Sashe 62
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wayar na mota"
Dan Allah muje Jafar na sani daman se munyi haka dakai kuma tunda muka zo nan dai ya kamata ka daure kawai mu ƙarasa yau ɗaya kaga Fatima na tabbatar duk wani grudges dake tsakaninku yau zaku warware shi muje please".
"Wannen ne gidan?" Jafar ya tambayeshi a ransa yana fatan ya nuna lungun daya miƙe yace a ciki gidansu Fatiman yake, kai shi da zata yuwu ma Ahmad yace makuwa yayi ba nan unguwar zasu zo ba saboda abubuwan da zuciyarsa take raya masa sunyi muni da yawa baya fatan ace hakan kuma ta zama gaskiya
"Wancan me Ash paint da baƙar Ƙofa daidai inda Solar take" Ahmad ya sake nuna masa gidan da kwatancen da duk yanda yaso da kautar da gaskiya dole ya shige shi. Ya zurawa gidan ido kamar me son gano inda aka haƙo Ƙasar da akayi ginin gidan da ita. Ahmad ya cigaba da tafiya yana ce masa
"Muje mana"
"Zan zo Yah Ahmad Allah bana son rigimar Afeeyah kaga ban gaya mata zan biya wani guri ba kuma na bar wayana a mota kar tayita kira taji shiru kaja mun tayi fushi" ya sake faÉ—i, yanda yayi maganar da ace Ahmad ya mayar da hankali ze fahimci akwai abinda yake dannewa. Ahmad ya girgiza kai yace
"Shikenan, amma wlh idan baka dawo ba Allah ka shirya tarbar rashin mutunchin da zanyi maka" Ahnad ya sake faÉ—a yana jefa masa key É—in mota seya cafe yana murmushin da gara ace kuka ya fasa dashi kafin ya juya yana cewa
"Zan dawo".
Wucewa Ahmad yayi abinsa ya tsaya a Ƙofar gidan kafin ya rangaɗawa Fatima kira a waya, Jay kuwa baya yayi amma be tafi ba, so yakeyi ya tabbatar da gaske wancan gidan Yah Ahmad yake nufi sannan yana so yaga wacece. Fatima a gidan. Indai baya samu makuwar tunani ba wannan shine gidan daya zo shekaran jiya waccen gurin Afeeyah. Irin kallon daya yiwa gidan yasa ko a mafarki baya zaton ze kasa tantance shi balle a zahiri sedai idan kuma gizo idanuwansa sukeyi masa. Bayan fitilar Solar dake kafe a Ƙofar fidan wadda haskenta har tsakar gida yake haska musu da akwai wutar nepa dan haka gurin tarwai yake ta yanda ko abun mutum ne ya faɗi ze iya ganinsa.
Yana jingine jikin katangar daya lafe dan bazeyi gigin tsayuwa akan Ƙafafuwansa kaɗai ba, yaga sanda Ahmad ya saka waya a kunne da alamu ita ya kira kafin ya ajiye mintinu kamar huɗu tsakani ƙofar dake rufe ta buɗe cikin Ƙasa da sakanni biyar Fatima ta bayyana. Tarwai yake hango fuskarta daga inda yake tsaye wadda yake ganin zanen fuskar Afeeyarsa akanta. Irin Doguwar riga Omo blue da farin V hijab da Afeeyah ta tura masa da hotonsu ɗazun a matsayin kayan da zata masa kwalliya dasu ne a jikinta. Daga inda yake tsaya yana iya hango fuskarta da take kicin kicin babu ko ɗigon fara'a inda ta Ahmad ke washe kamar yaron daya tsinci haƙorin makkah.
