jay da tura masa saƙonni ta kowacce kafa da ta san tana samunsa a baya amma a banza kamar me aikawa lahira. Sanda ta samu saƙon sunje har an tsayar da maganar auransu watanni shida masu zuwa kusan suma tayi dan a tsaye take ta sulale ta zauna seda aka jijjigata kafin ta farka daga suman zaunen ta kuma fasa musu kukan da tun suna bata baki da tambayar meya faru har kowa ya gaji ya rabu da ita, Maman Minal ce ta kira Anty Sauda dan taji ko mutuwa akayi a gida akan sanar mata, bata fiya zafi ba amma ranar seda ta warwarwa Afeeyah tayi mata tatas wai dan ma Badar bata nan ta tafi Kd dan har sannan Jikin Babansu se a hankali an dawo dashi dai amma duk weekend a gida takeyi Friday basa komai ranar take tafiya ta dawo Sunday bata ma san da zancen kawo kuɗin ba yanda Afeeyar bata gaya mata ba itama yanzu ta dena damun kanta da matsalarta, ta dai gaya mata yanda suke ciki da Jay ta kuma jimanta mata ta sake nusashsheta abinda ake mata hasashe kenan sanda suke ce mata karta saki jiki dashi shikenan ta kama kanta ta rabu da ita tunda bata ga alamun zata hankalta ta gane Allah guda bane domin har sannan cewa take Ahmad ne ya janyo mata zuwansa ne ranar ya ruguza komai.
Sati tsakanin zuwarwa Ahmad tambaya akaje na Jay, a bazata batun ya zowa kowa harda Ahmad da ita kanta Hajiyar seda aka saka ranar zuwa taji labari a bakin Alhaji Zakariyyah, data zabura zatayi bala'i se kuma tayi laƙwas kamar Tarwaɗa taji gishiri ta shiga zare idi dajin Yar wacce za'aje tambayowa Jay auranta. Se gani kawai Alhaji Zakariyyah yayi ta fashe da kuka, a zatonsa kukan bata sani bane kamar yanda ta tasammayin tijara a farko seda yaji tana cewa
"Ashe dai burina ze cika, Jafaru ze farantamun ya wanke mun takaicina Allah na gode maka kace dai ya gidan gwaunan bankin Najeriya ce ko ubana?" Zakariyyah murmushi kawai yayi dan yanda Hajiyar ta keyi kamar wata yarinya, daya tana neman ta ishe shi da tambayoyi ya fice ya barta ta shiga bige bigen waya tana sanarwa su Turai abin Arziƙin daya samesu. Ahmad kuwa Baba Alƙali ne ya kirashi yace ya shirya zasuje Abuja neman auran Jay, yayi mamaki, ko awa guda basu cika da gama magana da Jay ba amma beyi mentioning masa zancen auran ba koda yake duk Jay ɗin ya canza ya kuma kasa gane kansa balle abinda yake damunsa. Daya samu labarin shiru yayi be ce masa komai ba, a ransa yayi murna zasuyi aure lokaci ɗaya kamar yanda birinsu yake tun suna yara.
Juma'a Baba Alƙalin yace zasu tafi su kwana a can Asabar idan sun gama abinda ya kaisu su juyo a ranar shi kuma yayi niyyar tafiya Zaria gurin Fatima wadda tun bayan Baikonsu Al'amura suka fara sauyawa a tsakaninsu, a yanzu base ya kirata ba takan kirashi da kanta dukda dai babu sakewa ko soyayyar da yake fatan samu daga gareta amma a hakan shi ji yake kamar yafi kowa farin ciki ba kuma shi da wata damuwa dan haka ya kirata ya sanar mata da baze samu damar zuwa ba zasuje Abuja neman ma Jafar Aure, bata nuna taji ba balle ya saka ran zata sakawa lamarin Albarka. Ita kuwa sunan Jafar daya ambata mata tamkar fami ya zamar mata kan nata Jafar ɗin da har yau bata dena kukan rasa shi ba, dangana tayi ta ta kuma buɗe zuciyarta ta fahimci abinda aka daɗe ana nusashsheta amma ta doɗe zuciyarta da idanunta taƙi fahimta a yanzu ne ta ke godewa Allah domin nacin Ahmad ya mata rana domin da ace ya barta tamkar Jafar bata san wa zata kama ba.
