Sashe 56
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Amma ni kaÉ—ai zanje gaida mahaifin nata kamar wani mara galihu?" Ya faÉ—i kamar ze masa kuka, Ahmad ya sake cewa
"Duk ni sanda nake zuwa nawa gaisuwar dawa mukaje? In baka iya zuwa kai kai kaÉ—ai ka kira ko Sadik ko Anwar su rakaka"
"Ni dakai nake so muje"
"Shikenan seka jira na kai Alhajinmu dawo se mu tafi"
"Salon Babanta yace I'm not serious ba? Allah kawai dan ta riga da ta gaya masa ina zuwa da fasawa zanyi kawai naje muyi hira idan yaso daga baya se muje gurin Popsyn nata da kai" Jafar ya dira mita daga ƙarshe ya kama hanya ya tafi shi kaɗai Ahmad kuma ya kai Alhaji AKTH duba Abokinsa. A hanya Alhajin yake cewa Ahmad
"Babanku ya gaya mun iyayen yarinyar sun dakatar da zuwa tambaya sunce a basu sati huÉ—u ko?"
"Eh haka yace Alhaji" ya bashi amsa ba dan yaso ya tado masa da maganar ba. Alhaji ya sake cewa
"Ka bincika kaji dalilin daya saka suka ce hakan ne?"
"Eh, kawunta wanda ze bayar da auran ne baya nan yayi tafiya shine dalili" Ahmad ya yanko ƙarya ya lafta masa.
"Uhm kodai basu shirya ba dai kuma suna jin nauyin su gaya maka ka saka musu hannu a cikin shirin nasu?" Alhaji ya sake faÉ—i yana kallon Ahmad da yanayinsa ya nuna he is not comfortable da maganar da maganar da Alhajin ya tayar. A sanyaye yace kawai yayi shiru be bashi amsa ba hakan tasa shima Alhaji ya kama kansa can kuma ya sake soko wata maganar yace
"Wato shi gaban kansa yakeyi babu wanda ya saka cikin lamarin auransa daga kai se Uwarsa ko?"
Yasan da Jafar yake dan haka yace
"Jiya ya fara zuwa gidansu Alhaji, tsarin Babansu ne kuma se yaga mutum kafinya bashi damar neman auran yarsa shiyasa zeje yau ya gaishe shi amma ba wai maganar auran ce ta taso ba".
"Dama aiba zaka taɓa faɗar laifinsa ba, shi kuma yar waye yake nema?"
"Nima ban sani ba yanzun zamuje daman kuma ya tafi shi kaɗai" cikin yanayin Ƙosawa da tambayoyin ya bashi amsa se Alhaji ya Ƙaro radion Mota yayi shiru.
Jay kuwa be fahimci kwatancen da Afeeyah ta turo masa ba dan haka tace tayi sharing masa live location ɗinta haka kuwa akayi yana biye da Map tiryen tiryen se gashi a cikin gari tsukin unguwar Marmara. A bakin titi yayi parking mota yana ƙarewa gurin daya zo kallo, dukda darene amma Jama'a nata kai kawo yanda kasan kasuwa ga surutu kaya kaya banda ƙarar ababen hawa da suke karakaina akan titi.
He couldn't believe it a wannan unguwar suke zaune. Ya ringa zungura kai yana leƙa yan hanyoyin da yake gani, gurin da Map ɗinza yake pointing lungune da babu alamar Mota tana iya shiga.
"Ta yuwu Babansu irin mutanen nan ne da basa son canza muhalli shiyasa ya ke zaune a nan ƙila da akwai wata hanya kota can baya da suke bi da mota har ƙofar gida" ya shiga baiwa kansa Ƙwarin guiwa. A waya ya kirata ya gaya mata yana bakin titi besan ta inda ze shigo ba tace masa zata bawa Yayanta wayarta seya zo ya tafi dashi haka kuwa akayi ta bawa Yaya Malam wayar sukayi magana harya gano inda yake.
Seda ya rufe fuskarsa da Facemask kafin ya fita daga motar, sukayi musabiha sannan suka tsallaka Titi, suka ringa bin lunguna suna tafiya shidai bin Malam kawai yakeyi a baya a ransa yana mamakin wannan unguwa daya zo yau, a rayuwarsa be taɓa shiga makamancin lungun ba, iyakarsa da nan haka gidan Sarki dan kafin ya tafi Turai yayi nacin son Doki da sallah ko idan an gayyaci Alhajinsu wani taro yakan biyo shi saboda yaga Doki shi be san akwai irin lokunan nan bama a Kano.