Bazece ga lokacin daya ɗauka a gurin ba haka kuma baze iya wassafa tunanin da uake zarya a zuciyarsa ba Ƙafafunsa da sukayi sanyi har suka kusan kayar dashi a ƙasane suka ankarar dashi buƙatar ya bar gurin da yake. Tafiya kawai yakeyi bisa jagorancin Ƙafafuwansa ba tareda linzamin idanu ko zuciyarsa ba har Allah ya fitar dashi bakin titin lafiya. Yayi diri diri domin besan ina ze dosa ba. Daga cikin barandar da mutanen nan ke zaune ya hango wasu mutum biyu sun haɗa sahu suna sallah da alama makararrune, shidai baze ce ga yanda akayi ba ya tsinci kansa tsakiyarsu bayan daya saɓule takalmansa, mutanen sukayi raka'a biyu suka sallame Jay ya miƙe ya cigaba da sallah. Tun suna tsammanin ze sallame bayan rama raka'a biyu da be samu tare dasu ba a zatonsu sallar isha'i ce se gashi suna lissafa masa raka'a takwas a jere, ya tashi ze kai ta tara wani dattijo ya riƙe shi yana cewa
"Bawan Allah wace irin sallah ce wannan raka'a goma fa kayi tahiya ɗaya, ai ko sallar Asham ce ba haka akeyinta ba". Be ja ba ya sallame sallar be kuma tanka mutumin ba ya miƙe ya kwashi takalmansa a hannu ya tsallake titi ya tsaya ganin motar Ahmad ya saka ya tuna a mota suka zo harga muƙullin ma a aljihunsa seya zaro shi ya buɗe ya shiga mutanen nan dai suka bishi da idanunu baki harma da hanci wasu na cewa
"Da alamu kan ba ƙalau ba". Wani yace
"Gaskiya babu alamar hauka a tattare dashi idan dai aka ce damuwace ko firgici ya sakashi aikata hakan bazan musa ba"
"Shiko har wace kalar damuwa ko firgici ze sakashi jera raka'a goma har yana shirin ɗorawa ba dan an riƙe shi ba? Wai ba tare suke da yaron nan me zuwa gurin yar gidan Malam Hafizu ba? Su suka tsaya a waccen motar tare kuma suka tsallako yauwa ka gani ma gashi nan ya shiga motar ta yuwu wlh kara zube yake ba ilimin muhammadiyya kasan fa yayan masu kuɗin nan se a hankali da yawansu sallah kawai sukeyi amma basu san me suke yi ba" wani zgudujƙuri ya koro jawabin, oho Jay dai tuni ya bawa mota wuta yai reverse ya fice daga titin ba tare da sanin ina zashi ba.
A can ƙofar gidan Malam Hafizu kuwa bayan fitowar Fatima Ahmad ya kalleta cikin shauƙin So, Allah ne ya jarabce shi da ita dan haka masu ganin baikensa su dena. Fuska a washe kamar kullum yana kallonta bayan daya amsa gaisuwar data masa a daƙile kamar an mata dole yace
"Kinyi kyau" tace
"Uhm" tana wani sake tamke fuska shiko be dameshi ba, ya daÉ—e da sakawa a ransa Fatima tana cikin jerin mutane marasa yawan fara'a shiyasa haÉ—e fuskarta ya dena bashi haushi. Ya gyara tsayuwarsa yana ce mata
"Yasu Baffah da Umma?"
"Lafiya lau suke" ta bashi gajeriyar amaa tana duba wayarta, ya sake mata murmushi yana jingina da bango yace
"Da Sabuwar Fatiman nayi magana a waya kwanakin nan, ina ta zumuÉ—in nazo na tarar da ita se kuma naci sa'ar samun tsohuwar Sarauniya Fatima na nan tana cigaba da zuba mulkinta".
Tayi murmushin nan me kama da taɓe baki bata dai ce komai ba shi kuwa yace
"Tare muke da Jafar yau dai abokanan faÉ—a zasu ga junansu". Da sauri ta kalleshi jin sunan daya ambata tace
"Ashe ya dawo kenan?"
