Sashe 40
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"To ai banbancinsu kenan shi yasan mutunchin kansa baze zauna a ringa wulaƙantashi akan abinda yafi ƙarfi ba shi kuwa Ahmad kamar mara zuciya ke nifa ba zan auri Mijin da zan ringa juyawa ba ga yan uwansa basa sona naje ana wulaƙantani baze iya tsayawa ya kwatar mun yanci ba".
Badar tayi kasaƙe tana kallonta amma ta haɗiye abinda tayi niyyar cewa ta canza maganar da wata tace
"Yawwa, nikam kinsan Familyn Jay ne?" kai ta girgiza mata tana cewa
"Aa, me yasa kika tambayeni?"
Tayi ajiyar zuciya zata yi magana kenan Ummi tayi sallama ta shigo, ciki ciki ta amsa fuska a É—aure Badar ce ta tambayeta ya Exam ita kuwa ta zari Bucket ta fita dan tun daga ranar da Islam tace mata tana faÉ—ar maganganu akansu ta washsheta, bata son munafukin mutum, idan ta yarda dakai kayi breaking trust É—inta shikenan kuma.
A gurguje tayi wanka ta shirya dan har Badar ta shirya zata fita Library tace ta jirata suje tare. Maganar da suka fara ɗazu na rantaso take taji dalilin daya saka Badar ta tambayeta ko tasan Familyn Jay dan yanayin da tayi maganar ya nuna akwai wata a ƙasa. A Frizlers sukayi Lunch, tana kallon Badar dake ƙarasa cin abinta tace
"ÆŠazu kina tambayata akan Familyn Jay?" tasha ruwa ta goge bakinta kafin tace
"Oh yah nace kin san wani abu akansu kuwa?"
"Nace miki ai ban sani ba, wani abu ne ya faru kuma?" Ta tambayeta tana yatsina fuska, Badar ta gyara zama tace
Ranar Monday da naje office din Yah Sani (Abokin Yayantane ta ne da yake Lecturing anan) kinsan na gaya miki na taɓa ganinsa sunyi hoto da Jay sanda yaje Masters Uk hoton na office ɗinsa shine ina zuwa da na gani maganarku ta faɗo mun a rai nave masa two weeks ago Jay yazo school ɗin nan, he was suprised yace mun wai ya akayi na sani, then i told him about your encounter kinga mamakin da yayi kuwa? Ashe Mamansa da Maman Jay cousins ne shima suna bala'in shiri sosai gurinsa ma yazo nan Zaria kwanan sa ɗaya ya wuce babu wanda ya san yazo dan da daddare ya shigo kuma a gidansa ya sauka da safen daya fito ma be san inda yaje ba kuma harya tafi babu wanda yace masa ya ganshi then he asked me wai waye Dad dinki a Nigeria da har Jay yace yana sonki?"
"Ban gane ba?" Afeeyah ta katseta fuskar ta na nuna alamar confusion, Badar taci gaba da cewa
"Nima abinda nace masa kenan, to cut the story short Afeeyah abinda na fahimta Mamarsa yar Jari hujja ce, Yah Sani ya gaya mun Jay personally bashi da matsala, and tunda yace yana sonki dagaske yake yi amma inda matslar take mawuyacin abune Mahaifiyarsa ta yarda ya aureki saboda a duniya idan da akwai abinda ta tsana be wuce Talaka ba. Yaranta auran Jari take musu kuma babu wanda ta É—ora buri akansa Irin Jay saboda tafi sonsa duk cikinsu matsayin da yakai yasa ta tattara duk wani burinta na duniya akan matar da ze auro, ita a sonta cikin turawa ko larabawa zeyi aure ai kinsan Shahida Anchau ko?" Ta jefo mata tambaya, ruÉ—u da tashin hankalin da ta shiga yasa dakyar ta É—aga mata kanta da yayi nauyi Badar taci gaba da cewa
"To Mamansu babu yanda batayi akan a haɗa auransu da Shahida ba kinga dai Abbansu kafin ya rasu yayi kuɗi kamar me kuma har yanzu Mamansu kanta tana da kuɗi amma wai Maman Jay taƙi, ba Shahida kaɗai ba yace a Familynsu babu daga gidan da ba'ayi masa tayin aure ba amma taƙi bari ya karɓa. Ki ga dai Familyn ANCHAU duk Kaduna babu wanda be sansu ba saboda tsofaffin kuɗine, arziƙinsu tun duniya na kwance har jikokinsu ba lallai suyi talauchi ba amma Mahaifiyar Jay ta raina su tace bataga yar da ta dace da shi a ciki ba. Ni wlh mantawa nayi ma tunranar ban gaya miki ba se yau abin ya faɗo mun a rai nace masa ma zamuje tare ya faɗa miki da kansa kafin ki ce hassada nake miki ko ƙarya na shirya saboda na rabaki dashi".
