Sashe 1
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

NAGODE
BOOK 2
PAGE 1
"Alhaji! Alhaji!! Alhaji!!!" Taratsi da kwaroroton Binta ya maido shi daga cikin duniyar tunanin daya lula. Ya yunƙura ya zauna da kyau yana cije baki saboda yanda bayansa ya ƙage, baya iya dogon zama tun Hatsarin daya samu shekaru goma da suka wuce a hanyarsa ta zuwa Kaduna Jana'izar Alhaji Zakariyya Mahaifin Binta shikenan yake fama da Baya dukda iyakar bincike ance babu abinda ya samu bayan nasa amma kam yana ji a jikinsa ga kuma shekaru da suka miƙa wannan yana daga abinda yake ƙara ta'azzara masa ciwon.
"Alhaji lafiya kuwa? Nakusa minti goma tsaye akanka ina magana kayi shiru badan idonka a buÉ—e yake bama ai É—auka zanyi ka mutu" Bintan ta sake faÉ—a tana zama a gefensa. Ya tsura mata ido, ya rasa dalilin daya saka ranar Allah ba zata fito ta koma ba tareda Binta ta kawo zancen mutuwarsa ba, ya rasa meya tsare mata a duniya da take cike da burin taga ya kau.
"Kaci abinci ma kuwa? Koda yake la'asar sakaliya yaci ace kaci abincin rana ai" tayi tambaya kuma ta bawa kanta amsa tana tashi tsaye ta nufi firjin dake cikin Makeken Bedroom ɗinsa me kama da Turakar wani sarki. Ruwan gora ta ɗauko da Kofin tangaran da suke jere a saman firjin ta dawo ta zauna tana tsiyaya masa data gama ta miƙa masa babu musu ya karba dan yana buƙatar ruwan.
"Ya kukayi to? An samu kuɗin sun fito?" Ta jefa masa ainihin maganar data shigar da ita gurin nasa. Ya kurɓe ruwan yana gyara zama yace
"Ba'a samu ba, yace besan inda suka shiga ba kuma na yarda Aminu baze yimun sata ba dan haka maganar ta ƙare dukma wanda yayi sama da faɗi dasu shida Allah kuma a sannu wata rana asirinsa ze tonu"
"Kace me? Miliyan dubu dari biyun harda ɗori kake cewa kabar mutum da Allah akanta Lallai ma Alhaji, tsaya ma, yanzu kai har kana da bakinda zaka shaidi Aminu? Yaushe ka zauna dashi da har kasan halinsa da zakace bazeyi maka sata ba?" Binta tayi maganar a zabure. Alhaji Audu ya kalleta sheƙeƙe yace
"Waini nawane kasonki cikin kuÉ—in nan Binta da duk kika bi kika tashi hankalinki kamar ma kin fini damuwa da abinda ya faru?"
"Ni kuwa nake da kaso a ciki, karka manta Yara goma na ƙyanƙyashe maka a gidan nan ga Takwas nan a raye cikinsu kuma Zarata shida duk mazane kaga kuwa ni nake da Kaso a cikin dukiyarka kuma bazan zuba ido ina kallo a ringa damfararmu sannan kayi shiru kace ka bar mutum da Allah ba" ta bashi amsa tana kaɗa jiki tareda juya ido kamar wata ƙaramar yarinya, ya buɗe baki ze bata amsa sallamar Momy ta dakatar dashi seya haɗiye abinda yayi niyyar faɗa ɗin ya amsa sallamar ta ƙaraso ciki hannunta ɗauke da ƙaton Try. Akan Centre table dake tsakiyar ɗakin ba tareda ta nuna tasan da zaman Binta a gurin ba ta kalli Alhajin fuska babu yabo babu fallasa tace
"Ai bansan ka dawo ba seda nake nake cewa shiru kace kuma ba daÉ—ewa zakayi ba sannan Baba Bilki tace ai ko taji shigowarka tunÉ—azun ta zata na sani shiyasa batayi mun magana ba" abincin ta shiga zubawa ta gama jere komai ta sauke kulolin daga kan Teburin sannan ta tura masa shi gabansa yanda zeji dadin cin Abincin. Wani ruwan ta sake dakkowa daga firji ta ajiye masa Binta dai kallonta take tana zare ido a ranta tana tunanin wai ya akayi ta gaza korar wannan sailubar matar har suke dosar shekaru Arba'in tare a matsayin Kishiyoyi?
