Sashe 61
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jay be kirata ba se washe gari, idan kaga yanda ta fita a hayyacinta seka zata ciwo takeyi kwana guda kawai amma ji take kamar ta shekara ba taredashi ba faɗar irin zafin da takeji a zuciyarta kuwa ɓata lokaci ne, ashe haka Ahmad yake ji akanta shima? Tabbas So abune me ciwo da wahalarwa ta yarda yanzu da ta afka masa kuma ta dena ganin baiken masu zaucewa a soyayya domin ita kanta a yini ɗayan nan da takejin kamar tayi bankwana da farin cikin rayuwarta badan tsoron abinda ze je yazo ba ware baki zatayi tayita kwarara ihu a ɗaki harse nauyin da zuciyarta tayi mata ya ragu amma bata isa ba Umma zataci mata uwa da uba ne tabbas a gidan shiyasa sedai ta lafe a ɗaki tayi kuka ta share hawayenta.
Tana tsaka da shirya kayanta dan ta himmatu gobe zata koma makaranta kafin baƙin ciki yayi Ajalinta a gidan babu jimawa sun gama magana da Ahmad dukda ba qata magana me tsayi bace ba shiya kirata yaji ya take idan babu damuwa zezo Anjima da anyi Magrib tace masa Toh shikenan sukayi sallama. Tana zuge akwati wayarta tayi ƙara ta zabura jin Ringing tune data sakawa Jay ne. A tare suka sauke ajiyar zuciya bayan data amsa wayar kafin ya kira sunanta a sanyaye bata amsa ba se kawai ta sakar masa siririn kuka daya saka ya miƙe tsaye daga kwancen da yake babu shiri
"Kuka kuma? So kike ki ƙaramun damuwa akan wadda nake ciki?" Ya faɗi cikin yanayin daya saka Ahmad dake cin abinci kallonsa. Basu jima da dawowa daga gidan Baba Alƙali ba koda yake Jafar ya ɗakko acan besan ma yaje ba seda ya kirashi yace ya biya dan Alkah su taho tare suna shigowa kuma ya wuce gurin Momy ya karɓo abinci shi Jafar yace Azumi yakeyi seda suka gama magana da Fatima kafin ya fara cin abincin.
"To ba kaine ba tun da ka tafi baka waiwayeni ba" ta faÉ—a cikin kuka. Seya koma ya zauna yana cewa
"Kinyi mun laifi, baki kirani kin bani haƙuri ba and you are expecting me to call you kenan baki san girman lafin da kika aikata ba ko?"
"Na kiraka jiya sau biyu baka amsa ba" ta bashi amsa tana tsagaita kukanta se yace
"Jiya, wato baki damu ba na tafi cikin fushi, baki kirani tun a darenba se jiya shima da rana saboda kin lura ina sonki"
"Wlh ba haka bane ba, kai kace na cire layina daga waya na cire se da safe na samu Ƙarama na saka layin a ciki" ta sharfaɗo Ƙaryar da ita kanta se bayan ta dire maganar kunyar kanta ta dabaibayeta.
"Kinci darajar Son da nake miki shiyasa na kasa daurewa amma da wlh nayi niyyar bazan sake kiranki ba har se bayan anzo an tambayan mun auranki but i couldn't, my heart is going crazy about you ji nakeyi kamar nayi hauka just a day banji muryaki ba". Ina ruwa Afeeyah ta buga tsalle ta faɗa dajin ba haƙura Jay yayi da ita ba kuma ba fasa auranta yayi ba ashe punishing nata yakeyi da Ƙin kiranta aiko ta ladabtu.
"Kayi haƙuri" ta faɗa cikin wata lallausar murya, Jay ya saki murmushi yace
"Zan haƙura but let me see ur face first, oh na manta kin cire Sim daga wancan wayan ko? Then zanzo anjima zan taho miki da wani wayan amma ba fa jimawa zanyi ba dan ban gama hucewa ba, zan baki waya ne kawai na tafi"
Cike da zumuÉ—i kamar zata taka rawa tace
"Allah ya kawo ka lafiya"
"Aiit, take care I love you" ya faÉ—a, ta mayar masa da
"I love you more and i miss you" daga nan suka aje waya. Ya kalli Ahmad dake cin abinci yace
"Yau zamuje gurin Afeeyah"
"Wacece haka?" Ahmad ya tambaya, Jafar ya ɓata fuska yace
"Soyayyata"
"Soyayyarka da kake mun boye boye akanta ko? Aje lafiya nima yau gurin Babyta zanje mun shirya".