Tun yana hasashen ganin gida me Gate harya saduda domin dai gidajen jar laka yake tacin karo dasu wanda Hasken Nepa da Sololin da gwamnati ta ƙawata lokunan dasu suka taimaka masa gurin ganinsu tsaf kamar da rana. Seya saki tunanin gidan Gate ya kama na kodai Babansu Basarake ne? Tunda akan samu gidan Sarakai cikin lungu. Bashi da me bashi amsa haka ya ringa jefa ƙafafu har suka isa inda yaga Malam ya dakata da alamu nan ne gidansu Afeeyah.
Ya ƙarewa gidan kallo cikin abinda befi sakan biyar ba, da fulasta lulluɓe dan haka bayace ginin ƙasa bane kona sumunti. Filin dai dukansa baze wuce taku Ashirin da biyar a kwance ba idan ma ya kai, be san ya zurfinsa yake ta ciki ba. Zuciya da saƙe saƙe take ta ayyano masa ai Akurkin da Alhaji Audu ya watsasu a gidansa ma yafi wannan gidan girma da yalwa.
Muryar Malam ta dawo dashi daga tunanin daya tafi yana cewa
"Bari na sanar mata ka iso" ya wuce cikin siririn soron gidan Jay harda tura wuya yana leƙawa. Ya saki ajiyar zuciya me ƙarfi bayan da Malam ya dawo yace masa Baffah yace ya shiga. A baya ya bishi cikin taka tsan tsan dan kar Ƙofar gidan ta rafke masa goshi dan ya lura shima Malam ɗin da yake dogo ne sosai seya ranƙwafa yake shiga.
Tilas ya yabawa tsaftar matar gidan domin dukda darene ko ina tsaf yake babu tarkace, a fakaice ya kalli ƙofofi guda huɗu da suke cikin gidan wanda yake tsammanin ɗakuna ne, ya hango kitchen da kuma inda yake zaton makewayine saboda ga famfo nan se siririn lungu ya shiga ciki. A cikin barandar dake gaban ɗakuna biyu suna kuma kallon ragowan biyun ya zauna kan shimfiɗar babbar darduma da akayi. Harda standing fan a ajiye a gurin. Malam ya shige ɗakin Baffah ya sanar masa ga Baƙon wanda tuni Ƙamshin turarensa ya sanar musu da shigowarsa.
Dattijon daya tabbatar shine mahaifin Fatima ya fito, fuskarsa a sake yake yiwa Jafar da duk yaji ya rikice kamar wanda yaje gaban Sarki Maraba. Ya zauna daura dashi, Jafar ya duƙe yana gaida shi amma Baffan ya bashi hannu sukayi musabaha. Tattaunawar tasu batayi tsayi ba, ya tambayeshi waye shi sana'arsa data mahaifinsa. Daga yanayi na kamala da kuma tambayoyin da Baffah yayi masa be ga wata matsala a tattare dashi ba. Baffan yace masa
"Da akwai wanda yake neman Afeeyah kafin zuwanka sun jima dashi amma ta tabbatar mun da kai take so, ina fatan a shirye kake domin bana so maganar auran taja lokaci, zan baka daga nan zuwa sati biyu ka turo magabatanka domin muyi magana, da zarar ta kammala karatu a É—aura muku aure"
"In sha Allahu Baffah" Jay ya faÉ—i yana goge zufar data tsatstsafo masa daga goshi. Baffah ya karkato masa da fanka saitinsa yana cewa
"Garin da akwai zafi sosai dan ma an samu wuta kasha ruwan ko zaka samu sauƙin zafin" ya nuna masa ruwan pure water da Zoɓon gora wanda Umma take siyarwa Malam ya ajiye masa tun zamansu. Umma ce tace pure water za'a bashi domin su na famfo ma suke sha ai kuwa har kuka Afeeyah tayi akan hakan.
Jay ya kalli farantin ruwan yayi murmushi kawai ba tareda ya sha ba, Baffah ya miƙe yana cewa
"Bari naje, an gayyaceni Mauludi anan Ƙasanmu zuwan kane ya dakayar dani da tuni naje dan bana so nayi dare a waje" se shima Jay ya miƙe tsaye yana laluba Aljihunsa. Bandir na dubu ɗaya ya zaro ya rage tsayi kafin ya miƙawa Baffan yana cewa
"Gashi babu yawa a siyi goro". Baffah ya kalli kuɗin yayi ƙaramin murmushi kafin yace
"Nagode Allah yayi Albarka" ya wuce ba tareda ya karɓa ba yana cewa Umma ta leƙo su gaisa. Malam ne ya fito daga falo yace ya shiga can kawai, yayi masa jagora Umma na zaune kan kujera tana kallon Arewa 24 a yar Plasmarta da Baffah ya saka mata kwanannan da Hijabinta har ƙasa Jay ya kai ya gaisheta ta amsa a mutunce tana cewa ya hau kujera sw ya sake kalmashe ƙafa ya zauna sosai akan Centre carpet kansa a ƙasa.
