Sashe 27
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai ta É—aga kamar yana ganinta tace
"Na gane"
"Yawwa idan ma baki iya ba se ki koya dan ni babu ruwana da wasu continental dishes da kika ganni shiyasa ma kikaga nake daidaitan se Umma ta sauke abincin dare nake zuwa gidanku dan ba Ƙaramin daɗin girkinta nake ji ba kuma na ci na Anty Sauda ma naji yayi kalar na Umma Allah yasa kema haka kika iya girki"
"Ina koya" ta bashi amsa a taƙaice tana janye wayar daga kunnenta, minti goma sha daya suna magana zan iya cewa basu taɓa kaiwa haka suna waya ba idan ma sunyi to befi sau a ƙirga ba. Kamar ya shiga ranta taji shima yana cewa
"This is our longest phone call so far, bari na shigar dashi a Diary yau É—in ta shiga tarihi".
Ta yatsina fuska kamar yana ganinta kafin tayi magana cikin sauri taji yace
"Ki huta Fatima, i will call you later Jafar yana kiran É—aya wayana".
Wani tuƙuƙin baƙin ciki ya taso mata dajin sunan wanda ya ambata. Ta tsani Jafar ɗin nan tsana me tsanani da bata san iyakarta ba. Bata ko amsa masa ba ta kashe wayar tqna jan mugun tsaki. Maman Minal da bataji shigowarta ba ta ce
"Lafiya kike tsaki haka?"
"Babu komai" ta bata amsa tana miƙewa saboda yunwa data faraji. Ta zuba taliyar data gani a tukunya ta hau ci ranta duk a dagule, ta kusan cinyewa Badar ta shigo da alama ta kwaso yunwa dan hannu kawai ta wanke ta dirarwa abincin da Afeeyan take ci seta tsame hannu ta bar mata dan daman ta ƙoshi gudun kar su mata masifar da suka saba idan ta rage abinci yasa take turawa daƙyar.
"Jibi tuwo zamuci a É—akin nan" Maman Minal data idar da sallah ta faÉ—a, Afeeya ta kalleta, Badar tace
"Ai kuwa mun kwana biyu bamuyi tuwo ba. Bari rana ta lafa se muje cefane miyar me za'ayi?"
"Kamar Kuka naji kince ko Afee?" Ta jefawa Afeeyah tambayar, zare manyan idonunta tayi tana kallonta da rashin fahimta dan bata gane inda maganarta ta dosa ba, ita yaushe sukayi zancen tuwo?
Maman Minal Ta miƙe tana ninke sallaya tace
"Zancen tuwo naji sunayi da Ahmad shine naji sha'awarsa nima kinga se ta mana Jibi idan zezo"
"Kai Anty Zahra daga jin muna magana bafa cewa yayi yana so ba labari ne kawai ya kawo maganar ba cewa yayi na masa ba" tayi saurin defending kanta kafin su ƙallaba mata abinda bazata iya ba. Badar dake side hannu ta cafe tana cewa
"Aiko yin tuwo Lazim idan ba so yake ba meze saka ya miki zancensa kawai dai be fito kai tsaye bane ke kuma in kinada lissafi ai kinsan me yake nufi Allah ya kaimu jibin dama bamu da Lectures kuma na shinkafa zaki mana Aradu ki tuƙeshi da kyau yasa malmala mu kwashi gara abinmu"
"Aiko zaki ɗige indai ni zan tuƙa miki tuwo, shima ya nemi inda zeci tun dare be masa ba wlh" Cewar Afeeya, Badar ta hayayyaƙo mata tana cewa
"Wlh se kinyi, ko mu ba zaki dafa mana ba se kin wa Ahmad banza wadda bata san Abin kirki ba. Ahmad É—in nan kwanta miki kaÉ—ai ya rage ya farayi amma hakan be saka yaci darajar mutunchi kema ki ringa mutuntashi ba kici gaba ubangiji ya miki ni'ima amma kina nema ki butulce masa in bakiyi wasa ba kika watsar da damarki ba fata na miki ba gaba se kinyi kuka da dana sanin rasa shi dan wlh a zamanin nan samun kamar Ahmad Namiji kyakykyawa, me kuÉ—i ga Ilimi da nutsuwa ga hankali kuma ya soki tsakani da Allah bawai da lalataba se an tona ai mazan dai gasu nan ke zaki bada labari dan babu kalar saurayin da bakiyi ba kowa kuma yazo iskanci yake kawoshi koda wanda ya tsaya bayan Ahmad din" Badar ta faÉ—a a hasale bacin ran ya nuna har kan fuskarta.