"Gobe satinsa É—aya da dawowa shima soyayyarsa ce ta azalzaloshi ya taho yanda kuma suke buga wasan da zafi ina tsoron karfa suyi mana over taking" ya bata amsa yana kallon fuskarta kamar yanda itama take kallonsa, ta wani yamutsa baki kafin tace
"Allah sarki"
"Dan Allah idan yazo kar kiyi abinda ze sa ku raba hali, gaisawa kawai zakuyi ku maida komai daya wuce ba komai ba already na masa magana nasan shidai baze fara takalarki ba" Ahmad ya faÉ—a cikin sigar lallashi.
Ta harareshi a fakaice kafin tace
"Wato nice ma zan takale shi na janyo abinda zamu raba hali? Kuma da zaka ce abinda ya wuce ya wuce harda zagin mun uba kana zaton yaci banza kenan? Ni bazan iya pretending naso mutumin daya rigada ya furta da bakinsa baya Ƙaunata ba kaima kawai neman tada zaune tsayene ya saka ka taho dashi, ni wlh dana san shine baƙon da kake nufin zaku zo tare bazan ma jiraka ba tafiyata zanyi dan inada abu me muhimmanci a gabana na aje na zauna jiranka" ta Ƙarasa tana sakin ƙaramin tsaki.
Ƙarara fuskarsa ta nuna rashin jin abinda abinda ta faɗa ta gani kuma amma ta ɗauke kai tana cigaba da duba Keypad wayar hannunta tana kallon lokaci kafin ta sake duban hanyar tahowa a ranta tana addu'ar Allah yasa ma yaji haushi ya tafi kafin ya dama mata salalan tsiya.
Ahmad kuwa haka ya haÉ—iye abinda ya taso masa cikin sanyi ya kalli wayar da take ta juyawa a hannunta yace
"Meya samu wayarki na ganki da wannan?"
"Babu komai chaji ne babu na cire Sim É—in" ta bashi amsa ba tareda ta kalle shi ba seya zaro wayarsa daga aljihu ya nuna mata yana cewa
"Ya kamata ma a canza ta tunda anyi lunching sabuwa tuntuni, IPhone É—in kike so ko kina son Samsung irin wannan last week nima na canzata?"
"Waccen ma ta isheni na gode base ka wahalar da kanka ba" ta bashi amsa cikin yanayin irin kamar ya dameta, ya maida wayarsa yana cewa
"Wahala kike kira akan abinda ya shafeki? Idan ban hidimta miki ba neman da nakeyi bashi da amfani kenan. Nifa a rayuwata inajin daÉ—i kawai na kyautatawa mutum koda baze gode mun ba"
Lafazinsa na ƙarshe se taji kamar magana ya faɗa mata ta sake cukulewa bata ce komai ba. Ya waiwaya ya kalli hanya kafin ya ciro wayarsa ya shiga kiran Jay ganin kusan minti nawa shiru babu shi babu labarinsa. A lokacin Jay nata sharara gudu a titi beji kiran ba, sau biyu ya kirashi be amsa ba ya haƙura ya kalleta ganin tana dafe kai ya saka cikin kulawa yace mata
"Ya dai, meya faru kike riƙe kai?"
"Ciwo yakeyi mun yanzu ina tsayen nan naji ya sara" ta bashi amsa tana yatsina kamar gaske nan nan kuwa yace
"Ciwo kuma har yanzu be dena ba amma kika cemun kin warke kin sha magani?"
"Nasha kuma ya dena yanzu ne kawai ya dawo kodan na daɗe a tsaye ne ban sani ba" ta faɗa tana wani sake riƙe kan da hannu biyu. Burinta ya cika dan kuwa sannu ya shiga jero mata yana cewa ko zasuje Asibiti, tace
"Nafa gaya maka an bani magani daman Dr yace na dena yawan tsayuwa da shiga haske sosai su suke tayar mun da ciwon". Ya kalleta kamar me tantamar abinda ta faÉ—a amma yace
Dan Allah muje Jafar na sani daman se munyi haka dakai kuma tunda muka zo nan dai ya kamata ka daure kawai mu ƙarasa yau ɗaya kaga Fatima na tabbatar duk wani grudges dake tsakaninku yau zaku warware shi muje please".