Ƙasa Afeeyah tayi da kanta tanajin wani abu nayi mata yawo tsakanin ƙirjinta da maƙoshi yaƙi wucewa yayi ƙasa kuma yaƙi haurowa ya fito. Wato kallon yar masu ƙumbar susa Jay yayi mata saboda ya ganta fara ƙal kalar madara ya shaƙi ƙamshin designer turare a jikinta ga Hijabin Crep yard da Ummu-Maheer tayi mata ze tsammaci irin yan Turkey ɗinnan ne ko Egyptian shiyasa yake sonta?
Kenan wannan ne dalilin da ya saka yake yawan kawo mata labaran ƙasashen duniya idan ta nuna bata sani ba yace wasa takeyi masa? Bata manta ba ranar nan suna maganar kallon Ball da tace masa Badar na kalla a waya yace me yasa ita bazata kalla ba tace masa kawai, se yace ta roƙi Dadynta wannan Holiday ɗin suje Muje London ta kalli wasan sa Live har take ce masa ita Baffa ne da ita ba Dady ba kuma wace London ita da ko Aiport bata taɓa zuwa ba ya ringa dariya yana cewa ta raina masa hankali kenan kallon yar Masu kuɗi yake mata irin wadda Mahaifiyarsa take da burin ya aura lallai kuwa an yanka ta tashi.
"Afeeya your body is shaking, ki nutsu dan Allah ba fa na faÉ—a miki maganar nan saboda ki saka kanki a damuwa bane ba...."
"Na fahimta Badar na gane wlh dama kuma nima ina yawan wannan tunanin a raina, Ahmad da be kaishi matsayi da suna a duniya ba Yan uwansa suna ganin ban dace dashi ba ina ga JAY wanda ba yan uwa ba na tabbata mutanen duniya kansu se sunyi mocking ɗinsa idan suka san yar wa ya aura, damuwata kawai Badar me yasa yasan da wannan tsarin na mahaifiyarsa ze zo gurina? Tun haɗuwata dashi ban boye masa komai a kaina ba, na gaya masa Mahaifina ba kowa bane me neman na kansa ne amma se yayi dariya kawai yaga kamar wasa nakeyi, kuma banyi wani abu na ƙarya da ze saka yayi tunanin na fito daga wani babban Ahali ba ko kawai kenan Surata ce ta rudeshi yayi mun kallon daidai da matsayinsa? Kenan a gidan Masu kudi kadai ake samun Yara masu Kyau da sura irina ba'a haifarsu a gidajen Talakawa?" se tayi shiru tana jin kuka yana taso mata, bata iya riƙe shi ba kuwa ta fara Badar ta miƙe hankali a tashe ta dawo kusada ita ta riƙe hannuna tana cewa
"Dan Allah ki dena kuka kinga ana kallonmu"
"Badar ina son Jay, idan na rasa shi bansan ya rayuwata zata kaya ba. Na sani ban kai koda matsayin me aikinsa ba amma zuciyata ta yi ɗage ta kai kanta inda be kamata taje ba kuma shine sila, shi ya kwaɗaitamun soyayyarsa irin wadda na daɗe ina nema me yasa be dubi matsayi da tazarar dake tsakani mu ba ya shiga rayuwata da alƙawarurrukan ƙarya da ya san baze cikamun su ba ya san mahaifiyarsa nada zaɓi kullum yake cemun duk abinda yake so shi take so ba zata taɓa hanashi auran wata mace ba muddin yace ita yake da muradi?"
"To ai Afeeyah kinga shima Yah Sani ya faɗi abinda ya sani ne kawai akan Mamanshi, zata yuwu ta canza ko kuma kamar yanda ya gaya miki ba zata hanashi auran duk macen da yace yana so ba tunda ta fi sonshi cikin yayanta doke taso farin cikinsa. Ni dalilina na faɗa miki maganar nan saboda karki sake jiki kuma daga ƙarshe ba fata ba ki zama disappointed, amma kamar yanda kika ce shi yasan wacece ke kuma a hakan yace yaji ya gani yana sonki ki kwantar da hankali all shall be well in sha Allah" Badar ta faɗa cikin lallashi.