"Kayi haƙuri, i promise you idan muka dawo zan gaya maka komai ba abinda kake tunani bane"
"Bana so kuma ba zanje ba na gaya maka gurin Babyta zanje nima" Ahmad ya faÉ—a shima yana kumbura fuska kamar gaske Jafar yace
"How about ka rakani nima na rakaka? Amma gurin Soyayyata za'a fara zuwa"
"Then if you mean ita muje amma gurin Fatima zamu fara zuwa nine babba kaga matata tana gaba da taka kuma nasan wayo kake so kayi mu fara zuwa naka daga nan ka zame ka barni" inji Ahmad. Jay ya yamutsa fuska, kamar yasan abinda ya niyyata zeyi kenan, bashida zaɓi tunda yana so Yah Ahmad ya rakashi gurin Afeeyah dole ya yarda da tsarinsa koda yake gara ma yaje face to face ya zazzagewa Wannan Fatiman abubuwan da suke a ransa, wato ta mayar da Ahmad kamar wani Toy tayi wasa dashi sanda taso ta yar sanda taso to yau kuwa ze buɗe mata aiki.
Suka shirya bayan da akayi sallar magriba suka kama hanya. Jay ne yake tuƙi, suna fita Ahmad ya kira Fatima danya shaida mata bashi kaɗai bane kuma sun taho. Ita shaf ta manta ma da zuwan Ahmad tunda Jay yace mata zezo ta kasa zaune ta kasa tsaye, ta zabari mayafi ta tafi kusadasu aka mata baƙin lalle ranar daya fara zuwa yace mata yana so da yake da wuta nan da nan ta wanke kanta ta busar da Dryer ta tayi styling nasa da adon da ze bayyana sanna ta turara kayan da zata saka Two piece Gown and V Hijab data siya a gurin Ummu-Maheer (07061838488), yadi ne me sauƙin kuɗi amma kyakykyawan ɗinkin daya samu yasa idan ta sakasu ake ɗauka tafiyayyen ne daga Egypt haka Hijabanta.
Umma nata kallon ikon Allah amma bata ce mata komai ba tasan sunyi waya da Ahmad amma bata zaton zuwansa takewa wannan shirin haka.
Tana ganin kiran Ahmad ta tuna da batun zuwansa, ta yi kasaƙe tana tunanin mafita dan Jay ma yace mata yana hanya dukda dai yace ze biya wani guri tukunna. Da sauri ta shiga kiran layin Ahmad bayan data shirya Ƙaryar da zata masa da zata dakatar da zuwansa amma wayar taƙi shiga. Har wani tsirgawa cikinta ya ringayi saboda tashin hankali, ya zatayi idan Jay yazo ya tarar da Ahmad????
PAGE 22
JAY
Suna tafe a mota suna hira gwanin sha'awa irin wadda suka sabayi da alamu yardar zeje gurin Fatima tareda Ahmad ta faranta ran Ahmad ɗin matuƙa dan gashi nan a bayyane. Sun hau kan Gadar ƙofar Nasarawa ya tambayi Ahmad ina zasuyi.
"Miƙewa zakayi Mandawari zamuje" Ahmad ya bashi amsa. Ya taka mota yana cewa
"Ai bansan gurin ba"
"Muje masallacin sarki idan mukayi sallar isha se na karɓi tuƙin" Ahmad ya sake bashi amsa. Jay yayi shiru kamar yacewa Ahmad ai nan ne unguwar su Afeeyah se kuma ya ƙyale. Haka kawai yaki jikinsa ya masa wani iri, gudu yake da mota amma se gashi ya rage speed sosai ya koma tafiya a hankali har suka isa Masallacin, yanajin sanda sukayi waya da Fatiman yaja tsaki bayan da Ahmad yake ce masa wai gidan Yayarta zata tafi
"Kabarta ta tafi kawai se muje gurin my Afee, naga ta kirani ma bana so na amsa kewarta yasa na gudu na barka kace ban kyauta ba"
"Su tsuntsun soyayya, yau dai zanga wannan Afeeyah naga da wane charm ta sace zuciyarka" Ahmad ya faÉ—a yana dariya.
Be manta hanyar daya bi har zuwa bakin titin da ya jira Malam yazo ya tafi dashi ba wannan tasa mamaki ya kamashi sanda yaga bayan sun isa Mandawari Ahmad ya karkata ya shiga titin unguwar su Afeeyah, kasa haƙuri yayi har seda yace masa
"Wai nan ne unguwar su Fatiman?"
"Nan ne, ko kana zaton wata GRA zamuje? To a nan lungun tawa Babyn data sace zuciyata take kuma wlh karka kuskura muje kace zakayi mata izgilanci domin dai ka sani Arziƙi da Talauci duk na Allah ne kuma a aure Tarbiyyar mace ake dubawa bawai girman gidan data fito ba".
