← Book details Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 71

Sashe 28

Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Saboda ta tabbatar musu maganar ta wuce yasa washe gari suna gama Lectures tacewa Badar suje kasuwa ayi cefanen, ta kuwa ji daÉ—i sosai dan da sunta share juna amma daga zuwa kasuwar komai ya wuce aka dawo daidai
Harda kayan zoɓo suka siyo, sesaga baya kuma Badar tace su siya Kunun Ayar Shinkafi kawai ba se anyi Zoɓon ba.

"Bari na kira Salima Nasir ta zo manada snacks gobe se a hada masa ko?" Badar ta sake faɗa. Dole Afeeya ta amsa gudun karta ƙara laifi a gurin Badar data saki ranta dalilin za'ayiwa Ƙanin Dadynta girki. Sunyi markaɗen stwe a Kasuwa dan haka suna komawa suka ɗora girki suna hira kamar ba abinda ya faru jiya.

Washe gari haka Afeeya ta tuƙa tuwon rabin kwano tayi miyar kukar da Ƙamshinta ya karaɗe duka block ɗinsu ya buwayi hancin kowa. A Set din food flask da suka ɗakko da safe a gidan Maman Minal ta saka masa tuwon Miyar aka barta a tukunya akan seya zo se a sake dumamawa a zuba a flask din. Kayan da zan saka ko Badar ta turarasu ya kai sau uku, jikinta har rawa yake idan Ahmad zezo musamman wannan karon, sunyi waya da Afeeya ya gaya mata be taso da wuri na ze kai zuwa uku kafin ya sauka dan haka zuwa biyu ta gama komai tayi wanka suka zauna suna ta labarai. Biyu da rabi ya kirata akan ya shigo zaria.

"Na gaji da yawa ni nayi driving zan wuce nayi Lodging hotel idan na huta da Magriba sena shigo kuma bani kaɗai bane tare muke da mutumin Badar" ya faɗa mata. Har zatace masa toh ta tuna da Tuwon data gama shan wahalar tuƙawa hannayenta duk sun sage tafin se radadi yake mata Allah ma yasa kar nayi kanta. Da shagwabar da bata san tayi ba tace masa
"Toh Abincin fa? Shima se da magribar zaka ci?"
"Wane Abinci?" Ya tambayeta cikin rashin fahimta se sannan ta tuna da bata gaya masa tayi masa tuwon ba dan haka tace
"Girki mukayi shine na É—ibar maka ko bazaka ciba?"
"Nidin banza, gani nan yanzu kuwa zanzo na karba kamar kinsan yunwa nakeji ko breakfast banyi dakyau ba saboda dokin son ganinki"
Guntun murmushi tayi kafin suka aje waya. Miyar aka sake É—umamawa Maman Minal tayi masa zubi me kyau duk ta kwashe Albarkatun cikin miyar ta bar musu saura. Hijabi ta É—akko cikin na *UMMU-MAHEER 07061838488)* wankakke gogagge ta É—ora akan doguwar rigar jikinta Badar ta kwaso Ashar ta watsamata ta haÉ—iye dan daman ta san se sunyi.

"Tsabar iskanci in gama shan wahalar turara miki kaya ki wani kwashi Hijabi kamar me takaba ki saka" ta faÉ—a a fusace tana neman fizge hijabin. Maman Minal tace
"Ki barta ai ze dawo anjima se tayi kwalliyar sannan".
"Masifaffiyar banza kawai" Afeeya ta faɗa Ƙasa ƙasa. Sururat ce ta tayata ɗaukan Basket da suka zuba abincin.

Kallon da bata so ya kafeta dashi tun daga corridor harta fita wajen hakan da yayi yasa hankulan mutane da yawa yayiwo kanta har suka Ƙarasa gabansa yana ta sakin murmushi kamar wani wawa.