"Wannen ne gidan?" Jafar ya tambayeshi a ransa yana fatan ya nuna lungun daya miƙe yace a ciki gidansu Fatiman yake, kai shi da zata yuwu ma Ahmad yace makuwa yayi ba nan unguwar zasu zo ba saboda abubuwan da zuciyarsa take raya masa sunyi muni da yawa baya fatan ace hakan kuma ta zama gaskiya
"Wancan me Ash paint da baƙar Ƙofa daidai inda Solar take" Ahmad ya sake nuna masa gidan da kwatancen da duk yanda yaso da kautar da gaskiya dole ya shige shi. Ya zurawa gidan ido kamar me son gano inda aka haƙo Ƙasar da akayi ginin gidan da ita. Ahmad ya cigaba da tafiya yana ce masa
"Muje mana"
"Zan zo Yah Ahmad Allah bana son rigimar Afeeyah kaga ban gaya mata zan biya wani guri ba kuma na bar wayana a mota kar tayita kira taji shiru kaja mun tayi fushi" ya sake faÉ—i, yanda yayi maganar da ace Ahmad ya mayar da hankali ze fahimci akwai abinda yake dannewa. Ahmad ya girgiza kai yace
"Shikenan, amma wlh idan baka dawo ba Allah ka shirya tarbar rashin mutunchin da zanyi maka" Ahnad ya sake faÉ—a yana jefa masa key É—in mota seya cafe yana murmushin da gara ace kuka ya fasa dashi kafin ya juya yana cewa
"Zan dawo".
Wucewa Ahmad yayi abinsa ya tsaya a Ƙofar gidan kafin ya rangaɗawa Fatima kira a waya, Jay kuwa baya yayi amma be tafi ba, so yakeyi ya tabbatar da gaske wancan gidan Yah Ahmad yake nufi sannan yana so yaga wacece. Fatima a gidan. Indai baya samu makuwar tunani ba wannan shine gidan daya zo shekaran jiya waccen gurin Afeeyah. Irin kallon daya yiwa gidan yasa ko a mafarki baya zaton ze kasa tantance shi balle a zahiri sedai idan kuma gizo idanuwansa sukeyi masa. Bayan fitilar Solar dake kafe a Ƙofar fidan wadda haskenta har tsakar gida yake haska musu da akwai wutar nepa dan haka gurin tarwai yake ta yanda ko abun mutum ne ya faɗi ze iya ganinsa.
Yana jingine jikin katangar daya lafe dan bazeyi gigin tsayuwa akan Ƙafafuwansa kaɗai ba, yaga sanda Ahmad ya saka waya a kunne da alamu ita ya kira kafin ya ajiye mintinu kamar huɗu tsakani ƙofar dake rufe ta buɗe cikin Ƙasa da sakanni biyar Fatima ta bayyana. Tarwai yake hango fuskarta daga inda yake tsaye wadda yake ganin zanen fuskar Afeeyarsa akanta. Irin Doguwar riga Omo blue da farin V hijab da Afeeyah ta tura masa da hotonsu ɗazun a matsayin kayan da zata masa kwalliya dasu ne a jikinta. Daga inda yake tsaya yana iya hango fuskarta da take kicin kicin babu ko ɗigon fara'a inda ta Ahmad ke washe kamar yaron daya tsinci haƙorin makkah.