"Bari nayi sallar La'asar se naci abincin" Alhaji Audu ya faɗa kafin ya yunƙura ya shige banɗakin dake manne da ɗakin barcin nasa. Momy ta zauna kan doguwar kujera kwaya ɗaya dake cikin ɗakin Hajiya kuma har sannna tana zaune kan gado tana ƙarewa Momyn kallo kamae wata farin shigar Maita har Audu ya fito ya tada sallah ya idar ya hau kan abincinsa Binta na zaune ita kuma Momy bata ce mata ta fita ba dukda zaman nata ya ɓata mata rai. Har a yanzu da shekaru suka miƙa tsakanin ita ko Rabi babu wadda ta isa ta shiga Turakar Alhajin a ranakun girkin Hajiya Binta amma ita ko a kwance suke tana iya faɗo musu a yanzu ne kuma Alhaji Audun yake son ya gyara wannan barakar har yake ƙoƙarin taka mata burki wasu lokutan sedai a banza domin ta rigada ta raina shi, bashi da wani kwarjini ko Martaba a idonta da zw ce tayi abu tayi ko ya hanata ta hanu har ila yau kuma zancen tayi laifi ya mata faɗa kamar yanda yake musu fa babu shi, ita lamarin Alhaji da Hajiya Binta ma har rasa matsayin da zata ajiye shi takeyi dan ko a labarai bata taɓa cin karo da Macen da take zuba sharafi a gidan Auranta irin Hakiya Bintan ba.
"Ina kin gaka abinda ya kawoki?" Muryar Audu ta ratsa kunnuwansu, Momy na danna waya ta ɗago so take ta fahimci dawa yake a cikinsu? Ita me girki ko kuwa Binta data zo ta tasasu gaba? Hamshaƙiyar kuwa ƙara gyara zama tayo dan a tsammaninta da Aishar yake seda ya sake maimaita maganar yana kallon idonta kafin ta ankare, ta buɗe baki zata faɗa masa ba dadi se kuma ta gimtse data tuna tanada shirin da take so ta cimma seta miƙe tsaye tana murmushi tace
"Ai to bari naje, duk na shafa'a ne wlh se naga kamar a Ɗakina nake". Tana dafda fita daga ɗakin wayar Momy tayi ƙara alamar shigowar kira, Hajiya ta fice amma ta coge a bakin ƙofa ta kasa kunne, abin ya rigada ya zame mata Ɗabi'a ko ace ciwo, gulma da Laɓe, tsabar yanda ta ɗorawa kanta bala'i ko a hanya take tafe taji wasu na ƙusƙus seta dakata ta kasa kunne ko ba zataji ko ta fahimci abinda suke faɗi ba, ga zargi da tsarguwa ko yayan cikinta taga suna magana seta tsargu da ita suke ko wani abun suke shiryawa.
A cikin É—akin kuwa a speaker Momy ta saka wayar saboda kunnenta dake mata ciwo kwana biyu bata kara wata a kunnen muryar Ahmad ta ratso wayar yana cewa
"Momy, kin masa maganar kuwa?"
"Tukunna dai, wai idan sauri kakeyi haka ka tareshi da kanka kayi masa maganar mana seni zaka mayar yar aikenka" ta bashi amsa. Daga waje Binta ta sake manna kunne a jikin ƙofa tunda taji muryar Ahmad da kuma cewar anyi magana wace maganace? Abinda take so kunnuwanta su zuƙo mata kenan.
