← Book details Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 43 OF 71

Sashe 43

Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Alhaji kayi shiru" Hamshaƙiyar ta girgizashi. Ya aje farantin hannunsa ya miƙe tsaye yana cewa
"Ki karɓo kuɗinki kizo kuyi a nan cikin gidan kamar yanda su Aisha zasuyi ni banida wasu kuɗi da zan sake baki kuma a yanzu nayi iya abinda zan iya"

"Ai shikenan, kana ji Jafaru wai baze zo bikin bako? Gaskiya ka kirashi kayi masa magana ta yaya za'ayi ace baze halarci ɗaurin auran ba? Ta ya mutane wai zasu san Ɗanka ne yafi so ayi ta kallonsa a ba kowa ba ai idanya fito kowa ya san Ɗanka ne darajar sa seta sake linkuwa a ƙasar nan ko ya kace?" Ta sake soko masa wata maganar, ya miƙe yana shiga ɗaki yace
"Duk yanda kika ce Binta, bari na shirya na fita dai na baki guri" ya barta tana cizon yatsa. Daman ba Even centre data kama, tunda taji a gida Momy zatayi Kamunta zata kira masu Decoration taje kakarta ta yanke saƙa bari zatayi ta gama shirya komai se ranar tayi ta kankane ita da mutanenta dan ba zata iya zare Miliyan nawa ta kaiwa masu gurin biki ba, abinci ma da Turai tasa ta kashi kuɗaɗe ta bayar ciwon rai takeyi, so tayi ta bawa masu aikinsu ayi shi nan a cikin gida amma tace gun yan gayu zasu kai, so tayi ya bata kuɗin ta rage asarar wanda tabayar shine yace bashida su yanzu duk kwalliyar nan da tayi ta tashi a banza kenan ai shikenan.

Alhaji ya fito a shirye yana waya, bata san da waye ba abinda taji kawai ya fizgi hankalinta shine
"Babu damuwa nagode, bari mu gama da hayaniyar wannan bikin zanyi magana dashi. Idan son samune ya haƙura da yarinyar ya nemi wata dan sam banji abin ya kwanta mun a rai ba amma bama so na hanashi abinda yake so saboda yaron nada biyayya nasan muddin nace Aa tilas ze haƙura koda ace hakan ze cutar dashi amma yanzu zan samu Alƙali shima da maganar yanda mukayi zakaji".

"Toh fa wane yaro kuma ake magana akai?" Tayi tsalam ta tambaya bayanya kashe wayar. Yana tafiya ze sauka ƙasa tabi bayansa yace
"Ahmad ne, ya samu yarinyar da ze aura. Kiyiwa wancan yaron magana shima ya dakata da shashancin da yakeyi ya fitar da mata dan tare zan haÉ—u bana son Biki a rarraben nan"

"Yo naji kana cewa yarinyar bata maka ba? Halan kwashe kwashe yayo ko? Ni daman nasan za'a rina Allah yasa dai ba gidan matsiyata ya kwaso auran ba mu shiga uku su ƙara yawa bamu gama data gidan nan ba ya kwaso mana wata" Hajiya ta faɗa shidai be bata amsa ba ya fice daga falon dan Malam Sadi Driver sa yana tsaye harya kunna mota.

Ta wuce ciki inda ta baro ƙawayenta da sukazo ana ta tsara yanda biki ze kasance, Kamu dai rigar na Momy zasu shiga dukda ba haka su Hajiya Zainab suka so ba Turai kuma tace haka ne daidai tunda dai Yaran nan ubansu ɗaya toh ayi Kamun nan a tare idan yaso tunda kowacce gidan Mijinta sun shirya Dinner se suyi abarsu daban ga sauran events da kowacce Amarya zatayi da Ƙawayenta.

"Yanzu kawai sedai mu zama yan kallo mun raɓe raɓe kenan?" Hajiya Sha'awa ta faɗa, Binta ta karkace tace
"Inji wa? Ai biki namune wahala kawai zasu mana su shirya komai. Da kunji ance ina uwar Amarya ku rufa mun baya mu shige, duk wani kira da za'ayi ku shike kuyi kinini karku basu wata ƙofa a gurin" akayi shewa aka tafa.

Se ranar Laraba Ahmad ya kaiwa Fatima Ɗinkakkun kaya, Atamfa me kyau da akayiwa ɗinkin zamani amma Modest ɗinki se wani shegen Lace da Anty Sauda tace ya haura dubu ɗari biyu. Kowanne kaya da mahaɗinsa, Takalmi, mayafi, jaka harda Sarƙa da agogo. Zobunan gold guda biyu ya saka mata a ciki ganinsu ya tuna mata da ranar da yace ta nuna masa hannunta kenan measurement ɗin hannun ya ɗauka. Yace mata Atamfar ta Ankon Kamun ce dan ya gaya mata zasuyi biki har Iv ya tura mata Lace kuma kawai ɗinka mata yayi na Dinner.

Tace ba zataje ba Umma ta goya mata baya a cewarta babu tsayayyar magana a tsakaninsu da har zata saka taje musu biki, idan kuma zuwan nata ya janyo wani abu da ba za'a so ba fa? Gara dai da ace anyi magana yan uwansa sun san da zamanta da sauƙi ko cikin yan uwa tana iya samun wata suje tare su dawo. Baffa ma da aka gaya masa cewa yayi Aa. Da kansa ya kira Ahmad yace ba zataje ba, yayi kuma faɗan zobuna har biyu da Umma tace masa zinare ne yace in yazo ya karɓe su ya ajiye idanAllahyasa taje gidansa ya bata ya dai amsa da Toh amma koshi Baffan yasan baze karɓa ba dan yasha ya kawo mata abu yace a mayar yaƙi karɓa sedai ya kalallameshi da magana yace ko babu soyayya tsakaninsu Baffa Babansa ne zeyi mata komai saboda shi. Wannan ya rushe batun zuwanta Biki wanda daman ko da an barta a karan kanta ba zata so taje ba, to wai se taje a matsayinta nawa???