"Kira masa ita" Umma ta faɗa tana miƙewa ta fice daga falon sega Malam da Afeeyah, ya baje a gabansa daman Baffa yake jira ya fita dan ta Umma me sauƙi ne. Kamar wanda za'ayi wa Ƙarin karatu haka ya zauna bakin nan har kunne yau gashi ga Jay a gidansu.
"Wai meye haka Yah Malam?" Afeeyah ta faÉ—a tana tura baki. Jay ya kalleta bbau yabo babu fallasa yace
"Ina ruwanki? Yayanmu ne kuma Fan"
"Loyal Fan ma kuwa, dan Allah ina zuwa be kamata naci amanar Jay ba gara na fara sanar masa ya zo ya ganka inaga har suma zeyi yau saboda ÆŠaÉ—i" Yah Malam ya faÉ—i kafin ya sake ficewa da sauri kiran Amininsa Sani. Tsabar yanda yake Son Jay ne sunansa ya koma haka, babarsa kanta ta tashi daga Mamansu Sani ta koma Mamansu Jay dako ka zagi Jay a gaban Sani gara ka ambato Babansa Malam Hamza ka zaga.
Bayan fitar Malam Afeeyah ta zauna yanda Jay yake binta da kallo kamar me neman wani abu a jikinta ne duk yasa ta tsargu. Atamfa ta saka yau A line gown Dark blue ce da fari se dan jaja kaɗan a jiki kalar ta haska ta sosai ta mata kyau. Cikin sanyin murya ta gaishe shi, ya amsa bataji sautin muryarsa ba laɓɓansa taga sun motsa shine ta fahimci ya amsa mata. Jikinta yayi sanyi, murnar dake ranta ta yau Jafar yazo gurin Baffah alamar maganar auransu na dab da Ƙulluwa ta disashe. Ta tsammaci ganin fuskarsa a washe kamar jiya koma tafi hakan amma se taga saɓanin zatonta, ba yabo ba fallasa, ba wannan Fara'ar da ya ringayi jiya balle zumuɗin taɓata se binta yakeyi da kallon data rasa dalilin sa.
"Duk ni sanda nake zuwa nawa gaisuwar dawa mukaje? In baka iya zuwa kai kai kaÉ—ai ka kira ko Sadik ko Anwar su rakaka"
"Ni dakai nake so muje"
"Shikenan seka jira na kai Alhajinmu dawo se mu tafi"
"Salon Babanta yace I'm not serious ba? Allah kawai dan ta riga da ta gaya masa ina zuwa da fasawa zanyi kawai naje muyi hira idan yaso daga baya se muje gurin Popsyn nata da kai" Jafar ya dira mita daga ƙarshe ya kama hanya ya tafi shi kaɗai Ahmad kuma ya kai Alhaji AKTH duba Abokinsa. A hanya Alhajin yake cewa Ahmad
"Babanku ya gaya mun iyayen yarinyar sun dakatar da zuwa tambaya sunce a basu sati huÉ—u ko?"
"Eh haka yace Alhaji" ya bashi amsa ba dan yaso ya tado masa da maganar ba. Alhaji ya sake cewa
"Ka bincika kaji dalilin daya saka suka ce hakan ne?"
"Eh, kawunta wanda ze bayar da auran ne baya nan yayi tafiya shine dalili" Ahmad ya yanko ƙarya ya lafta masa.
"Uhm kodai basu shirya ba dai kuma suna jin nauyin su gaya maka ka saka musu hannu a cikin shirin nasu?" Alhaji ya sake faÉ—i yana kallon Ahmad da yanayinsa ya nuna he is not comfortable da maganar da maganar da Alhajin ya tayar. A sanyaye yace kawai yayi shiru be bashi amsa ba hakan tasa shima Alhaji ya kama kansa can kuma ya sake soko wata maganar yace
"Wato shi gaban kansa yakeyi babu wanda ya saka cikin lamarin auransa daga kai se Uwarsa ko?"
Yasan da Jafar yake dan haka yace
"Jiya ya fara zuwa gidansu Alhaji, tsarin Babansu ne kuma se yaga mutum kafinya bashi damar neman auran yarsa shiyasa zeje yau ya gaishe shi amma ba wai maganar auran ce ta taso ba".
"Dama aiba zaka taɓa faɗar laifinsa ba, shi kuma yar waye yake nema?"