Kallonsa tayi taga ya sake zama wani dan tsurut musamman daya saka ƙananan kaya se taga ma har tsakiyar kansa tana kallo tsanar sharri, murmushi tayi itama ta shiga gaishe su shida Abokinsa da kana ganinsa kaga Kanuri. Wani Baƙi dashi hausar ma se a hankali se surutu kamar ya ƙone a kai.

"Gaskiya Amaryarmu ba kalar rana bace, dan haka kodai ka nemi inuwa ku zauna ko kuma ka barta ta koma ciki an jima idan gari yayi sanyi seka dawo. Ni ganin basket É—in nan ma gaba É—aya ya sake tadomun da yunwa" Bukar ya faÉ—a ga surutu ga saurin baki.
Kanta na ƙasa tana wasa da zoben hannunta duk kallon da Ahmda ya kafeta dashi ya takurata,

"Bari muje Fatima anjima se na dawo bayan La'asar ko?" Ya faÉ—a cikin sigar tambaya ta É—aga masa kai ta ce
"Toh".
Abokin ne ya karɓi basket ya saka a mota Ahmad ya bishi ya ɗakko wata leda me tambarin super market dinsa BECHI STORES ya miƙa mata ta karɓa ta ɗan rusuna tace
"Nagode"
"Tsarabarki ce, tukuicin girki kuma se naci naji ÆŠanÉ—anon sa tukunna"

Murmushi tayi, ya langwaɓe kai ya jingina da mota yace
"Kamar karna tafi, kinyi kyau sosai Fatima Hijab suna miki kyau" Yaƙe kawai takeyi Abokinsa ya leƙo daga mota yace
"Kodai na zuba na fara ci ne in ba yanzu zamu tafi ba?"

"Kaga kun kwaso gajiya, kodan saboda dashi kuje Anjiman se ku dawo" ta faÉ—a, seya gyara tsayuwarsa yana cewa
"Naga hannunki"

Ƙirjinta ya buga, me ze gani a hannunta kuma? Amma haka ta daure ta miƙa masa hannun da daga wrist zuwa fingers ɗin ne a buɗe,
"Masha Allah ya faÉ—a" kafin ya juya yana É—aga mata hannu da cewar
Se ta dawo ita ma ta É—aga masa. Ta tsallaka ta shige hostel tana ta mamakin dalilin son ganin hannunta da yayi.
Tuwo ta tarar suna ci ta wanke hannu ta zauna, tunda ta gama taso taci jarabar Badar ta hanata wai bakinta zeyi warin daddawa se kace idan ta wanke baze fita ba. Seda suka qoshi Ƙat kafin a zazzage ledar tsarabar.

Wata Arniyar Turkish gown ce Material me sharashara Amma tana da landing Dark blue ce da flowers Yellow da fari da dan yarfin ja kadan. Irin design da ake sakawa roba a waist ta matse ta sama ƙasan kuma ya buɗe ce se mayafai Medium guda biyu plain da kana ganinsu kasan suma daga Turkey suke saboda samfurin jikinsu, takalmi loafers dark blue qafa daya se Wani kwali ƙarami na turarene babu suna a jiki hakan ya tabbatar mata da sabone basu luncher shi ba testing ya kawo mata kamar yanda ya saba tunda suka haɗu, Ahmad yanayin Designer perfumes kuma duk sanda sukayi sabon Turare kafin a fitar dashi seya kawo mata.

Company haÉ—in guiwa ne da wasu Abokanansa da sukayi karatu tare a Paris Asalin kamfanin yake amma a Dubai suke operating.

Tarkacen Chocolate na yan gayu birjik su su Badar suka ɗiba ragowar kayan ta watsa su a kan gado. Ahnad baya gajiyawa kullum cikin hidimta mata yake. Idan ya tashi siya mata kaya tamkar besan zafin kuɗi ba daidai da Slippers yanda yake saka Designer haka yake siya mata tun Baffa da Umma na faɗa har suka haƙura suka zuba masa ido kyautar Kuɗi ce dai Baffa ya dakatar shine yace idan an hanata karɓan kuɗi ai ba za'a hanata kaya ba dukda haka kuma idan zata koma school seya tura mata kuɗi masu nauyi sedai taji dirim.