Afeeyah ta kife kai kan Table taci gaba da rera kuka tamkar har ranar rabuwarsu da Jay tazo, she can't imagine loosing Jay, is like loosing her whole life dan bata tsammanin zata sake moruwa, soyayyar sati uku jinta takeyi tamkar ta shekara ɗari uku, daƙyar ta haƙurtar da kanta ta kuma ɗauki shawarar Badar da tace tayi confronting Jay domin tasan makomar relationship ɗinsu tunda wuri tunda dai shi zuciyarta tayi amannan da. Tabbas tana da buƙatar hakan, zata so ya furta mata da bakinsa tunanin da yakeyi akan Ahalin da ta fito sannan zata kawo maaa maganar Mahaifiyarsa taji view ɗinsa akai.
PAGE 15
A daddafe suka ƙarasa exams idan kaga Afeeyah se ka ɗauka jinya takeyi saboda yanda ta fita a hayyacin ta. Tun daga ranar da Badar ta bata taƙaitaccen labarin Mahaifiyar Jay ta shiga wani yanayi na tunani da lissafin yanda makomarta zata kasance. Ƙarin tashin hankalinta kwanki huɗu kenan basuyi waya da Jay ba, zeyi mata text safe rana dare ya tambayeta ya take amma a ƙarshe ze sake jaddada mata karta kuskura tace zata kirashi har se ta kammala Exam ta san koda ta kira kuma baze amsa ba ita kuma taso suyi magana, ya warware mata abinda ya addabeta a zuciyarta ko ta samu nutsuwa.
Ranar Thursday suka kammala, ƙarfe bakwai da rabi suna shirin fita Ahmad ya kirata wai ya shigo Zaria yana Dogarawa lokacin, tayi kasaƙe da waya tana mamaki dan gaba ɗaya ma ta manta da batun ze zo ɗaukarta yau, ita bata ma shirya kayanta ba dan lissafinta kawai se gobe Juma'a zata wuce gidan amma tunda yazo babu damar tace ya koma hakan dai dole zata shirya ta bishi su tafi dan haka suna fitowa daga Exam basu tsaya komai ba suka wuce Hostel. Ahmad ya sake kiranta akan idan babu damuwa zeje Kd yanzu ya amso wani saƙo kafin ta gama shiryawa ya dawo
Badar tayi kasaƙe tana kallonta amma ta haɗiye abinda tayi niyyar cewa ta canza maganar da wata tace
"Yawwa, nikam kinsan Familyn Jay ne?" kai ta girgiza mata tana cewa
"Aa, me yasa kika tambayeni?"
Tayi ajiyar zuciya zata yi magana kenan Ummi tayi sallama ta shigo, ciki ciki ta amsa fuska a É—aure Badar ce ta tambayeta ya Exam ita kuwa ta zari Bucket ta fita dan tun daga ranar da Islam tace mata tana faÉ—ar maganganu akansu ta washsheta, bata son munafukin mutum, idan ta yarda dakai kayi breaking trust É—inta shikenan kuma.
A gurguje tayi wanka ta shirya dan har Badar ta shirya zata fita Library tace ta jirata suje tare. Maganar da suka fara ɗazu na rantaso take taji dalilin daya saka Badar ta tambayeta ko tasan Familyn Jay dan yanayin da tayi maganar ya nuna akwai wata a ƙasa. A Frizlers sukayi Lunch, tana kallon Badar dake ƙarasa cin abinta tace
"ÆŠazu kina tambayata akan Familyn Jay?" tasha ruwa ta goge bakinta kafin tace
"Oh yah nace kin san wani abu akansu kuwa?"
"Nace miki ai ban sani ba, wani abu ne ya faru kuma?" Ta tambayeta tana yatsina fuska, Badar ta gyara zama tace
Ranar Monday da naje office din Yah Sani (Abokin Yayantane ta ne da yake Lecturing anan) kinsan na gaya miki na taɓa ganinsa sunyi hoto da Jay sanda yaje Masters Uk hoton na office ɗinsa shine ina zuwa da na gani maganarku ta faɗo mun a rai nave masa two weeks ago Jay yazo school ɗin nan, he was suprised yace mun wai ya akayi na sani, then i told him about your encounter kinga mamakin da yayi kuwa? Ashe Mamansa da Maman Jay cousins ne shima suna bala'in shiri sosai gurinsa ma yazo nan Zaria kwanan sa ɗaya ya wuce babu wanda ya san yazo dan da daddare ya shigo kuma a gidansa ya sauka da safen daya fito ma be san inda yaje ba kuma harya tafi babu wanda yace masa ya ganshi then he asked me wai waye Dad dinki a Nigeria da har Jay yace yana sonki?"