Ahmad ya sake marairaicewa Momy yana cewa
"Haba sweet mother, haba rabin raina kinsan dai bazan iya tunkararsa ba kuma na gaya miki Jafar ya masa magana yace he will get back to us yanzun kusan one month kenan bamuji komai daga gareshi ba and time is really against me Momy, idan baze samu ta hanyar sa ba na sani na nemi wani Alternative ɗin kinji Mamana? Ya ƙarasa maganar kamar ze saka mata kuka yana idarwa kuma tari ya sarƙe shi"
"Bakaje Asibitin da nace kaje ba kenan?" Ta jefa masa tambaya ba tareda tabi ta kan maganar da suka fara ba, Ahmad da tarin ya tsagaita masa yace
"Naje wlh Momy an rubutamun magani na ma farasha, kiyi masa maganar yanzu dan Allah kinji"
"Zanyi" ta faɗa a taƙaice daga nan ta kashe wayar. Alh Audu na cin abincinsa kuma yana sauraron duk wayar da sukeyi tuni kuma ya fahimci zancen da tunin da Ahmad ɗin yake magiyar tayi masa. Ruwa yasha yana kallonta yace
"Shi baze iya zuwa ya sameni muyi magana ba se ya ringa turomun yan aike?"
"Wane shi? Wannan ai se Yayan gida Yayan So" ta bashi amsa hankalinta na kan wayarta se yayi shiru yana kallonta, a yan shekarun nan Aishar ta fara canzawa, idan tayi wani abun se yaga kamar ta fara gajiyawa dashi ne kamar me neman wani dalili da ze janyo saɓani a tsakaninsu. Ajiyar rai yayi yace
"Ai shikenan, kice masa gobe ya sameni a gidan Gona na Kwanar Dawaki se mu tattauna maganar kuma yazo da takaddun"
"Baka da lambar wayarsa kaima kenan?" Ta faÉ—a tana tsareshi da ido, tamke fuska yayi be kuma bata amsa ba ya shige banÉ—aki wanko hannu.
Tayi tsaki a ranta wani abu me ɗaci yana taso mata seta miƙe ta shiga tattara kwanukan daya gama dasu ta ɗora akan Try ɗin data kawo su ta fita. A bakin ƙofa sukayi kiciɓus da Hajiya dake dakon jiran a faɗi gundarin abinda take so taji buƙatar da Ahmad ɗin yake nema a gurin Alhajin da har yace ya sameshi a gidan Gona.
Kardai fa tufka take ta baya tana warwarewa tana nan tana haƙilon ganin sun danne komai Aisha ta ringa mata zagon ƙasa suna wawasa ita da Yayanta? Dole ta Ƙara saka idanu kenan akan harkar shige da ficen gidan da duk abinda yake faruwa wannan maganar ma da ba'a ƙarasa ba seta bi diddiginta tunda sunan Jafar ya fito a ciki shi zata tambaya dukda dai shegen Yaro ne ba lallai ya faɗa mata ba tunda sirrin ubansa Ahmad ne. Tana ganin Momyn ta ɗan diririce se kuma ta waske ta tura ƙofar irin dawowa ta sakeyi zata shiga. Momyn ta kaɗa kai kawai ta wuce, ba yau Hajiyar ta sababa Laɓe ya zame mata ɗabi'a.
Hajiya na ganin Momy ta sauka ta juyo itama ta fice dan akwai abinda yake a gabanta yanzu kafin ta juya takan zancen Ahmad ɗin, ɗakinta ta wuce ta tarar da YAKUBU na cin abinci, Hajiya ƙarama na tsaye gaban console mirror dake falon tana gyara ɗaurin kallabinta. Ganinta yasaka Binta sakin fuska ta washe haƙwaranta duka, guda biyu data sakawa Haƙorin Makka na zinari sunata ƙyalli, Umarar Bara da sukaje ta cire Asalin guda daya na bakinta daya cinye aka saka mata biyun.