Kallonta Afeeya tayi bayan data zauna akan gadonta, bata tanka mata ba ta maida kai kan wayarta tana duba number data kirata yanzu kafinkuma ta answer ta katse, ganin ta waje ce yasa ta ajiye wayar ta yuwu Kamfanine ko sacammer. Tana jin Badar na maganganu tayi mata banza dan idan ta tanka se ran kowa ya ɓaci.
Badar tana yawan faÉ—a mata maganganun da bata jin daÉ—insu akan Ahmad amma tanayi mata uzuri saboda tasan bada wata manufa take faÉ—arsu ba a ganinta damuwa da lamarinta nema har yasa take tada jijiyar wuya akan abinda ya shafeta amma kuma idan aka kalli maganar tata ta wata sigar tana nuna kamr Alfarma Ahmad yayi mata da har yake sonta wanda wannan yana daga cikin abubuwan da yasa bata sonsa.
Bazata auri Mijin da ya zarce matsayinta ba wanda kowa ze ringa mata kallon cusa kanta tayi ko kuma Alfarma yayi mata daya aureta bata kai Ajinsa ba kamar yanda ÆŠan uwansa ya faÉ—a mata.
"Badar na gaya miki ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba idan kina son Ahmad na bar miki shi kuma zanyi duk iyawata gurin ganin kin same shi. Na sani ba tsarana bane, ire irenki ne m daidai dashi, matsayi da Arziqin iyayenku yayi kamanceceniya kinga babu me ganin cewar Alfarma yayi miki idan yayi tarayya dake" Afeeya ta faɗa zafafe tana barin ɗakin saboda gajiya da maganganun Badar dukda yanda Maman Minal da Ummi suke mata magana akan tayi shiru amma taƙi, dagaske neman fitinarta takeyi yau amma ba zata biye mata ba gara ta fita.
"Saboda ina sonki na damu dake ina miki burin ki auri Mijin da yake sonki kiji daɗi shine kike gaya mun haka ko Afeeya?" Ta faɗa tana Ƙanƙancr ido. Fes Afeeyan ta kalleta tace
"Kinji abinda na faÉ—a ai, Ahmad ne bana sonsa bazan aure shi ba kuma fatan da kike mun baze kamani ba Allah ze kawo mun Miji Talaka daidaini na aura wanda babu me saka mana ido ballantana a ringa fassara duk wani motsina akan sa da sunan na butulcewa ni'imar ubangiji".
"Meye haka Afeeya?" Maman Minal ta dakatar da ita, ta kalleta da idonta da suka fara canza kala tace
"To akan me Anty Zahra? Duk sanda magana zata haɗo akan Ahamd se Badar ta yimun gori a fakaice tace yafi ƙarfi na? ni na janyo shi nace ya soni ko yaya? Da yana da zuciya ma ai da bamu kai haka tare ba saboda na nuna masa bana muradinsa ta duk hanyar data dace amma ya nace ya kafe so takeyi na aureshi Alhalin danginsa basa ƙaunata? Ba'a a kunnenta ƙaninsa yayi mun cin mutunchi ya zagi iyayena sannan ta dage sena cusa kaina inda Allah be kaini ba saboda kwadayin abin duniya?