Sam bama sauraron Ahmad yake ba illah baza idanu da yayi dakyau yana so ya gane layin da suka shiga da Malam. Akwai wani gida me rumfar langa langa doguwa a daidai kan layin mutane suna zama gurin ya zama kamar masallaci ma dan har butuci ya gani da drum na ruwa a gurin ranar daya zo wannan ya riƙe a ransa matsayin alamar daze ringa gane mashigar lokon nasu dukda idan ya shiga ciki babu tabbacin ya kai kansa saboda zurfin gurin.
Zuciyarsa ta buga Dumm sanda Ahmad yayi parking a daidai spot É—in daya haddace a ransa. Ya ringa kallonsa sanda yake ce masa
"Da yar tafiya daga nan zadai ka iya ko?" Se ya ƙaƙalo murmushin dole yace
"Nida nake zagaye field sau babu adadi kake cewa zan iya wani ɗan trecking kaɗan". Ya fita yanajin wani sanyi na raysa gaɓɓansa dukda cewar zafi akeyi, ya ringa kallon gurin kamar meson yaga ya canza masa daga abinda zuciyarsa take hasaso ma, suka tsallaka yana biye da Ahmad a baya suka shiga cikin lokon
"Ba lallai abinda kake hasashe ya zama gaskiya ba, Ƙaddarah bazatayi muku haka ba, baza ta saka ku Son abu ɗaya wanda baze yuwu ku mallakeshi a tare ba" zuciyarsa ta ringa Ƙarfafa masa guiwa. Ahmad dake masa hira jin baya amsawa ya saka shi kama bakinsa suka ci gaba da tafiya. Jay da yake tunanin idan ya dawo baze iya sake maida kansa gidansu Afeeyah ba se gashi taswirar Lokon na zuwar masa kamar zane a Ƙwaƙwalwarsa, bugun zuciyarsa ya tsananta sanda yaga dagaske sun tasarma layin da gidan Malam Hafizu mahaifin Afeeyah yake ciki, akan kwana yaci burki Ahmad ya kalleshi yace
"Ya akayi naga ka tsaya"
"Nasan Afeeyah tana can tana jirana, so nakeyi na kirata na gaya mata zanyi latti kartaji shiru kayi gaba zan biyo ka" ya rattabo masa ƙaryar da yake ganin ita zata fitar dashi. Ahmad yace
"Ga gidan can ai mu ƙarasa seka kirata ko sarki me Afeeyah" ba tareda ya kalli gidan daya nuna masa ba ya shiga shafa Aljihunsa yana laluben waya amma be jita ba ya saki ajiyar zuciya kafin yace masa
Tana tsaka da shirya kayanta dan ta himmatu gobe zata koma makaranta kafin baƙin ciki yayi Ajalinta a gidan babu jimawa sun gama magana da Ahmad dukda ba qata magana me tsayi bace ba shiya kirata yaji ya take idan babu damuwa zezo Anjima da anyi Magrib tace masa Toh shikenan sukayi sallama. Tana zuge akwati wayarta tayi ƙara ta zabura jin Ringing tune data sakawa Jay ne. A tare suka sauke ajiyar zuciya bayan data amsa wayar kafin ya kira sunanta a sanyaye bata amsa ba se kawai ta sakar masa siririn kuka daya saka ya miƙe tsaye daga kwancen da yake babu shiri
"Kuka kuma? So kike ki ƙaramun damuwa akan wadda nake ciki?" Ya faɗi cikin yanayin daya saka Ahmad dake cin abinci kallonsa. Basu jima da dawowa daga gidan Baba Alƙali ba koda yake Jafar ya ɗakko acan besan ma yaje ba seda ya kirashi yace ya biya dan Alkah su taho tare suna shigowa kuma ya wuce gurin Momy ya karɓo abinci shi Jafar yace Azumi yakeyi seda suka gama magana da Fatima kafin ya fara cin abincin.
"To ba kaine ba tun da ka tafi baka waiwayeni ba" ta faÉ—a cikin kuka. Seya koma ya zauna yana cewa
"Kinyi mun laifi, baki kirani kin bani haƙuri ba and you are expecting me to call you kenan baki san girman lafin da kika aikata ba ko?"
