← Book details Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 55 OF 71

Sashe 55

Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Komawa yayi kan kujerar daya tashi yana kallon yanda take kokawa da numfashinta tana zare ido.
"Kizo ki zauna" ya faɗa yana nuna mata kusa dashi, ta maƙale masa kafaɗa. Da wani mayaudarin sauti bayan daya saka idonsa cikin nata yace
"Please Afeenah". Yanda kasan ya jata da magnet haka ta fara takawa dukda can ƙasan ranta wani irin tsoro da kokontonsa ne ya shigeta, karo na farko kenan a rayuwarta da makamancin haka ya faru da ita. Namiji Baligi ya runguneta harya ɗaga ta sama tayi tantiran Samari kala kala amma babu Wanda Allah ya bawa sa'ar kwatanta mata irin wannan abun sw Jay. Bawan Allah Ahmad ya faɗo mata a rai, a shekara uku sau ɗaya fatar hannunsa ta taɓa haɗuwa da tata shima bada niyya ba, ko hoto zasuyi basa tsayuwar da jikinsu ze gogi juna...

"I said I'm sorry fa, menene kum duk fuskarki ta canza or you are mot happy to see me?" Jay ya sake marairaicewa yana faÉ—a yatsunta guda goma cikin nasa yana murzawa, bata san sanda harya kama hannun ba seda ya fara magana ta ankare.

"Jayyy, babu kyau, don't touch me again" ta faɗa kamar zata rusa masa kuka bayan data zame hannayenta daga nasa. Yayi wani mayaudarin murmushi kafin yaja baya ya zauna dakyau seya tallafe fuskarsa da hannu biyu ya zuba mata iso, irin kallon ƙurillar. Ƙasa tayi da kanta dan bazata jure wannan kallon ba bayan abubuwan daya yi mata,
"Kinfi kyau a fili, kinfi kyau a kusa" ya faÉ—a yana kai hannunsa ya shafa fuskarta, ta tura baki da sauri yace
"Don't do that again ki bari ba yanzu ba se kin zama halalina don't make me loose my self Afeeyah you won't like me".

Da sauri ta miƙe daga inda take zaune saboda yanda yayi maganar daidai nan Salaha ta turo ƙofa janye da Food Trolley. Akan kantamemen centre table da yake tsakiyar falon ta shiga jere abubuwan data kawo bayan data gaida Jafar. Seda ta gama tas ta fita har sannan Afeeyah na tsaye dan gaba ɗaya Jafar ɗin ya tsoratata.

"Ki zauna wlh bazan sake taɓa ki ba" yayi magana yana mata murmushi, gabanta ya yanke ya faɗi, sautin muryarsa da murmushin da yayi taga sun rikiɗe mata ya koma kamar Ahmad. A sanyaye ta zauna kan kujerar da ke can nesa dashi. Yan kallonta yace

"Ko gaisawa bamuyi ba duk na tsorataki, anya ma kuwa zaki iya dani yarinyar nan naga alama tsoro ne dake sosai".

"Ina wuni" ta faɗa a sanyaye tana ƙoƙarim kauda tunanin Ahmad daya ziyarceta. Seda Jay yayi dagaske kafin ta sake ba duka ba dan salon daya zo mata dashi yasa ta ɗarare ga Ahmad dake ta mata yawo a zuciya. Shiya ringa janta da hira tana amsawa se yayi shiru fuskarsa ta canza nan da nan hankalinta ya tashi ta shiga tambayarsa meya faru.

"I said I'm sorry amma from the way you are behaving kamar bakiyi mun uzuri ba. Kasa riƙe kaina nayi nace bazan sake ba in sha Allah amma kalla ko magana ma ni kaɗai nakeyi daman saboda ki ɓata mun rai kika damu nazo" ya wani haɗe fuska kamar gaske aiko ya tayar mata da hankali yanda ya tsammata se gashi ta buɗe baki tana bashi haƙuri yana shan ƙamshi daga nan kuma suka koma normal suka fara hira irin yanda suka saba a waya. Duk abinda tace ita ta girka da kanta ya taɓa kaɗan Chinese rice da tayi da wani Chicken wings yace ta masa packaging zeje gida da shi. Seda aka kira Magriba kafin suka rabu yace zeje masallacin daya gani a farkom dake layin yana fita ya tarar da taron jama'ar da Mu'az ya haɗa a wajen gidan dan megadi ya hanasu shiga.