Toni kudinsa ko wani matsayi nasa ba zasu rufe mun ido ba su sa na jefa rayuwata cikin ƙunci na rayu da mutanen da basa so na, idan tana sonsa gashi nan na bar mata ta aureshi itace daidaishi" ta ƙarasa tana Ƙoƙarin riƙe kukan daya taho mata amma ta kasa dole ta sakeshi ta doshi Ƙofa zata fita amma mutanen da suka tsatstsaya munafunci yasa ta fasa fitar ta shige bayan Ummi da ke zaune ta kasa cewa komai ta kwanta tana kuka.
Maman Minal ta kulle Ƙofar jiki a sanyaye kafin ta zauna tana cewa
"Daga zancen tuwo shikenan se tashin hankali? da alama sheɗan ya shigo ya laɓe a ɗakin nan shiya haɗa komai kuma bazeyi nasara ba in sha Allah".
Badar da jikinta yayi sanyi laƙwas ta zauna daga tsayuwar da tayi ta kasa cigaba da masifar tata. Har ga Allah ita batayi magana da manufar da Afeeya ta ɗauka ba, ta riƙi Afeeyar a matsayin yar uwa shiyasa har take son cigabanta take kuma son ta da Ahmad ganin cewar mutumin kirkine ya na da duk wasu qualities da mace zata so a gurin Namiji gashi yana sonta baya ga haka wlh ita bata da wata manufa ta daban akan maganar.
Dakin ya ɗauki shiru se shasheƙar kukan Afeeya, kowa da tunanin da take a ranta wayarta ta sake ɗaukar ƙara lambar dazun ce bacin ran da take ciki yasa ta kashe wayar gaba ɗaya ba tareda na amsa kiran ba. Ranar har dare dukkansu basu da walwala shiru ɗakin kamar anyi mutuwa, tsakaninta da Badar kuwa se kallo seda Baffa ya kira wayarta akan be samu ta Afeeyan ba sannan nema ta tuna data kashe wayar tata, data miƙa mata bata kar ɓa ba, ta kunna tata ta kirashi.
Sururat ce ta saka su shirin dole cikin daren bayan ta dawo Ummi da Maman Minal suka tsara mata abinda ya faru ta ringa masifa ta kuma É—orawa Afeeya laifi kacokan wannan yasa suma sauran suka buÉ—e baki tare da nuna cewar ita ce bata kyauta ba su da kyakykyawar niyya suke tare da ita kuma wannan tasa har suke son abinda suke ganin ze zamar mata Alkhairi ba wani abu ba.
Bata so aja maganar da tsaho dan haka nace taji ta kuma bawa Badar haƙuri kamar yanda Sururat tayi insisting.
"Wlh Afeeya ina jinki kamar Yah Yusra, idan har zan iya aure ko soyayya da Mijinta to zanyi da Ahmad. Son da yake miki da kamalarsa tasa har nake miki sha'awar auransa dan nasan irinsa basu da yawa a duniyar yanzu amma tunda har zuciyarki tana raya miki wani abu daban akan niyyata in sha Allahu zan kama kaina, bazan sake yi miki wata magana data shafeshi ko ma akan saurayi ba gaba ɗaya. Zanci gaba dayi miki Addu'a Allah ya zaɓa miki abinda yafi Alkhairi" Badar din ta faɗa bayan da Afeeya ta bata haƙurin,
jikinta yayi sanyi ganin yanda idonta ke zubar kwalla sanda take maganar, ta tabbata har ranta gaskiya take faɗa kuma Badar na sonta kamar yanda ita ma take sonta amma abune yazo da rashin fahimta dukkan su kowa tana da dalilanta na so ko Ƙin tarayyata da Ahmad amma ta haɗiye nata za kuma ta cigaba da addu'a Allah ya fiddo mata da Mijinta daidai ita ya fiye mata sauƙi.