"Nima ban sani ba yanzun zamuje daman kuma ya tafi shi kaɗai" cikin yanayin Ƙosawa da tambayoyin ya bashi amsa se Alhaji ya Ƙaro radion Mota yayi shiru.
Jay kuwa be fahimci kwatancen da Afeeyah ta turo masa ba dan haka tace tayi sharing masa live location ɗinta haka kuwa akayi yana biye da Map tiryen tiryen se gashi a cikin gari tsukin unguwar Marmara. A bakin titi yayi parking mota yana ƙarewa gurin daya zo kallo, dukda darene amma Jama'a nata kai kawo yanda kasan kasuwa ga surutu kaya kaya banda ƙarar ababen hawa da suke karakaina akan titi.
He couldn't believe it a wannan unguwar suke zaune. Ya ringa zungura kai yana leƙa yan hanyoyin da yake gani, gurin da Map ɗinza yake pointing lungune da babu alamar Mota tana iya shiga.
"Ta yuwu Babansu irin mutanen nan ne da basa son canza muhalli shiyasa ya ke zaune a nan ƙila da akwai wata hanya kota can baya da suke bi da mota har ƙofar gida" ya shiga baiwa kansa Ƙwarin guiwa. A waya ya kirata ya gaya mata yana bakin titi besan ta inda ze shigo ba tace masa zata bawa Yayanta wayarta seya zo ya tafi dashi haka kuwa akayi ta bawa Yaya Malam wayar sukayi magana harya gano inda yake.
Seda ya rufe fuskarsa da Facemask kafin ya fita daga motar, sukayi musabiha sannan suka tsallaka Titi, suka ringa bin lunguna suna tafiya shidai bin Malam kawai yakeyi a baya a ransa yana mamakin wannan unguwa daya zo yau, a rayuwarsa be taɓa shiga makamancin lungun ba, iyakarsa da nan haka gidan Sarki dan kafin ya tafi Turai yayi nacin son Doki da sallah ko idan an gayyaci Alhajinsu wani taro yakan biyo shi saboda yaga Doki shi be san akwai irin lokunan nan bama a Kano.
Tun yana hasashen ganin gida me Gate harya saduda domin dai gidajen jar laka yake tacin karo dasu wanda Hasken Nepa da Sololin da gwamnati ta ƙawata lokunan dasu suka taimaka masa gurin ganinsu tsaf kamar da rana. Seya saki tunanin gidan Gate ya kama na kodai Babansu Basarake ne? Tunda akan samu gidan Sarakai cikin lungu. Bashi da me bashi amsa haka ya ringa jefa ƙafafu har suka isa inda yaga Malam ya dakata da alamu nan ne gidansu Afeeyah.
Ya ƙarewa gidan kallo cikin abinda befi sakan biyar ba, da fulasta lulluɓe dan haka bayace ginin ƙasa bane kona sumunti. Filin dai dukansa baze wuce taku Ashirin da biyar a kwance ba idan ma ya kai, be san ya zurfinsa yake ta ciki ba. Zuciya da saƙe saƙe take ta ayyano masa ai Akurkin da Alhaji Audu ya watsasu a gidansa ma yafi wannan gidan girma da yalwa.
Muryar Malam ta dawo dashi daga tunanin daya tafi yana cewa
"Bari na sanar mata ka iso" ya wuce cikin siririn soron gidan Jay harda tura wuya yana leƙawa. Ya saki ajiyar zuciya me ƙarfi bayan da Malam ya dawo yace masa Baffah yace ya shiga. A baya ya bishi cikin taka tsan tsan dan kar Ƙofar gidan ta rafke masa goshi dan ya lura shima Malam ɗin da yake dogo ne sosai seya ranƙwafa yake shiga.
Tilas ya yabawa tsaftar matar gidan domin dukda darene ko ina tsaf yake babu tarkace, a fakaice ya kalli ƙofofi guda huɗu da suke cikin gidan wanda yake tsammanin ɗakuna ne, ya hango kitchen da kuma inda yake zaton makewayine saboda ga famfo nan se siririn lungu ya shiga ciki. A cikin barandar dake gaban ɗakuna biyu suna kuma kallon ragowan biyun ya zauna kan shimfiɗar babbar darduma da akayi. Harda standing fan a ajiye a gurin. Malam ya shige ɗakin Baffah ya sanar masa ga Baƙon wanda tuni Ƙamshin turarensa ya sanar musu da shigowarsa.