Ita da kanta ta yarda haɗuwarta da Jafar da soyayyarsu har zuwa rabuwarsu haƙƙin Ahmad ne, ta godewa Allah daya bata damar gane kurenta harya yasa tana da sauran lokacin da zata iya gyarawa, sedai aka ce So ɗayane, har yau har gobe tana son Jay, bata sani ba ko se ranar data tabbatar da ta zama mallakin waninsa sannan zatayi jana'izar soyayyarsa ta binneta badan ta mutu ba.
Baba Alƙali, Alhaji Babangida, Alhaji Abdullahi, Zakariyyah Bechi, Naziru Bechi, da Ahmad Bechi da se Aminan Alhaji Audu na ƙut da ƙut Alhaji Mu'azzamu da Alhaji Aliko sukaje neman auran saɓanin na Ahmad da Baba Alƙalin ne tareda Alhaji Abdullahi sukaje, ya sanarwa Alhaji Babangida lokacin ya bashi uzurin ranar ze tafi Umarah dalilin daya saka ba'aje dashi ba. Harka akayita girma, aure ake shirin yi irin wanda ake kira ƙwarya tabi ƙwarya. Shima kamar Ahmad watanni shida aka saka, suka dawo Kano niƙi niƙi da kayan arziƙin da aka haɗo su dashi. Hajiya bata iya bacci ba, tun daren Juma'a take dokawa Naziru kira daya gaji da amsa ma yayi restricting number, yanda kasan zatayi tsuntsuwa ta tafi can haka tayi ta kasa zaune ta kasa tsaye har seda suka dawo abubuwan da suka zo dasu suka gigitata haka ta fita tsakar gida tana taka rawar murna tareda sakin habaici wa Momy da ko biskit ba'a kawo mata daga gidan Surukan Ahmad ba sanda akaje neman aure sun dai kawo tukucin naira dubu hamsin wadda aka cire musu daga dubu ɗari biyar da suka kai kuɗin aure da saka rana. Shima Jay ɗari biyar ɗin aka kai dukda Hajiya tace tayi kaɗan Baba Alƙali dashi ya bada kuɗin daman yace haka yayi niyya kuma baya isa ta saka a ƙara ba ko Zinariya ze auro.
Bayan sun dawo Ahmad ya kirashi murya a sake sam be riƙi cewar Jay ya zame shi daga abubuwa da yawa da suka shafi rayuwarsa a yanzu ba ya shiga tsokanarsa da Ango Ango. Seda suka gama barkwanci kafin yace masa
"Amma fa na É—anji babu daÉ—i, ni ya kamata nayi breaking news na auranka bawai naji labari daga sama ba, amma ya wuce ,I'm happy for you, I'm happy for us, at long last mun kusa mallakar muradan zuciyarmu"
"Ka kusa mallakar muradin zuciyoyinmu nida kai dai" Jaya ya raya a ransa a fili kuma ya marairaice yace masa
"Kunya nakeji, bansan taya zan gaya maka ba". Dariyar da Ahmad ya ringayi har seda ya sauka daga kan kujerar Momy da yake zaune, seda yayi me isarsa kafin yace
"Amma bakaji kunyar kanka ba da kake faÉ—ar wannan maganar? Ni zakace kana jin kunya ba zaka iya gaya mun za'aje neman maka aure ba? Ai shikenan amma ko na ji tausayin Afeeyah ne sunanta ko? Allah kaÉ—ai yasan yanda zataji idan labarin nan ya iske ta".