"Na gane"
"Yawwa idan ma baki iya ba se ki koya dan ni babu ruwana da wasu continental dishes da kika ganni shiyasa ma kikaga nake daidaitan se Umma ta sauke abincin dare nake zuwa gidanku dan ba Ƙaramin daɗin girkinta nake ji ba kuma na ci na Anty Sauda ma naji yayi kalar na Umma Allah yasa kema haka kika iya girki"
"Ina koya" ta bashi amsa a taƙaice tana janye wayar daga kunnenta, minti goma sha daya suna magana zan iya cewa basu taɓa kaiwa haka suna waya ba idan ma sunyi to befi sau a ƙirga ba. Kamar ya shiga ranta taji shima yana cewa
"This is our longest phone call so far, bari na shigar dashi a Diary yau É—in ta shiga tarihi".
Ta yatsina fuska kamar yana ganinta kafin tayi magana cikin sauri taji yace
"Ki huta Fatima, i will call you later Jafar yana kiran É—aya wayana".
Wani tuƙuƙin baƙin ciki ya taso mata dajin sunan wanda ya ambata. Ta tsani Jafar ɗin nan tsana me tsanani da bata san iyakarta ba. Bata ko amsa masa ba ta kashe wayar tqna jan mugun tsaki. Maman Minal da bataji shigowarta ba ta ce
"Lafiya kike tsaki haka?"
"Babu komai" ta bata amsa tana miƙewa saboda yunwa data faraji. Ta zuba taliyar data gani a tukunya ta hau ci ranta duk a dagule, ta kusan cinyewa Badar ta shigo da alama ta kwaso yunwa dan hannu kawai ta wanke ta dirarwa abincin da Afeeyan take ci seta tsame hannu ta bar mata dan daman ta ƙoshi gudun kar su mata masifar da suka saba idan ta rage abinci yasa take turawa daƙyar.
"Jibi tuwo zamuci a É—akin nan" Maman Minal data idar da sallah ta faÉ—a, Afeeya ta kalleta, Badar tace
"Ai kuwa mun kwana biyu bamuyi tuwo ba. Bari rana ta lafa se muje cefane miyar me za'ayi?"
"Kamar Kuka naji kince ko Afee?" Ta jefawa Afeeyah tambayar, zare manyan idonunta tayi tana kallonta da rashin fahimta dan bata gane inda maganarta ta dosa ba, ita yaushe sukayi zancen tuwo?
Maman Minal Ta miƙe tana ninke sallaya tace
"Zancen tuwo naji sunayi da Ahmad shine naji sha'awarsa nima kinga se ta mana Jibi idan zezo"
"Kai Anty Zahra daga jin muna magana bafa cewa yayi yana so ba labari ne kawai ya kawo maganar ba cewa yayi na masa ba" tayi saurin defending kanta kafin su ƙallaba mata abinda bazata iya ba. Badar dake side hannu ta cafe tana cewa
"Aiko yin tuwo Lazim idan ba so yake ba meze saka ya miki zancensa kawai dai be fito kai tsaye bane ke kuma in kinada lissafi ai kinsan me yake nufi Allah ya kaimu jibin dama bamu da Lectures kuma na shinkafa zaki mana Aradu ki tuƙeshi da kyau yasa malmala mu kwashi gara abinmu"
"Aiko zaki ɗige indai ni zan tuƙa miki tuwo, shima ya nemi inda zeci tun dare be masa ba wlh" Cewar Afeeya, Badar ta hayayyaƙo mata tana cewa
"Wlh se kinyi, ko mu ba zaki dafa mana ba se kin wa Ahmad banza wadda bata san Abin kirki ba. Ahmad É—in nan kwanta miki kaÉ—ai ya rage ya farayi amma hakan be saka yaci darajar mutunchi kema ki ringa mutuntashi ba kici gaba ubangiji ya miki ni'ima amma kina nema ki butulce masa in bakiyi wasa ba kika watsar da damarki ba fata na miki ba gaba se kinyi kuka da dana sanin rasa shi dan wlh a zamanin nan samun kamar Ahmad Namiji kyakykyawa, me kuÉ—i ga Ilimi da nutsuwa ga hankali kuma ya soki tsakani da Allah bawai da lalataba se an tona ai mazan dai gasu nan ke zaki bada labari dan babu kalar saurayin da bakiyi ba kowa kuma yazo iskanci yake kawoshi koda wanda ya tsaya bayan Ahmad din" Badar ta faÉ—a a hasale bacin ran ya nuna har kan fuskarta.