NAGODE
BOOK 2
PAGE 1
"Alhaji! Alhaji!! Alhaji!!!" Taratsi da kwaroroton Binta ya maido shi daga cikin duniyar tunanin daya lula. Ya yunƙura ya zauna da kyau yana cije baki saboda yanda bayansa ya ƙage, baya iya dogon zama tun Hatsarin daya samu shekaru goma da suka wuce a hanyarsa ta zuwa Kaduna Jana'izar Alhaji Zakariyya Mahaifin Binta shikenan yake fama da Baya dukda iyakar bincike ance babu abinda ya samu bayan nasa amma kam yana ji a jikinsa ga kuma shekaru da suka miƙa wannan yana daga abinda yake ƙara ta'azzara masa ciwon.
"Alhaji lafiya kuwa? Nakusa minti goma tsaye akanka ina magana kayi shiru badan idonka a buÉ—e yake bama ai É—auka zanyi ka mutu" Bintan ta sake faÉ—a tana zama a gefensa. Ya tsura mata ido, ya rasa dalilin daya saka ranar Allah ba zata fito ta koma ba tareda Binta ta kawo zancen mutuwarsa ba, ya rasa meya tsare mata a duniya da take cike da burin taga ya kau.
"Kaci abinci ma kuwa? Koda yake la'asar sakaliya yaci ace kaci abincin rana ai" tayi tambaya kuma ta bawa kanta amsa tana tashi tsaye ta nufi firjin dake cikin Makeken Bedroom ɗinsa me kama da Turakar wani sarki. Ruwan gora ta ɗauko da Kofin tangaran da suke jere a saman firjin ta dawo ta zauna tana tsiyaya masa data gama ta miƙa masa babu musu ya karba dan yana buƙatar ruwan.
"Ya kukayi to? An samu kuɗin sun fito?" Ta jefa masa ainihin maganar data shigar da ita gurin nasa. Ya kurɓe ruwan yana gyara zama yace
"Ba'a samu ba, yace besan inda suka shiga ba kuma na yarda Aminu baze yimun sata ba dan haka maganar ta ƙare dukma wanda yayi sama da faɗi dasu shida Allah kuma a sannu wata rana asirinsa ze tonu"
"Kace me? Miliyan dubu dari biyun harda ɗori kake cewa kabar mutum da Allah akanta Lallai ma Alhaji, tsaya ma, yanzu kai har kana da bakinda zaka shaidi Aminu? Yaushe ka zauna dashi da har kasan halinsa da zakace bazeyi maka sata ba?" Binta tayi maganar a zabure. Alhaji Audu ya kalleta sheƙeƙe yace
"Waini nawane kasonki cikin kuÉ—in nan Binta da duk kika bi kika tashi hankalinki kamar ma kin fini damuwa da abinda ya faru?"
"Ni kuwa nake da kaso a ciki, karka manta Yara goma na ƙyanƙyashe maka a gidan nan ga Takwas nan a raye cikinsu kuma Zarata shida duk mazane kaga kuwa ni nake da Kaso a cikin dukiyarka kuma bazan zuba ido ina kallo a ringa damfararmu sannan kayi shiru kace ka bar mutum da Allah ba" ta bashi amsa tana kaɗa jiki tareda juya ido kamar wata ƙaramar yarinya, ya buɗe baki ze bata amsa sallamar Momy ta dakatar dashi seya haɗiye abinda yayi niyyar faɗa ɗin ya amsa sallamar ta ƙaraso ciki hannunta ɗauke da ƙaton Try. Akan Centre table dake tsakiyar ɗakin ba tareda ta nuna tasan da zaman Binta a gurin ba ta kalli Alhajin fuska babu yabo babu fallasa tace
"Ai bansan ka dawo ba seda nake nake cewa shiru kace kuma ba daÉ—ewa zakayi ba sannan Baba Bilki tace ai ko taji shigowarka tunÉ—azun ta zata na sani shiyasa batayi mun magana ba" abincin ta shiga zubawa ta gama jere komai ta sauke kulolin daga kan Teburin sannan ta tura masa shi gabansa yanda zeji dadin cin Abincin. Wani ruwan ta sake dakkowa daga firji ta ajiye masa Binta dai kallonta take tana zare ido a ranta tana tunanin wai ya akayi ta gaza korar wannan sailubar matar har suke dosar shekaru Arba'in tare a matsayin Kishiyoyi?