An dai yi biki a gidan Alhajin Bechi lafiya duk kalen bala'in Hajia da yan korarta dole suka kama kansu domin Yan uwan Momy da ƙawayenta wannan karon basu zo da wasa ba. Yanda Hajiyar ta saba musu idan ana biki ba yarta ba amma komai yana hannu ta se abinda tace se yanda ta tsara za'ayi wannan karon basu bari ba. Basu saurari Alhajin ba kansa Ahmad da Sarki sun share mata hawayen komai domin duk halinsa shima wannan karon Ahmad ya shawo kansa sun fitarda mahaifiyarsu kunya ba tareda sunyi jiran kowa ba. Anyi biki lafiya Amare sun tare Hafsatu an tafi Abuja Aslamiyyah na nan Kano se Amaryar Yakubu shima da Allah yayi bana yayi auran tsalle tsalle ya ƙare dukda seda Alhajin yayi masa barazana da ze saukeshi daga Acting Account General dan har yanzu ba'ayi confirming nasa ba kafin ya kawo matar akayi Bikin.

Afeeyah kuwa Rikicewa ta ringayi harta fara zaton WhatsApp ɗinta ya samu matsala saboda status ɗin Ahmad da Jay da suka zama iri ɗaya tunda aka fara bikin har aka gama seta yi tunanin repeating sukeyi taga kamar ana Jay dan komai ma gizon sunansa yake mata yanzu. Ko kusa bata kawo cewar Jay ze iya haɗa wata alaƙa da Ahamd ba shiyasa ma bata tsawaita tunani ko bincike ba ganin kuma komai ya koma normal shikenan ta manta. Ada bata fiya wani duba status ba amma haɗuwarta da Jay kusan kullum seta duba update ɗinsa wanda duk akanta yakeyi. Yace mata yaso yazo Nigeria abinda ya hanashi zuwa contract ɗinsa da Arsenal taje ƙarshe, Clubs da yawa suna zawarcinsa har yanzu kuma beyi finalizing inda ze koma ba yana so se yayi sealing deal ɗin kafin yaje wani guri. Ya tura maata da sabon Field name ɗinsa, a maimakon JAY its going to be AJAY. Yace A for AFEEYAH and JAY remain for the JAFAR bata yarda da gaske yake ba har se ranar da yayi sealing deal da PSG sabuwar rigarsa da AJAY aka bugata.

Ta ringa murmushi kamar wawiya sanda take kallon Interview ɗinsa, an tambayeshi me yasa ya canza suna kuma me A take nufi yace it remains secret lokacin da ze bayyana yana zuwa. Tana jin Yah Malam ɗinsu da Abokinsa Sani da tsabar yanda yake son Jay sunansa ya koma Jay ranar sunata magana. Ance Initial ɗin budurwarsa ne, wasu sunce Initial ɗin Yayansa ne da yake bala'in so kowa dai da abinda yake faɗi. Kamar taje ta gaya musu gaskiya se kuma ta kama bakinta. Anty Sauda tayiwa Umma zancen itama bata bada goyon baya na cewa ma tayi karsu bari Baffa yaji dan ranta ne ze ɓaci. Ya za'ayi tsayin lokacin nan ta dawo tace wani daban ba Ahmad ba itama tasan wasa takeyi. A ranta ko babu gudu babu ja da baya tasan kuma Baffa baze taɓa bin ta tasu ba ya aura mata abinda bata so. Ai da bakinta bata taɓa cewa wani tana son Ahmad ba ko zata aureshi su suke kiɗansu suna rawarsu dan haka babu wata hujja da za'a kafa da zata rabata da wanda take so, badai yace ya kusa zuwa Nigeria ba yana zuwa zata kaishi gidan ayita ta ƙare da haka suka cinye hutun session daya ritsa da Strike kusan watansu uku a gidan kafin suka koma School First semester Four hundred level.
PAGE 16
Rayuwa ta shuɗa, soyayyar Afeeyah da Jay tana ƙara ƙarfi inda al'amarinta tsakaninta da Ahmad yake sake taɓaɓarewa. Zywa yanzu ya gama tabbatarwa Fatima bata ta tashi da gaske wani ya masa shigar sauri kuma ya sure Imaninta. Ya sake tsananta Addu'a akan Al'amarin amma mainakon rangwame se sake jinta yakeyi a zuciyarsa kamar ture. Damuwar da yake ciki da ayyuka da suka masa yawa yasa duk ya sake figewa ya fita a hayyacinsa. Kowa a gidan yaro da babba ya shaida Ahmad yana da damuwa hatta Hajiya kuwa seda ranar ta tsare shi tace

"Kai Amadu anya magauta basu danneka ba? Wannan uwar rama haka kamar wanda ake ɗiba ayi miya kullum? Koda yake jarabar neman kuɗi daka saka a ranka ai dole kaƙi abin kirki, ni na rasa ma me kake nema ko kuwa so kake se ka yi gasa da ƙaninka ne? Shidai kasan yan guje guje kawai zeyi a fili ya dirim Miliyoyi sun shiga akawun, shiyasa yake mulla ƙibarsa kai kuwa kana ta fama da dogon wuya kamar tsohon raƙumi takwaran ubanka". A Ƙofar ɗakinta take maganar ga Hajiya bata rage Volume dan haka hatta Momy dake cikin falonta suna magana da Baba Bilki sun jiyota. Baba Bilki ta girgiza kai tace
Chapter 43 · 0% Book details