Kallonta Afeeya tayi bayan data zauna akan gadonta, bata tanka mata ba ta maida kai kan wayarta tana duba number data kirata yanzu kafinkuma ta answer ta katse, ganin ta waje ce yasa ta ajiye wayar ta yuwu Kamfanine ko sacammer. Tana jin Badar na maganganu tayi mata banza dan idan ta tanka se ran kowa ya ɓaci.
Badar tana yawan faÉ—a mata maganganun da bata jin daÉ—insu akan Ahmad amma tanayi mata uzuri saboda tasan bada wata manufa take faÉ—arsu ba a ganinta damuwa da lamarinta nema har yasa take tada jijiyar wuya akan abinda ya shafeta amma kuma idan aka kalli maganar tata ta wata sigar tana nuna kamr Alfarma Ahmad yayi mata da har yake sonta wanda wannan yana daga cikin abubuwan da yasa bata sonsa.
Bazata auri Mijin da ya zarce matsayinta ba wanda kowa ze ringa mata kallon cusa kanta tayi ko kuma Alfarma yayi mata daya aureta bata kai Ajinsa ba kamar yanda ÆŠan uwansa ya faÉ—a mata.
"Badar na gaya miki ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba idan kina son Ahmad na bar miki shi kuma zanyi duk iyawata gurin ganin kin same shi. Na sani ba tsarana bane, ire irenki ne m daidai dashi, matsayi da Arziqin iyayenku yayi kamanceceniya kinga babu me ganin cewar Alfarma yayi miki idan yayi tarayya dake" Afeeya ta faɗa zafafe tana barin ɗakin saboda gajiya da maganganun Badar dukda yanda Maman Minal da Ummi suke mata magana akan tayi shiru amma taƙi, dagaske neman fitinarta takeyi yau amma ba zata biye mata ba gara ta fita.
"Saboda ina sonki na damu dake ina miki burin ki auri Mijin da yake sonki kiji daɗi shine kike gaya mun haka ko Afeeya?" Ta faɗa tana Ƙanƙancr ido. Fes Afeeyan ta kalleta tace
"Kinji abinda na faÉ—a ai, Ahmad ne bana sonsa bazan aure shi ba kuma fatan da kike mun baze kamani ba Allah ze kawo mun Miji Talaka daidaini na aura wanda babu me saka mana ido ballantana a ringa fassara duk wani motsina akan sa da sunan na butulcewa ni'imar ubangiji".
"Meye haka Afeeya?" Maman Minal ta dakatar da ita, ta kalleta da idonta da suka fara canza kala tace
"To akan me Anty Zahra? Duk sanda magana zata haɗo akan Ahamd se Badar ta yimun gori a fakaice tace yafi ƙarfi na? ni na janyo shi nace ya soni ko yaya? Da yana da zuciya ma ai da bamu kai haka tare ba saboda na nuna masa bana muradinsa ta duk hanyar data dace amma ya nace ya kafe so takeyi na aureshi Alhalin danginsa basa ƙaunata? Ba'a a kunnenta ƙaninsa yayi mun cin mutunchi ya zagi iyayena sannan ta dage sena cusa kaina inda Allah be kaini ba saboda kwadayin abin duniya?