A fusace Jay yace
"Allah yasa ya zama silar Ajalinta ma kowa ya huta Annamimiya me fuska biyu munafuka kawai"
"Jafar me yake damunka? Me yasa baka da magana seta fatanma wani mutuwa haka kawai san kana da matsala dashi? Babu kyau tsananta Ƙiyayya, ina jiye maka tsoron kar a jarabceka da abinda kafi ƙi a rayuwarka wlh seka gwammaci kida da karatu" Ahmad ya faɗa in a serious tune se Jay yace
"Na nawa kuma? Jarabta ai an mun sedai nayi addu'ar Allah ya bani ikon cinyeta kawai amma batun wai wani waye tuni an wuce gurin"
"To karkayi saɓo Malam nikam se anjima, daga kira muyi farin ciki kar ka jawo abinda rayukanmu zasu ɓaci, haba, kanka aka fara kasa Namiji a neman aure da zaka ɗauki abu da zafi ka hana rayuwarka sakat? Duk ka canza daga Happy Jay ka koma wani Aggressive person akan me? Ita rayuwa daman ai tilas akwai samu akwai rashi ba kuma dole duk abinda mutum yaso ace ya same shi ba. Nasan zafin So amma idan ka kasance me neman zaɓi da yardar Ubangiji cikin dukkan lamuranka koda zakayi fushi da wani abu daya sameka a rayuwa ya zama na ɗan lokaci, Allah ya fika sanin dalilin daya saka ya hakana samun wannan abun naci da dagiyarka se ta janyo maka abinda zaka zo kana dana sani da nadama mara amfani a rayuwarka se Allah ya barka da abin yaga iyakar gudun ruwanka. Ga rabonka nan ka dace da ita, kayi addu'a Allah yasa ta zamo maka sanyin idaniya macen da kowanne Namiji yake fatan samu"
Da "In sha Allah" Jay ya amsa masa shikenan aka gama wayar saboda ya sake goga masa gishiri akan rauni. Tun haɗuwarsa da Afeeyah yake hasaso yanda wannan ranar zata kasance musu, ranar da za'ace yarjejeniyar aure ta Ƙullu tsakaninsu, yaci burin zuwan lokacin har party yace ze shirya se gashi tazo masa da wacce be taɓa koda hasaso zata zama matarsa ba. Gaba ɗaya ma yanda abubuwa suke faruwa shi baze ce ga shi ba kawai dai komai yana faruwa ne tamkar shirin film kamar wasa yanzu an tasarma zuwa No going back stage
"Ya rayuwarsa zata kasance da watan Afeeyah???" Tambayar da ke kara kaina cikin zuciyarsa.
Shirin biki ya kankama a gidan Alhaji Audu Bechi. Shiri akeyi tamkar a wannan karon ne za'a fara aurar da ÆŠa a cikin gidan dukda shirin tsakanin Yayan cikin gida ne na waje dai nasu ido. Hajiya Binta tamkar zata haukacw saboda yanda ta azawa kanta tashin hankali akan wannan aure da Jay zeyi, Turai da Hajiya Zainab ne kan gaba akan shirin Komai, su suke haÉ—a Lefe, kuÉ—aÉ—e masu nauyin gaske ya aika musu na haÉ—a lefen. Me hali baya fasa abinsa, duk irin zumuÉ—i da zirgillin da Hajiya takeyi akan shirin Bikin da aka zo batun haÉ—a lefe taga uban kuÉ—aÉ—en da ake narkawa domin Turai tsakani da Allah ta tsaya take abun nan Hajiya ta rikice tace bata san zance ba ta yaya za'aje ana siyan Lesuna na dubu dari biyar zuwa sama ai Almubazzaranci ne.
Sati tsakanin zuwarwa Ahmad tambaya akaje na Jay, a bazata batun ya zowa kowa harda Ahmad da ita kanta Hajiyar seda aka saka ranar zuwa taji labari a bakin Alhaji Zakariyyah, data zabura zatayi bala'i se kuma tayi laƙwas kamar Tarwaɗa taji gishiri ta shiga zare idi dajin Yar wacce za'aje tambayowa Jay auranta. Se gani kawai Alhaji Zakariyyah yayi ta fashe da kuka, a zatonsa kukan bata sani bane kamar yanda ta tasammayin tijara a farko seda yaji tana cewa
"Ashe dai burina ze cika, Jafaru ze farantamun ya wanke mun takaicina Allah na gode maka kace dai ya gidan gwaunan bankin Najeriya ce ko ubana?" Zakariyyah murmushi kawai yayi dan yanda Hajiyar ta keyi kamar wata yarinya, daya tana neman ta ishe shi da tambayoyi ya fice ya barta ta shiga bige bigen waya tana sanarwa su Turai abin Arziƙin daya samesu. Ahmad kuwa Baba Alƙali ne ya kirashi yace ya shirya zasuje Abuja neman auran Jay, yayi mamaki, ko awa guda basu cika da gama magana da Jay ba amma beyi mentioning masa zancen auran ba koda yake duk Jay ɗin ya canza ya kuma kasa gane kansa balle abinda yake damunsa. Daya samu labarin shiru yayi be ce masa komai ba, a ransa yayi murna zasuyi aure lokaci ɗaya kamar yanda birinsu yake tun suna yara.