"Bari nayi sallar La'asar se naci abincin" Alhaji Audu ya faɗa kafin ya yunƙura ya shige banɗakin dake manne da ɗakin barcin nasa. Momy ta zauna kan doguwar kujera kwaya ɗaya dake cikin ɗakin Hajiya kuma har sannna tana zaune kan gado tana ƙarewa Momyn kallo kamae wata farin shigar Maita har Audu ya fito ya tada sallah ya idar ya hau kan abincinsa Binta na zaune ita kuma Momy bata ce mata ta fita ba dukda zaman nata ya ɓata mata rai. Har a yanzu da shekaru suka miƙa tsakanin ita ko Rabi babu wadda ta isa ta shiga Turakar Alhajin a ranakun girkin Hajiya Binta amma ita ko a kwance suke tana iya faɗo musu a yanzu ne kuma Alhaji Audun yake son ya gyara wannan barakar har yake ƙoƙarin taka mata burki wasu lokutan sedai a banza domin ta rigada ta raina shi, bashi da wani kwarjini ko Martaba a idonta da zw ce tayi abu tayi ko ya hanata ta hanu har ila yau kuma zancen tayi laifi ya mata faɗa kamar yanda yake musu fa babu shi, ita lamarin Alhaji da Hajiya Binta ma har rasa matsayin da zata ajiye shi takeyi dan ko a labarai bata taɓa cin karo da Macen da take zuba sharafi a gidan Auranta irin Hakiya Bintan ba.
"Ina kin gaka abinda ya kawoki?" Muryar Audu ta ratsa kunnuwansu, Momy na danna waya ta ɗago so take ta fahimci dawa yake a cikinsu? Ita me girki ko kuwa Binta data zo ta tasasu gaba? Hamshaƙiyar kuwa ƙara gyara zama tayo dan a tsammaninta da Aishar yake seda ya sake maimaita maganar yana kallon idonta kafin ta ankare, ta buɗe baki zata faɗa masa ba dadi se kuma ta gimtse data tuna tanada shirin da take so ta cimma seta miƙe tsaye tana murmushi tace
"Ai to bari naje, duk na shafa'a ne wlh se naga kamar a Ɗakina nake". Tana dafda fita daga ɗakin wayar Momy tayi ƙara alamar shigowar kira, Hajiya ta fice amma ta coge a bakin ƙofa ta kasa kunne, abin ya rigada ya zame mata Ɗabi'a ko ace ciwo, gulma da Laɓe, tsabar yanda ta ɗorawa kanta bala'i ko a hanya take tafe taji wasu na ƙusƙus seta dakata ta kasa kunne ko ba zataji ko ta fahimci abinda suke faɗi ba, ga zargi da tsarguwa ko yayan cikinta taga suna magana seta tsargu da ita suke ko wani abun suke shiryawa.
A cikin É—akin kuwa a speaker Momy ta saka wayar saboda kunnenta dake mata ciwo kwana biyu bata kara wata a kunnen muryar Ahmad ta ratso wayar yana cewa
"Momy, kin masa maganar kuwa?"
"Tukunna dai, wai idan sauri kakeyi haka ka tareshi da kanka kayi masa maganar mana seni zaka mayar yar aikenka" ta bashi amsa. Daga waje Binta ta sake manna kunne a jikin ƙofa tunda taji muryar Ahmad da kuma cewar anyi magana wace maganace? Abinda take so kunnuwanta su zuƙo mata kenan.