"Ban gane ba?" Afeeyah ta katseta fuskar ta na nuna alamar confusion, Badar taci gaba da cewa
"Nima abinda nace masa kenan, to cut the story short Afeeyah abinda na fahimta Mamarsa yar Jari hujja ce, Yah Sani ya gaya mun Jay personally bashi da matsala, and tunda yace yana sonki dagaske yake yi amma inda matslar take mawuyacin abune Mahaifiyarsa ta yarda ya aureki saboda a duniya idan da akwai abinda ta tsana be wuce Talaka ba. Yaranta auran Jari take musu kuma babu wanda ta É—ora buri akansa Irin Jay saboda tafi sonsa duk cikinsu matsayin da yakai yasa ta tattara duk wani burinta na duniya akan matar da ze auro, ita a sonta cikin turawa ko larabawa zeyi aure ai kinsan Shahida Anchau ko?" Ta jefo mata tambaya, ruÉ—u da tashin hankalin da ta shiga yasa dakyar ta É—aga mata kanta da yayi nauyi Badar taci gaba da cewa
"To Mamansu babu yanda batayi akan a haɗa auransu da Shahida ba kinga dai Abbansu kafin ya rasu yayi kuɗi kamar me kuma har yanzu Mamansu kanta tana da kuɗi amma wai Maman Jay taƙi, ba Shahida kaɗai ba yace a Familynsu babu daga gidan da ba'ayi masa tayin aure ba amma taƙi bari ya karɓa. Ki ga dai Familyn ANCHAU duk Kaduna babu wanda be sansu ba saboda tsofaffin kuɗine, arziƙinsu tun duniya na kwance har jikokinsu ba lallai suyi talauchi ba amma Mahaifiyar Jay ta raina su tace bataga yar da ta dace da shi a ciki ba. Ni wlh mantawa nayi ma tunranar ban gaya miki ba se yau abin ya faɗo mun a rai nace masa ma zamuje tare ya faɗa miki da kansa kafin ki ce hassada nake miki ko ƙarya na shirya saboda na rabaki dashi".
Ƙasa Afeeyah tayi da kanta tanajin wani abu nayi mata yawo tsakanin ƙirjinta da maƙoshi yaƙi wucewa yayi ƙasa kuma yaƙi haurowa ya fito. Wato kallon yar masu ƙumbar susa Jay yayi mata saboda ya ganta fara ƙal kalar madara ya shaƙi ƙamshin designer turare a jikinta ga Hijabin Crep yard da Ummu-Maheer tayi mata ze tsammaci irin yan Turkey ɗinnan ne ko Egyptian shiyasa yake sonta?
Kenan wannan ne dalilin da ya saka yake yawan kawo mata labaran ƙasashen duniya idan ta nuna bata sani ba yace wasa takeyi masa? Bata manta ba ranar nan suna maganar kallon Ball da tace masa Badar na kalla a waya yace me yasa ita bazata kalla ba tace masa kawai, se yace ta roƙi Dadynta wannan Holiday ɗin suje Muje London ta kalli wasan sa Live har take ce masa ita Baffa ne da ita ba Dady ba kuma wace London ita da ko Aiport bata taɓa zuwa ba ya ringa dariya yana cewa ta raina masa hankali kenan kallon yar Masu kuɗi yake mata irin wadda Mahaifiyarsa take da burin ya aura lallai kuwa an yanka ta tashi.
"Afeeya your body is shaking, ki nutsu dan Allah ba fa na faÉ—a miki maganar nan saboda ki saka kanki a damuwa bane ba...."