Juma'a Baba Alƙalin yace zasu tafi su kwana a can Asabar idan sun gama abinda ya kaisu su juyo a ranar shi kuma yayi niyyar tafiya Zaria gurin Fatima wadda tun bayan Baikonsu Al'amura suka fara sauyawa a tsakaninsu, a yanzu base ya kirata ba takan kirashi da kanta dukda dai babu sakewa ko soyayyar da yake fatan samu daga gareta amma a hakan shi ji yake kamar yafi kowa farin ciki ba kuma shi da wata damuwa dan haka ya kirata ya sanar mata da baze samu damar zuwa ba zasuje Abuja neman ma Jafar Aure, bata nuna taji ba balle ya saka ran zata sakawa lamarin Albarka. Ita kuwa sunan Jafar daya ambata mata tamkar fami ya zamar mata kan nata Jafar ɗin da har yau bata dena kukan rasa shi ba, dangana tayi ta ta kuma buɗe zuciyarta ta fahimci abinda aka daɗe ana nusashsheta amma ta doɗe zuciyarta da idanunta taƙi fahimta a yanzu ne ta ke godewa Allah domin nacin Ahmad ya mata rana domin da ace ya barta tamkar Jafar bata san wa zata kama ba.
Ita da kanta ta yarda haɗuwarta da Jafar da soyayyarsu har zuwa rabuwarsu haƙƙin Ahmad ne, ta godewa Allah daya bata damar gane kurenta harya yasa tana da sauran lokacin da zata iya gyarawa, sedai aka ce So ɗayane, har yau har gobe tana son Jay, bata sani ba ko se ranar data tabbatar da ta zama mallakin waninsa sannan zatayi jana'izar soyayyarsa ta binneta badan ta mutu ba.
Baba Alƙali, Alhaji Babangida, Alhaji Abdullahi, Zakariyyah Bechi, Naziru Bechi, da Ahmad Bechi da se Aminan Alhaji Audu na ƙut da ƙut Alhaji Mu'azzamu da Alhaji Aliko sukaje neman auran saɓanin na Ahmad da Baba Alƙalin ne tareda Alhaji Abdullahi sukaje, ya sanarwa Alhaji Babangida lokacin ya bashi uzurin ranar ze tafi Umarah dalilin daya saka ba'aje dashi ba. Harka akayita girma, aure ake shirin yi irin wanda ake kira ƙwarya tabi ƙwarya. Shima kamar Ahmad watanni shida aka saka, suka dawo Kano niƙi niƙi da kayan arziƙin da aka haɗo su dashi. Hajiya bata iya bacci ba, tun daren Juma'a take dokawa Naziru kira daya gaji da amsa ma yayi restricting number, yanda kasan zatayi tsuntsuwa ta tafi can haka tayi ta kasa zaune ta kasa tsaye har seda suka dawo abubuwan da suka zo dasu suka gigitata haka ta fita tsakar gida tana taka rawar murna tareda sakin habaici wa Momy da ko biskit ba'a kawo mata daga gidan Surukan Ahmad ba sanda akaje neman aure sun dai kawo tukucin naira dubu hamsin wadda aka cire musu daga dubu ɗari biyar da suka kai kuɗin aure da saka rana. Shima Jay ɗari biyar ɗin aka kai dukda Hajiya tace tayi kaɗan Baba Alƙali dashi ya bada kuɗin daman yace haka yayi niyya kuma baya isa ta saka a ƙara ba ko Zinariya ze auro.
Bayan sun dawo Ahmad ya kirashi murya a sake sam be riƙi cewar Jay ya zame shi daga abubuwa da yawa da suka shafi rayuwarsa a yanzu ba ya shiga tsokanarsa da Ango Ango. Seda suka gama barkwanci kafin yace masa
"Amma fa na É—anji babu daÉ—i, ni ya kamata nayi breaking news na auranka bawai naji labari daga sama ba, amma ya wuce ,I'm happy for you, I'm happy for us, at long last mun kusa mallakar muradan zuciyarmu"
"Ka kusa mallakar muradin zuciyoyinmu nida kai dai" Jaya ya raya a ransa a fili kuma ya marairaice yace masa
"Kunya nakeji, bansan taya zan gaya maka ba". Dariyar da Ahmad ya ringayi har seda ya sauka daga kan kujerar Momy da yake zaune, seda yayi me isarsa kafin yace
"Amma bakaji kunyar kanka ba da kake faÉ—ar wannan maganar? Ni zakace kana jin kunya ba zaka iya gaya mun za'aje neman maka aure ba? Ai shikenan amma ko na ji tausayin Afeeyah ne sunanta ko? Allah kaÉ—ai yasan yanda zataji idan labarin nan ya iske ta".