"Na kiraka jiya sau biyu baka amsa ba" ta bashi amsa tana tsagaita kukanta se yace
"Jiya, wato baki damu ba na tafi cikin fushi, baki kirani tun a darenba se jiya shima da rana saboda kin lura ina sonki"
"Wlh ba haka bane ba, kai kace na cire layina daga waya na cire se da safe na samu Ƙarama na saka layin a ciki" ta sharfaɗo Ƙaryar da ita kanta se bayan ta dire maganar kunyar kanta ta dabaibayeta.
"Kinci darajar Son da nake miki shiyasa na kasa daurewa amma da wlh nayi niyyar bazan sake kiranki ba har se bayan anzo an tambayan mun auranki but i couldn't, my heart is going crazy about you ji nakeyi kamar nayi hauka just a day banji muryaki ba". Ina ruwa Afeeyah ta buga tsalle ta faɗa dajin ba haƙura Jay yayi da ita ba kuma ba fasa auranta yayi ba ashe punishing nata yakeyi da Ƙin kiranta aiko ta ladabtu.
"Kayi haƙuri" ta faɗa cikin wata lallausar murya, Jay ya saki murmushi yace
"Zan haƙura but let me see ur face first, oh na manta kin cire Sim daga wancan wayan ko? Then zanzo anjima zan taho miki da wani wayan amma ba fa jimawa zanyi ba dan ban gama hucewa ba, zan baki waya ne kawai na tafi"
Cike da zumuÉ—i kamar zata taka rawa tace
"Allah ya kawo ka lafiya"
"Aiit, take care I love you" ya faÉ—a, ta mayar masa da
"I love you more and i miss you" daga nan suka aje waya. Ya kalli Ahmad dake cin abinci yace
"Yau zamuje gurin Afeeyah"
"Wacece haka?" Ahmad ya tambaya, Jafar ya ɓata fuska yace
"Soyayyata"
"Soyayyarka da kake mun boye boye akanta ko? Aje lafiya nima yau gurin Babyta zanje mun shirya".
"Kayi haƙuri, i promise you idan muka dawo zan gaya maka komai ba abinda kake tunani bane"
"Bana so kuma ba zanje ba na gaya maka gurin Babyta zanje nima" Ahmad ya faÉ—a shima yana kumbura fuska kamar gaske Jafar yace
"How about ka rakani nima na rakaka? Amma gurin Soyayyata za'a fara zuwa"
"Then if you mean ita muje amma gurin Fatima zamu fara zuwa nine babba kaga matata tana gaba da taka kuma nasan wayo kake so kayi mu fara zuwa naka daga nan ka zame ka barni" inji Ahmad. Jay ya yamutsa fuska, kamar yasan abinda ya niyyata zeyi kenan, bashida zaɓi tunda yana so Yah Ahmad ya rakashi gurin Afeeyah dole ya yarda da tsarinsa koda yake gara ma yaje face to face ya zazzagewa Wannan Fatiman abubuwan da suke a ransa, wato ta mayar da Ahmad kamar wani Toy tayi wasa dashi sanda taso ta yar sanda taso to yau kuwa ze buɗe mata aiki.
Suka shirya bayan da akayi sallar magriba suka kama hanya. Jay ne yake tuƙi, suna fita Ahmad ya kira Fatima danya shaida mata bashi kaɗai bane kuma sun taho. Ita shaf ta manta ma da zuwan Ahmad tunda Jay yace mata zezo ta kasa zaune ta kasa tsaye, ta zabari mayafi ta tafi kusadasu aka mata baƙin lalle ranar daya fara zuwa yace mata yana so da yake da wuta nan da nan ta wanke kanta ta busar da Dryer ta tayi styling nasa da adon da ze bayyana sanna ta turara kayan da zata saka Two piece Gown and V Hijab data siya a gurin Ummu-Maheer (07061838488), yadi ne me sauƙin kuɗi amma kyakykyawan ɗinkin daya samu yasa idan ta sakasu ake ɗauka tafiyayyen ne daga Egypt haka Hijabanta.
Umma nata kallon ikon Allah amma bata ce mata komai ba tasan sunyi waya da Ahmad amma bata zaton zuwansa takewa wannan shirin haka.
Tana ganin kiran Ahmad ta tuna da batun zuwansa, ta yi kasaƙe tana tunanin mafita dan Jay ma yace mata yana hanya dukda dai yace ze biya wani guri tukunna. Da sauri ta shiga kiran layin Ahmad bayan data shirya Ƙaryar da zata masa da zata dakatar da zuwansa amma wayar taƙi shiga. Har wani tsirgawa cikinta ya ringayi saboda tashin hankali, ya zatayi idan Jay yazo ya tarar da Ahmad????