Dattijon daya tabbatar shine mahaifin Fatima ya fito, fuskarsa a sake yake yiwa Jafar da duk yaji ya rikice kamar wanda yaje gaban Sarki Maraba. Ya zauna daura dashi, Jafar ya duƙe yana gaida shi amma Baffan ya bashi hannu sukayi musabaha. Tattaunawar tasu batayi tsayi ba, ya tambayeshi waye shi sana'arsa data mahaifinsa. Daga yanayi na kamala da kuma tambayoyin da Baffah yayi masa be ga wata matsala a tattare dashi ba. Baffan yace masa
"Da akwai wanda yake neman Afeeyah kafin zuwanka sun jima dashi amma ta tabbatar mun da kai take so, ina fatan a shirye kake domin bana so maganar auran taja lokaci, zan baka daga nan zuwa sati biyu ka turo magabatanka domin muyi magana, da zarar ta kammala karatu a É—aura muku aure"
"In sha Allahu Baffah" Jay ya faÉ—i yana goge zufar data tsatstsafo masa daga goshi. Baffah ya karkato masa da fanka saitinsa yana cewa
"Garin da akwai zafi sosai dan ma an samu wuta kasha ruwan ko zaka samu sauƙin zafin" ya nuna masa ruwan pure water da Zoɓon gora wanda Umma take siyarwa Malam ya ajiye masa tun zamansu. Umma ce tace pure water za'a bashi domin su na famfo ma suke sha ai kuwa har kuka Afeeyah tayi akan hakan.
Jay ya kalli farantin ruwan yayi murmushi kawai ba tareda ya sha ba, Baffah ya miƙe yana cewa
"Bari naje, an gayyaceni Mauludi anan Ƙasanmu zuwan kane ya dakayar dani da tuni naje dan bana so nayi dare a waje" se shima Jay ya miƙe tsaye yana laluba Aljihunsa. Bandir na dubu ɗaya ya zaro ya rage tsayi kafin ya miƙawa Baffan yana cewa
"Gashi babu yawa a siyi goro". Baffah ya kalli kuɗin yayi ƙaramin murmushi kafin yace
"Nagode Allah yayi Albarka" ya wuce ba tareda ya karɓa ba yana cewa Umma ta leƙo su gaisa. Malam ne ya fito daga falo yace ya shiga can kawai, yayi masa jagora Umma na zaune kan kujera tana kallon Arewa 24 a yar Plasmarta da Baffah ya saka mata kwanannan da Hijabinta har ƙasa Jay ya kai ya gaisheta ta amsa a mutunce tana cewa ya hau kujera sw ya sake kalmashe ƙafa ya zauna sosai akan Centre carpet kansa a ƙasa.
"Kira masa ita" Umma ta faɗa tana miƙewa ta fice daga falon sega Malam da Afeeyah, ya baje a gabansa daman Baffa yake jira ya fita dan ta Umma me sauƙi ne. Kamar wanda za'ayi wa Ƙarin karatu haka ya zauna bakin nan har kunne yau gashi ga Jay a gidansu.
"Wai meye haka Yah Malam?" Afeeyah ta faÉ—a tana tura baki. Jay ya kalleta bbau yabo babu fallasa yace
"Ina ruwanki? Yayanmu ne kuma Fan"
"Loyal Fan ma kuwa, dan Allah ina zuwa be kamata naci amanar Jay ba gara na fara sanar masa ya zo ya ganka inaga har suma zeyi yau saboda ÆŠaÉ—i" Yah Malam ya faÉ—i kafin ya sake ficewa da sauri kiran Amininsa Sani. Tsabar yanda yake Son Jay ne sunansa ya koma haka, babarsa kanta ta tashi daga Mamansu Sani ta koma Mamansu Jay dako ka zagi Jay a gaban Sani gara ka ambato Babansa Malam Hamza ka zaga.
Bayan fitar Malam Afeeyah ta zauna yanda Jay yake binta da kallo kamar me neman wani abu a jikinta ne duk yasa ta tsargu. Atamfa ta saka yau A line gown Dark blue ce da fari se dan jaja kaɗan a jiki kalar ta haska ta sosai ta mata kyau. Cikin sanyin murya ta gaishe shi, ya amsa bataji sautin muryarsa ba laɓɓansa taga sun motsa shine ta fahimci ya amsa mata. Jikinta yayi sanyi, murnar dake ranta ta yau Jafar yazo gurin Baffah alamar maganar auransu na dab da Ƙulluwa ta disashe. Ta tsammaci ganin fuskarsa a washe kamar jiya koma tafi hakan amma se taga saɓanin zatonta, ba yabo ba fallasa, ba wannan Fara'ar da ya ringayi jiya balle zumuɗin taɓata se binta yakeyi da kallon data rasa dalilin sa.