"Na fahimta Badar na gane wlh dama kuma nima ina yawan wannan tunanin a raina, Ahmad da be kaishi matsayi da suna a duniya ba Yan uwansa suna ganin ban dace dashi ba ina ga JAY wanda ba yan uwa ba na tabbata mutanen duniya kansu se sunyi mocking ɗinsa idan suka san yar wa ya aura, damuwata kawai Badar me yasa yasan da wannan tsarin na mahaifiyarsa ze zo gurina? Tun haɗuwata dashi ban boye masa komai a kaina ba, na gaya masa Mahaifina ba kowa bane me neman na kansa ne amma se yayi dariya kawai yaga kamar wasa nakeyi, kuma banyi wani abu na ƙarya da ze saka yayi tunanin na fito daga wani babban Ahali ba ko kawai kenan Surata ce ta rudeshi yayi mun kallon daidai da matsayinsa? Kenan a gidan Masu kudi kadai ake samun Yara masu Kyau da sura irina ba'a haifarsu a gidajen Talakawa?" se tayi shiru tana jin kuka yana taso mata, bata iya riƙe shi ba kuwa ta fara Badar ta miƙe hankali a tashe ta dawo kusada ita ta riƙe hannuna tana cewa
"Dan Allah ki dena kuka kinga ana kallonmu"
"Badar ina son Jay, idan na rasa shi bansan ya rayuwata zata kaya ba. Na sani ban kai koda matsayin me aikinsa ba amma zuciyata ta yi ɗage ta kai kanta inda be kamata taje ba kuma shine sila, shi ya kwaɗaitamun soyayyarsa irin wadda na daɗe ina nema me yasa be dubi matsayi da tazarar dake tsakani mu ba ya shiga rayuwata da alƙawarurrukan ƙarya da ya san baze cikamun su ba ya san mahaifiyarsa nada zaɓi kullum yake cemun duk abinda yake so shi take so ba zata taɓa hanashi auran wata mace ba muddin yace ita yake da muradi?"
"To ai Afeeyah kinga shima Yah Sani ya faɗi abinda ya sani ne kawai akan Mamanshi, zata yuwu ta canza ko kuma kamar yanda ya gaya miki ba zata hanashi auran duk macen da yace yana so ba tunda ta fi sonshi cikin yayanta doke taso farin cikinsa. Ni dalilina na faɗa miki maganar nan saboda karki sake jiki kuma daga ƙarshe ba fata ba ki zama disappointed, amma kamar yanda kika ce shi yasan wacece ke kuma a hakan yace yaji ya gani yana sonki ki kwantar da hankali all shall be well in sha Allah" Badar ta faɗa cikin lallashi.
Afeeyah ta kife kai kan Table taci gaba da rera kuka tamkar har ranar rabuwarsu da Jay tazo, she can't imagine loosing Jay, is like loosing her whole life dan bata tsammanin zata sake moruwa, soyayyar sati uku jinta takeyi tamkar ta shekara ɗari uku, daƙyar ta haƙurtar da kanta ta kuma ɗauki shawarar Badar da tace tayi confronting Jay domin tasan makomar relationship ɗinsu tunda wuri tunda dai shi zuciyarta tayi amannan da. Tabbas tana da buƙatar hakan, zata so ya furta mata da bakinsa tunanin da yakeyi akan Ahalin da ta fito sannan zata kawo maaa maganar Mahaifiyarsa taji view ɗinsa akai.
PAGE 15
A daddafe suka ƙarasa exams idan kaga Afeeyah se ka ɗauka jinya takeyi saboda yanda ta fita a hayyacin ta. Tun daga ranar da Badar ta bata taƙaitaccen labarin Mahaifiyar Jay ta shiga wani yanayi na tunani da lissafin yanda makomarta zata kasance. Ƙarin tashin hankalinta kwanki huɗu kenan basuyi waya da Jay ba, zeyi mata text safe rana dare ya tambayeta ya take amma a ƙarshe ze sake jaddada mata karta kuskura tace zata kirashi har se ta kammala Exam ta san koda ta kira kuma baze amsa ba ita kuma taso suyi magana, ya warware mata abinda ya addabeta a zuciyarta ko ta samu nutsuwa.
Ranar Thursday suka kammala, ƙarfe bakwai da rabi suna shirin fita Ahmad ya kirata wai ya shigo Zaria yana Dogarawa lokacin, tayi kasaƙe da waya tana mamaki dan gaba ɗaya ma ta manta da batun ze zo ɗaukarta yau, ita bata ma shirya kayanta ba dan lissafinta kawai se gobe Juma'a zata wuce gidan amma tunda yazo babu damar tace ya koma hakan dai dole zata shirya ta bishi su tafi dan haka suna fitowa daga Exam basu tsaya komai ba suka wuce Hostel. Ahmad ya sake kiranta akan idan babu damuwa zeje Kd yanzu ya amso wani saƙo kafin ta gama shiryawa ya dawo