A fusace Jay yace
"Allah yasa ya zama silar Ajalinta ma kowa ya huta Annamimiya me fuska biyu munafuka kawai"
"Jafar me yake damunka? Me yasa baka da magana seta fatanma wani mutuwa haka kawai san kana da matsala dashi? Babu kyau tsananta Ƙiyayya, ina jiye maka tsoron kar a jarabceka da abinda kafi ƙi a rayuwarka wlh seka gwammaci kida da karatu" Ahmad ya faɗa in a serious tune se Jay yace
"Na nawa kuma? Jarabta ai an mun sedai nayi addu'ar Allah ya bani ikon cinyeta kawai amma batun wai wani waye tuni an wuce gurin"
"To karkayi saɓo Malam nikam se anjima, daga kira muyi farin ciki kar ka jawo abinda rayukanmu zasu ɓaci, haba, kanka aka fara kasa Namiji a neman aure da zaka ɗauki abu da zafi ka hana rayuwarka sakat? Duk ka canza daga Happy Jay ka koma wani Aggressive person akan me? Ita rayuwa daman ai tilas akwai samu akwai rashi ba kuma dole duk abinda mutum yaso ace ya same shi ba. Nasan zafin So amma idan ka kasance me neman zaɓi da yardar Ubangiji cikin dukkan lamuranka koda zakayi fushi da wani abu daya sameka a rayuwa ya zama na ɗan lokaci, Allah ya fika sanin dalilin daya saka ya hakana samun wannan abun naci da dagiyarka se ta janyo maka abinda zaka zo kana dana sani da nadama mara amfani a rayuwarka se Allah ya barka da abin yaga iyakar gudun ruwanka. Ga rabonka nan ka dace da ita, kayi addu'a Allah yasa ta zamo maka sanyin idaniya macen da kowanne Namiji yake fatan samu"
Da "In sha Allah" Jay ya amsa masa shikenan aka gama wayar saboda ya sake goga masa gishiri akan rauni. Tun haɗuwarsa da Afeeyah yake hasaso yanda wannan ranar zata kasance musu, ranar da za'ace yarjejeniyar aure ta Ƙullu tsakaninsu, yaci burin zuwan lokacin har party yace ze shirya se gashi tazo masa da wacce be taɓa koda hasaso zata zama matarsa ba. Gaba ɗaya ma yanda abubuwa suke faruwa shi baze ce ga shi ba kawai dai komai yana faruwa ne tamkar shirin film kamar wasa yanzu an tasarma zuwa No going back stage
"Ya rayuwarsa zata kasance da watan Afeeyah???" Tambayar da ke kara kaina cikin zuciyarsa.
Shirin biki ya kankama a gidan Alhaji Audu Bechi. Shiri akeyi tamkar a wannan karon ne za'a fara aurar da ÆŠa a cikin gidan dukda shirin tsakanin Yayan cikin gida ne na waje dai nasu ido. Hajiya Binta tamkar zata haukacw saboda yanda ta azawa kanta tashin hankali akan wannan aure da Jay zeyi, Turai da Hajiya Zainab ne kan gaba akan shirin Komai, su suke haÉ—a Lefe, kuÉ—aÉ—e masu nauyin gaske ya aika musu na haÉ—a lefen. Me hali baya fasa abinsa, duk irin zumuÉ—i da zirgillin da Hajiya takeyi akan shirin Bikin da aka zo batun haÉ—a lefe taga uban kuÉ—aÉ—en da ake narkawa domin Turai tsakani da Allah ta tsaya take abun nan Hajiya ta rikice tace bata san zance ba ta yaya za'aje ana siyan Lesuna na dubu dari biyar zuwa sama ai Almubazzaranci ne.