Yaran unguwa Abokanansa ya ringa bi gida gida yana ce musu ga Jay a gidansu suka taho harda manya marasa abinyi za'ace ko kuwa tsabar sonJay yasa suka yarda da maganar Mu'az É—in shi kuma Malam Sa'idu ya hanasu shiga dan daman ba kirki ya cika ba. A falonya koma yayi sallar dan baze fita ba,bayanya idar ya kirata tace gata nan tareda Anty Sauda zasu gaisa.

A mutunce tamkar tanayi dashi Anty Saudan suka gaisa yana jan Amani data liƙe mata suka fito tare bayan sun ƙare gaisuwar ta barshi da Afeeyah suka ƙarasa magana. Jikinsa ya sake janta ya shiga ɗaukansu pictures wanda duk ta kare fuskarta da hannu ba'a ganinta. Tana ƙunƙuni suka fita ta rakashi jikin motarsa ya fitar mata da tsarabar daya kawo mata.

"Bangaji da ganinki ba, kamar karna tafi" ya faɗa yana binta da kallo daga sama zuwa ƙasa kamar Maye. Tayi shiru tana wasa da zoben hannunta, yayi murmushi ya sake cewa
"Se yaushe, yaushe zanje na gaida su Baffah?"
"Yace from today to friday" ta bashi amsa a sanyaye tana tuna kalaman Baffa. Yanzu ace ya san Jafar ya kakkamata haka ai babu ma zancenya bashi auranta tasan cewa zeyi bashi da tarbiyya, ta dai yi masa uzurin kasancewarsa Rainon turai a gurinsu wannan ba wani abu bane su.

"Ok, wednesday yayi?" Ya tambaya yana É—age mata gira, ta gyaÉ—a kai, ya yashi daga kishingiÉ—ar da yayi jikin mota yace
"Gobe anan zan sameki ko gidanku?"
"Gobe ma zaka dawo?" Ta tambaya tana ware ido,
"Ko kar nazo kin gaji dani?" Ya mayar mata tambayar yana buɗe ido yanda tayi se tayi ƙasa da nata tana murmushi tace
"Aa"
"Don't worry, I'm not going to touch you again tunda naga raguwa ce ke".

Yanda yayi maganar yasa taji kamar ta nitse a gurin da take tsaye, Ƙarara zaka fahimci da biyu yayi maganar musamman murmushin da yakeyi da irin kallon dayake binta dashi seta juya da sauri ta shige gida. Me gadi ya bawa Boxes ɗin ya shigar mata dasu bayan ya masa ihisani ya wuce gida cikin nishaɗi jama'ar da Mu'az ya tara kuwa hannu kawai ya ɗaga musu suka ringa ihu har seda matan cikin gida suka fara zaburowa sunayin waje suga meya faru shidai tuni ma yabar layin ya kama hanyar gida. A traffic ya shafa Aljihunsa yaji kwalbar turaren daya ɗauka a safe ɗin Yah Ahmad, ya zaroshi ya kai hancinsa ya shaƙi ƙamshin, hannunaa na hagu ya shanshana wanda ya fi amfani dashi gurin riƙe Afeeyah ba hannun kaɗai ba duk jikinsa har motar ma ta kama ƙamshin turaren da yake da yaƙinin na jikinta ne dan ya shaƙe shi yanda ya kamata lokacin daya ɗagata sama.

Daya kasa gane abinda yake so ya tantance se kawai ya ajiye turaren a gefenshi, ta yuwu yanda ya shaƙeshi a gida da daɗin daya masa yasa yaji kamar shine a jikinta. Da wannan tunanin ya aminta yaci gaba da tuƙi yan tuno ta harya isa gida ganin motar Ahmad yasa ya wuce ɗakinsu ba tareda ya shiga cikin gida ba dukda tun yana gurin Afeeyah yaga kiran Hajiya, yanzu a hanya ma ta sake kira.
PAGE 20
Ranar laraba kamar yanda sukayi da Afeeyah tun safe yake shirin zuwa gaida Mahaifita. Ya jawa Ahmad kunne akan kar a maimaita ta wancan ranar, dawowa da yayi ya tarar dashi ba lafiya nema ya rage kaifin Mitar da yayi niyyar dasa masa.