PAGE 22
JAY
Suna tafe a mota suna hira gwanin sha'awa irin wadda suka sabayi da alamu yardar zeje gurin Fatima tareda Ahmad ta faranta ran Ahmad ɗin matuƙa dan gashi nan a bayyane. Sun hau kan Gadar ƙofar Nasarawa ya tambayi Ahmad ina zasuyi.
"Miƙewa zakayi Mandawari zamuje" Ahmad ya bashi amsa. Ya taka mota yana cewa
"Ai bansan gurin ba"
"Muje masallacin sarki idan mukayi sallar isha se na karɓi tuƙin" Ahmad ya sake bashi amsa. Jay yayi shiru kamar yacewa Ahmad ai nan ne unguwar su Afeeyah se kuma ya ƙyale. Haka kawai yaki jikinsa ya masa wani iri, gudu yake da mota amma se gashi ya rage speed sosai ya koma tafiya a hankali har suka isa Masallacin, yanajin sanda sukayi waya da Fatiman yaja tsaki bayan da Ahmad yake ce masa wai gidan Yayarta zata tafi
"Kabarta ta tafi kawai se muje gurin my Afee, naga ta kirani ma bana so na amsa kewarta yasa na gudu na barka kace ban kyauta ba"
"Su tsuntsun soyayya, yau dai zanga wannan Afeeyah naga da wane charm ta sace zuciyarka" Ahmad ya faÉ—a yana dariya.
Be manta hanyar daya bi har zuwa bakin titin da ya jira Malam yazo ya tafi dashi ba wannan tasa mamaki ya kamashi sanda yaga bayan sun isa Mandawari Ahmad ya karkata ya shiga titin unguwar su Afeeyah, kasa haƙuri yayi har seda yace masa
"Wai nan ne unguwar su Fatiman?"
"Nan ne, ko kana zaton wata GRA zamuje? To a nan lungun tawa Babyn data sace zuciyata take kuma wlh karka kuskura muje kace zakayi mata izgilanci domin dai ka sani Arziƙi da Talauci duk na Allah ne kuma a aure Tarbiyyar mace ake dubawa bawai girman gidan data fito ba".
Sam bama sauraron Ahmad yake ba illah baza idanu da yayi dakyau yana so ya gane layin da suka shiga da Malam. Akwai wani gida me rumfar langa langa doguwa a daidai kan layin mutane suna zama gurin ya zama kamar masallaci ma dan har butuci ya gani da drum na ruwa a gurin ranar daya zo wannan ya riƙe a ransa matsayin alamar daze ringa gane mashigar lokon nasu dukda idan ya shiga ciki babu tabbacin ya kai kansa saboda zurfin gurin.
Zuciyarsa ta buga Dumm sanda Ahmad yayi parking a daidai spot É—in daya haddace a ransa. Ya ringa kallonsa sanda yake ce masa
"Da yar tafiya daga nan zadai ka iya ko?" Se ya ƙaƙalo murmushin dole yace
"Nida nake zagaye field sau babu adadi kake cewa zan iya wani ɗan trecking kaɗan". Ya fita yanajin wani sanyi na raysa gaɓɓansa dukda cewar zafi akeyi, ya ringa kallon gurin kamar meson yaga ya canza masa daga abinda zuciyarsa take hasaso ma, suka tsallaka yana biye da Ahmad a baya suka shiga cikin lokon
"Ba lallai abinda kake hasashe ya zama gaskiya ba, Ƙaddarah bazatayi muku haka ba, baza ta saka ku Son abu ɗaya wanda baze yuwu ku mallakeshi a tare ba" zuciyarsa ta ringa Ƙarfafa masa guiwa. Ahmad dake masa hira jin baya amsawa ya saka shi kama bakinsa suka ci gaba da tafiya. Jay da yake tunanin idan ya dawo baze iya sake maida kansa gidansu Afeeyah ba se gashi taswirar Lokon na zuwar masa kamar zane a Ƙwaƙwalwarsa, bugun zuciyarsa ya tsananta sanda yaga dagaske sun tasarma layin da gidan Malam Hafizu mahaifin Afeeyah yake ciki, akan kwana yaci burki Ahmad ya kalleshi yace
"Ya akayi naga ka tsaya"
"Nasan Afeeyah tana can tana jirana, so nakeyi na kirata na gaya mata zanyi latti kartaji shiru kayi gaba zan biyo ka" ya rattabo masa ƙaryar da yake ganin ita zata fitar dashi. Ahmad yace
"Ga gidan can ai mu ƙarasa seka kirata ko sarki me Afeeyah" ba tareda ya kalli gidan daya nuna masa ba ya shiga shafa Aljihunsa yana laluben waya amma be jita ba ya saki ajiyar zuciya kafin yace masa