Bazece ga lokacin daya ɗauka a gurin ba haka kuma baze iya wassafa tunanin da uake zarya a zuciyarsa ba Ƙafafunsa da sukayi sanyi har suka kusan kayar dashi a ƙasane suka ankarar dashi buƙatar ya bar gurin da yake. Tafiya kawai yakeyi bisa jagorancin Ƙafafuwansa ba tareda linzamin idanu ko zuciyarsa ba har Allah ya fitar dashi bakin titin lafiya. Yayi diri diri domin besan ina ze dosa ba. Daga cikin barandar da mutanen nan ke zaune ya hango wasu mutum biyu sun haɗa sahu suna sallah da alama makararrune, shidai baze ce ga yanda akayi ba ya tsinci kansa tsakiyarsu bayan daya saɓule takalmansa, mutanen sukayi raka'a biyu suka sallame Jay ya miƙe ya cigaba da sallah. Tun suna tsammanin ze sallame bayan rama raka'a biyu da be samu tare dasu ba a zatonsu sallar isha'i ce se gashi suna lissafa masa raka'a takwas a jere, ya tashi ze kai ta tara wani dattijo ya riƙe shi yana cewa
"Bawan Allah wace irin sallah ce wannan raka'a goma fa kayi tahiya ɗaya, ai ko sallar Asham ce ba haka akeyinta ba". Be ja ba ya sallame sallar be kuma tanka mutumin ba ya miƙe ya kwashi takalmansa a hannu ya tsallake titi ya tsaya ganin motar Ahmad ya saka ya tuna a mota suka zo harga muƙullin ma a aljihunsa seya zaro shi ya buɗe ya shiga mutanen nan dai suka bishi da idanunu baki harma da hanci wasu na cewa
"Da alamu kan ba ƙalau ba". Wani yace
"Gaskiya babu alamar hauka a tattare dashi idan dai aka ce damuwace ko firgici ya sakashi aikata hakan bazan musa ba"
"Shiko har wace kalar damuwa ko firgici ze sakashi jera raka'a goma har yana shirin ɗorawa ba dan an riƙe shi ba? Wai ba tare suke da yaron nan me zuwa gurin yar gidan Malam Hafizu ba? Su suka tsaya a waccen motar tare kuma suka tsallako yauwa ka gani ma gashi nan ya shiga motar ta yuwu wlh kara zube yake ba ilimin muhammadiyya kasan fa yayan masu kuɗin nan se a hankali da yawansu sallah kawai sukeyi amma basu san me suke yi ba" wani zgudujƙuri ya koro jawabin, oho Jay dai tuni ya bawa mota wuta yai reverse ya fice daga titin ba tare da sanin ina zashi ba.
A can ƙofar gidan Malam Hafizu kuwa bayan fitowar Fatima Ahmad ya kalleta cikin shauƙin So, Allah ne ya jarabce shi da ita dan haka masu ganin baikensa su dena. Fuska a washe kamar kullum yana kallonta bayan daya amsa gaisuwar data masa a daƙile kamar an mata dole yace
"Kinyi kyau" tace
"Uhm" tana wani sake tamke fuska shiko be dameshi ba, ya daÉ—e da sakawa a ransa Fatima tana cikin jerin mutane marasa yawan fara'a shiyasa haÉ—e fuskarta ya dena bashi haushi. Ya gyara tsayuwarsa yana ce mata
"Yasu Baffah da Umma?"
"Lafiya lau suke" ta bashi gajeriyar amaa tana duba wayarta, ya sake mata murmushi yana jingina da bango yace
"Da Sabuwar Fatiman nayi magana a waya kwanakin nan, ina ta zumuÉ—in nazo na tarar da ita se kuma naci sa'ar samun tsohuwar Sarauniya Fatima na nan tana cigaba da zuba mulkinta".
Tayi murmushin nan me kama da taɓe baki bata dai ce komai ba shi kuwa yace
"Tare muke da Jafar yau dai abokanan faÉ—a zasu ga junansu". Da sauri ta kalleshi jin sunan daya ambata tace
"Ashe ya dawo kenan?"