"Zaka rakani gidansu Fatima biko nima" Ahmad ya faɗa masa. Jay ya taɓe baki, ya lura kamar sun samu matsala da Fatiman dan beji ya kirata ba kuma sukukun da ya ganshi yasan baya rasa nasaba da rashin shirunsu Allah yasa dai abinda ya faru ya saka ya haƙura da auranta kowa ya huta.

BayanSallar Magrib suka shiryi tafiyar dan Jafar baya ditar rana muddinba hayaniya da cunkoso yake so ya haɗa ba. Tsaf suka shirya kamar tagwaye, kaya iri ɗaya suka saka Shadda Cream Color ta karɓi jikin kowanne duk iya hassadar mutum sedai ya kallesu yace Tabarakallah badai ya kushe shigar wani daga ciki ba. Jafar ya sake jefa turaren jiya a Aljihu dan karya manta. Suka jero suna tafiya Ahmad na tsokanarsa har suka zo daidai part ɗin Alhaji.

"Ba zaka shiga kayiwa Hajiya Sallama ba?" Ahmad ya tambayeshi se yayi saurin cewa
"Kai Aa muje kawai, tun fa dana dawo maganar da take tayi mun kenan wacece nake so a ina nake neman Aure, kasan matsaltsalun Hajiya yanzu setace ba haka ba shiyasa nake so ayi komai a sirrince se an kai kuÉ—i idan Allah yasa an É—aura auran kawai se taji labari".

Ahmad ya ringa dariya yana cewa
"Lallai ka shahara, to wlh na barka da Allah idan ka janyo mun magana dan cewa zatayi ni na zugaka ka ɓoye mata"

"Ina zakuje haka?" Muryar Alhaji Audu daya fito da shirin fita masallaci ta dakatar dasu. Ko wanne ya tsume kafin suka shiga gaishe shi.
"Se ina haka kuka kafa huluna kamar sababbin Angwaye?" Alhaji ya tambaya. Ahmad ne ya bashi amsa yana shaf kai yace

"Gaisuwar surukan Jafar zamuje". Kamar Alhajin zece wani abu daga yanayin kallon daya bisu dashi se kuma ya canza da cewa
"Amma da kun jira kunyi sallar Isha'i a Jam'i ba lallai inda zakuje ku tarar basu idar ba" ya wuce is suka bishi a baya. Bayan an idar da sallah suka sake rankayowa tareda Alhajin suka shiga gida. Har Ahmad ya tada mota Balarabe guda daga ma'aikatan yaje da sauri yace masa Alhaji na magana seya bar motar a kunne ya wuce yanajin JafdaƘƙƊƘananun tsaki, har mamakin irin zumuɗin da yakeyi akan yarinyar yake kamar ba Jafar da Mata ne suke zigilli akansa ba se gashi wata ta zargeshi tsaf tana ja a ƙasa.

"Yanzu na samu waya Alhaji Munzali yayi hatsarin mota kuma jikin babu daÉ—i ina so naje na ganshi" Alhaji ya faÉ—a bayan da Ahmad yaje. Cikin jimami yayiwa Abokin Alhajin jaje da fatan samun lafiya. Alhaji ya sake cewa

"Bari na shiryo seka rakani mu duba shi" ya wuce sama ba tareda ya jira amsarsa ba. A waya Ahmad ya kira Jafar ya shaida masa, ya fara balbalin bala'i,
"Ai se kazo ka sameshi da kanka ka tuna masa fita zamuyi, nasan ba mantawa yayi ba yana sane tunda ya buƙaci na kaishi kayi haƙuri kawai kaje ma koma tare wani lokacin" Ahmad ya faɗa da Jafar yace wai ya gayawa Alhaji fita fa zasuyi.
Chapter 55 · 0% Book details