Ahmad ya sake marairaicewa Momy yana cewa
"Haba sweet mother, haba rabin raina kinsan dai bazan iya tunkararsa ba kuma na gaya miki Jafar ya masa magana yace he will get back to us yanzun kusan one month kenan bamuji komai daga gareshi ba and time is really against me Momy, idan baze samu ta hanyar sa ba na sani na nemi wani Alternative ɗin kinji Mamana? Ya ƙarasa maganar kamar ze saka mata kuka yana idarwa kuma tari ya sarƙe shi"
"Bakaje Asibitin da nace kaje ba kenan?" Ta jefa masa tambaya ba tareda tabi ta kan maganar da suka fara ba, Ahmad da tarin ya tsagaita masa yace
"Naje wlh Momy an rubutamun magani na ma farasha, kiyi masa maganar yanzu dan Allah kinji"
"Zanyi" ta faɗa a taƙaice daga nan ta kashe wayar. Alh Audu na cin abincinsa kuma yana sauraron duk wayar da sukeyi tuni kuma ya fahimci zancen da tunin da Ahmad ɗin yake magiyar tayi masa. Ruwa yasha yana kallonta yace
"Shi baze iya zuwa ya sameni muyi magana ba se ya ringa turomun yan aike?"
"Wane shi? Wannan ai se Yayan gida Yayan So" ta bashi amsa hankalinta na kan wayarta se yayi shiru yana kallonta, a yan shekarun nan Aishar ta fara canzawa, idan tayi wani abun se yaga kamar ta fara gajiyawa dashi ne kamar me neman wani dalili da ze janyo saɓani a tsakaninsu. Ajiyar rai yayi yace
"Ai shikenan, kice masa gobe ya sameni a gidan Gona na Kwanar Dawaki se mu tattauna maganar kuma yazo da takaddun"
"Baka da lambar wayarsa kaima kenan?" Ta faÉ—a tana tsareshi da ido, tamke fuska yayi be kuma bata amsa ba ya shige banÉ—aki wanko hannu.
Tayi tsaki a ranta wani abu me ɗaci yana taso mata seta miƙe ta shiga tattara kwanukan daya gama dasu ta ɗora akan Try ɗin data kawo su ta fita. A bakin ƙofa sukayi kiciɓus da Hajiya dake dakon jiran a faɗi gundarin abinda take so taji buƙatar da Ahmad ɗin yake nema a gurin Alhajin da har yace ya sameshi a gidan Gona.
Kardai fa tufka take ta baya tana warwarewa tana nan tana haƙilon ganin sun danne komai Aisha ta ringa mata zagon ƙasa suna wawasa ita da Yayanta? Dole ta Ƙara saka idanu kenan akan harkar shige da ficen gidan da duk abinda yake faruwa wannan maganar ma da ba'a ƙarasa ba seta bi diddiginta tunda sunan Jafar ya fito a ciki shi zata tambaya dukda dai shegen Yaro ne ba lallai ya faɗa mata ba tunda sirrin ubansa Ahmad ne. Tana ganin Momyn ta ɗan diririce se kuma ta waske ta tura ƙofar irin dawowa ta sakeyi zata shiga. Momyn ta kaɗa kai kawai ta wuce, ba yau Hajiyar ta sababa Laɓe ya zame mata ɗabi'a.
Hajiya na ganin Momy ta sauka ta juyo itama ta fice dan akwai abinda yake a gabanta yanzu kafin ta juya takan zancen Ahmad ɗin, ɗakinta ta wuce ta tarar da YAKUBU na cin abinci, Hajiya ƙarama na tsaye gaban console mirror dake falon tana gyara ɗaurin kallabinta. Ganinta yasaka Binta sakin fuska ta washe haƙwaranta duka, guda biyu data sakawa Haƙorin Makka na zinari sunata ƙyalli, Umarar Bara da sukaje ta cire Asalin guda daya na bakinta daya cinye aka saka mata biyun.