Toni kudinsa ko wani matsayi nasa ba zasu rufe mun ido ba su sa na jefa rayuwata cikin ƙunci na rayu da mutanen da basa so na, idan tana sonsa gashi nan na bar mata ta aureshi itace daidaishi" ta ƙarasa tana Ƙoƙarin riƙe kukan daya taho mata amma ta kasa dole ta sakeshi ta doshi Ƙofa zata fita amma mutanen da suka tsatstsaya munafunci yasa ta fasa fitar ta shige bayan Ummi da ke zaune ta kasa cewa komai ta kwanta tana kuka.
Maman Minal ta kulle Ƙofar jiki a sanyaye kafin ta zauna tana cewa
"Daga zancen tuwo shikenan se tashin hankali? da alama sheɗan ya shigo ya laɓe a ɗakin nan shiya haɗa komai kuma bazeyi nasara ba in sha Allah".
Badar da jikinta yayi sanyi laƙwas ta zauna daga tsayuwar da tayi ta kasa cigaba da masifar tata. Har ga Allah ita batayi magana da manufar da Afeeya ta ɗauka ba, ta riƙi Afeeyar a matsayin yar uwa shiyasa har take son cigabanta take kuma son ta da Ahmad ganin cewar mutumin kirkine ya na da duk wasu qualities da mace zata so a gurin Namiji gashi yana sonta baya ga haka wlh ita bata da wata manufa ta daban akan maganar.
Dakin ya ɗauki shiru se shasheƙar kukan Afeeya, kowa da tunanin da take a ranta wayarta ta sake ɗaukar ƙara lambar dazun ce bacin ran da take ciki yasa ta kashe wayar gaba ɗaya ba tareda na amsa kiran ba. Ranar har dare dukkansu basu da walwala shiru ɗakin kamar anyi mutuwa, tsakaninta da Badar kuwa se kallo seda Baffa ya kira wayarta akan be samu ta Afeeyan ba sannan nema ta tuna data kashe wayar tata, data miƙa mata bata kar ɓa ba, ta kunna tata ta kirashi.
Sururat ce ta saka su shirin dole cikin daren bayan ta dawo Ummi da Maman Minal suka tsara mata abinda ya faru ta ringa masifa ta kuma É—orawa Afeeya laifi kacokan wannan yasa suma sauran suka buÉ—e baki tare da nuna cewar ita ce bata kyauta ba su da kyakykyawar niyya suke tare da ita kuma wannan tasa har suke son abinda suke ganin ze zamar mata Alkhairi ba wani abu ba.
Bata so aja maganar da tsaho dan haka nace taji ta kuma bawa Badar haƙuri kamar yanda Sururat tayi insisting.
"Wlh Afeeya ina jinki kamar Yah Yusra, idan har zan iya aure ko soyayya da Mijinta to zanyi da Ahmad. Son da yake miki da kamalarsa tasa har nake miki sha'awar auransa dan nasan irinsa basu da yawa a duniyar yanzu amma tunda har zuciyarki tana raya miki wani abu daban akan niyyata in sha Allahu zan kama kaina, bazan sake yi miki wata magana data shafeshi ko ma akan saurayi ba gaba ɗaya. Zanci gaba dayi miki Addu'a Allah ya zaɓa miki abinda yafi Alkhairi" Badar din ta faɗa bayan da Afeeya ta bata haƙurin,
jikinta yayi sanyi ganin yanda idonta ke zubar kwalla sanda take maganar, ta tabbata har ranta gaskiya take faɗa kuma Badar na sonta kamar yanda ita ma take sonta amma abune yazo da rashin fahimta dukkan su kowa tana da dalilanta na so ko Ƙin tarayyata da Ahmad amma ta haɗiye nata za kuma ta cigaba da addu'a Allah ya fiddo mata da Mijinta daidai ita ya fiye mata sauƙi.