Shida saura Ahmad ya kirata akan sun fito suna hanyar Samaru, bisa takurawar Badar Ummi tayi mata light make up ta cakare cikin Atamfa dinkin fitted straight Bubu, bata kamata tsam ba haka bata yi buhu ba tabi shape dinta ko ina ya fita masha Allah abinka da dogowar Mace na ta juya Anty Zahra tace
"Afee kinyi kyau, komai kika saka kyau yake miki".
Badar ce tayi mata É—auri me kyau daya dace da kwalliyarta

Seda aka idar da sallar magriba kafin ta fita dan bayan ya isa kirata yace ze shiga central mosque yayi sallah tukunna. Bata cika fita babu Hijabi ba infai ba Abaya ta saka ko irin Bubu plain Gown ba a hakan babu kwalliya gajiya takeyi da idanun mutane balle yau datayi shigar Atamfa harda kwalliya a fuskarta ga ɗaurin gaban goshi wani irin kyau tayi me sanyi da ƙayatarwa ba Maza ba hatta matan dake kaikawo a waje Hostel binta suka ringayi da kallo duk seta jita a takure shoyasa tafi gane ta suturta kanta da Hijabi Ko Abaya.

Yanda Ahmad ya saki baki yana yabon kyan da tayi ko har seda abin ya bata kunya ta sunkuyar dakai tana murmushi. Shi kaɗai ya dawo Abokin nasa wai ya shiga City, a nan Basket ball court suka zauna suna hirar duniya dan a itane take sakewa dashi suyi magana ko zancen Business dan tanada sha'awar kasuwanci sosai abinda ma zata ce ya a birgeta da Ahmad kenan Business mind set, a tsaye yake da ƙafafunsa kuma kullum cikin nuna mata amfanin neman na kai yakeyi. Yakan ce mata
"Ina so naga matata tana sana'a badan bazan wadata ta da komai na rayuwa ba Aa sedan ni na yarda da ko wani zeyi mun abu ya zamana nima inada abuna wanda zan kalla nace da gumi na na sameshi".

Seda aka kira yace ta kira su Badar su fita wannan daman constant ne duk sanda yazo seya fita dams yawo sun sha iska sunyi ciye ciye, tana kiranta minti goma suka fito duk a shirye harda Ruth suka zauna su huÉ—u a baya ita a gaba banda Maman Minal suka tafi Zaria Suya kamar yanda Badar tace can za'aje sunata hira da Ahmad har suka isa.

Sunci kifi sun sha shayi sunyi take away kaza da Suya amma banda Afeeya da idanun da Ahmad ya kafeta dasu suka hanata sakat. Yau se take ganin kamar tasan wani bayan shi me irin idon, amma ta gaza tuna waye.
PAGE 11

"Saura sati nawa kuyi hutu?" Ya tambayeta yana sake narkar da idanunsa a kanta. Ta lissafa a zuciyarta kafin tace
"Four weeks i think"
"Fatima" ya kira sunanta da sautin dake nuna muhimmancin maganar da zasuyi, ta gyara zamanta ta saci kallonsa yaci gaba da cewa
"Shekara biyu kenan since i meat you. Banyi zaton zan ƙara wata shida ba daga ranar dana haɗu dake ba tare da kin zama matata ba amma se gashi har an tafi shekaru which kece kika jawo hakan, please Fatima, i will ask you again ki aureni, last week na je na samu Baffa akan ina so na turo magabatana yace na nemi Amincewarki tukunna, idan kin yarda ko yaushe na shirya na tura ayi magana.
Chapter 28 · 0% Book details