"Gobe satinsa É—aya da dawowa shima soyayyarsa ce ta azalzaloshi ya taho yanda kuma suke buga wasan da zafi ina tsoron karfa suyi mana over taking" ya bata amsa yana kallon fuskarta kamar yanda itama take kallonsa, ta wani yamutsa baki kafin tace
"Allah sarki"
"Dan Allah idan yazo kar kiyi abinda ze sa ku raba hali, gaisawa kawai zakuyi ku maida komai daya wuce ba komai ba already na masa magana nasan shidai baze fara takalarki ba" Ahmad ya faÉ—a cikin sigar lallashi.
Ta harareshi a fakaice kafin tace
"Wato nice ma zan takale shi na janyo abinda zamu raba hali? Kuma da zaka ce abinda ya wuce ya wuce harda zagin mun uba kana zaton yaci banza kenan? Ni bazan iya pretending naso mutumin daya rigada ya furta da bakinsa baya Ƙaunata ba kaima kawai neman tada zaune tsayene ya saka ka taho dashi, ni wlh dana san shine baƙon da kake nufin zaku zo tare bazan ma jiraka ba tafiyata zanyi dan inada abu me muhimmanci a gabana na aje na zauna jiranka" ta Ƙarasa tana sakin ƙaramin tsaki.
Ƙarara fuskarsa ta nuna rashin jin abinda abinda ta faɗa ta gani kuma amma ta ɗauke kai tana cigaba da duba Keypad wayar hannunta tana kallon lokaci kafin ta sake duban hanyar tahowa a ranta tana addu'ar Allah yasa ma yaji haushi ya tafi kafin ya dama mata salalan tsiya.
Ahmad kuwa haka ya haÉ—iye abinda ya taso masa cikin sanyi ya kalli wayar da take ta juyawa a hannunta yace
"Meya samu wayarki na ganki da wannan?"
"Babu komai chaji ne babu na cire Sim É—in" ta bashi amsa ba tareda ta kalle shi ba seya zaro wayarsa daga aljihu ya nuna mata yana cewa
"Ya kamata ma a canza ta tunda anyi lunching sabuwa tuntuni, IPhone É—in kike so ko kina son Samsung irin wannan last week nima na canzata?"
"Waccen ma ta isheni na gode base ka wahalar da kanka ba" ta bashi amsa cikin yanayin irin kamar ya dameta, ya maida wayarsa yana cewa
"Wahala kike kira akan abinda ya shafeki? Idan ban hidimta miki ba neman da nakeyi bashi da amfani kenan. Nifa a rayuwata inajin daÉ—i kawai na kyautatawa mutum koda baze gode mun ba"
Lafazinsa na ƙarshe se taji kamar magana ya faɗa mata ta sake cukulewa bata ce komai ba. Ya waiwaya ya kalli hanya kafin ya ciro wayarsa ya shiga kiran Jay ganin kusan minti nawa shiru babu shi babu labarinsa. A lokacin Jay nata sharara gudu a titi beji kiran ba, sau biyu ya kirashi be amsa ba ya haƙura ya kalleta ganin tana dafe kai ya saka cikin kulawa yace mata
"Ya dai, meya faru kike riƙe kai?"
"Ciwo yakeyi mun yanzu ina tsayen nan naji ya sara" ta bashi amsa tana yatsina kamar gaske nan nan kuwa yace
"Ciwo kuma har yanzu be dena ba amma kika cemun kin warke kin sha magani?"
"Nasha kuma ya dena yanzu ne kawai ya dawo kodan na daɗe a tsaye ne ban sani ba" ta faɗa tana wani sake riƙe kan da hannu biyu. Burinta ya cika dan kuwa sannu ya shiga jero mata yana cewa ko zasuje Asibiti, tace
"Nafa gaya maka an bani magani daman Dr yace na dena yawan tsayuwa da shiga haske sosai su suke tayar mun da ciwon". Ya kalleta kamar me tantamar abinda ta faÉ—a amma yace