Sashe 57
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sukayi shiru for almost 10 mins shi yana kallonta ita kuma tana wasa da zoben hannunta zuciyarta na dakan lugude. Meya kawo canji a fuskar Jay? Abinda take tambayar kanta kenan.
"Afeeyah" taji ya kira sunanta ta ɗago a hanzarce kamar tana jira, idanunta da suka fara tara saboda tunane tunanen da takeyi ta sauke a cikin nasa daya zuba mata. Tana kallo ya taune Lips ɗinsa na ƙasa kafin ya kalli gefe alamu sun nuna maganganu ne a bakinsa bama magana ba amna ya haɗiye su se ya miƙe yana ƙaƙalo murmushin data tabbatar na yaƙene yace mata
"Muje ki rakani, kar Umma tace bani da kunya na shige mata falo nayi zamana". Yanda yayi maganar yasa dole ta murmusa lokaci ɗauke ƙwallar data ziraro mata duk akan idonsa. Ya cire rafar Kuɗin ɗazu ya ajiye a inda ya tashi kafin ya juya ya fara tafiya tabi bayansa tana cewa
"Ka ɗauki kuɗinka indai ba faɗa kake so ka janyo mun ba" be amsata ba ya sa kai ya fice. Umma na tsaye gaban ƙatoton Fridge ɗinta tana jera Gororin Zoɓo, dama yanzu take shiri a ranta ta leƙa falon se gasu sun fito. Jafar yayi mata sallama tace ya gaida mutanen gida ta juya taci gaba da aikinta Afeeyah tabi bayansa zalo zalo jiki a saluɓe.
A soro ya tsaya bayan ya tura ƙofar gidan ya jingina bayansa da ita ya harɗe hannu a ƙirji yana mata kallon da yake sakata faɗuwar gaba. Ko a mafarki be taɓa hasashen Afeeyan ta fito daga irin wannan gidan ba, ƙirarta, fatar jikinta, kwalliyarta basuyi kama dana wadda take rayuwa cikin wanna lokon ba. Abubuwa da yawa suke masa yawo a rai amma yayi ƙoƙarin furzo wanda yafi tsaya masa a rai da Baffanta yace masa akwai wanda ta daɗe tare dashi amma tace shi take so. Kamar saukar Aradu haka taji tambayar
"Wanene wanda Baffa yace kun daÉ—e tare dashi?".
Seda tayi dagaske kafin ta iya danne firgicinta ta saita kanta ta hanyar marairaice fuska, yanayin da tayin ransa a ɓace yake amma abin ya bigeshi se kawai ya ɗage kai sama yana shaƙa tareda furzar da iska me cakuɗe da Ƙamshin turaren da a yanzu ya tabbatar a jikinta yake jinsa.
"Kai da kanka kana cewa baze yuwu ace mace kamata na rasa saurayi ba, haka ne amma kuma babu wanda nake so cikinsu" ta faÉ—a cikin rawar murya
Idanunta akan fuskarsa, so takeyi ta fahimci abinda yake zuciyarsa amma yaƙi bayyanar da hakan. Zuciyarta ta sake tsinkewa sanda taji yace
"Bana son ƙarya Afeeyah na kuma tsani me yinta. I asked you everything that concerns you me yasa zaki ɓoye mun wannan? Kuma har Baffahnki yasan da zamansa tsakanin ni dashi wa kike shirin ki yaudara?"
"Amma kasan babu batun yaudara tunda har na kawoka gaban Mahaifina, idan ƙarya nakeyi maka bazan taɓa bari kaga tushe na ba zamu ƙare soyayyar mune kawai a waya ba zaka taɓa sanin inda zaka saneni ba idan na gama na sallameka"
"Shi da k ika fara kawowa shi kika yaudara kenan?" Ya tsareta da idanunsa da suka canza kala saboda abinda shi yaɗai yasan menene. Tayi shiru dan gani tayi kamar ze iya kwasa mata mari idan ta sakw faɗin wani abu. Ya dafa ƙofa yana nunata da yatsa yace
"Ki tabbatar da kin sallameshi, karna sake ganinki da duk wani abu daya dangance shi, i mean daga kan sutura, cosmetics har wayar hannunki ki cire Sim yanzu I'm going to send you another one. Ki nemi izini gobe or the next day I'm taking you out to shop, bana so na sake ganin duk wani abu daya siya miki a jikinki har wannan turaren da kike sakawa bana so na sake jinsa a jikinki".
Yanda kasan Ya da Uba haka yake nunata yana zazzaga mata maganganu, tunda take a rayuwarta bata tabajin ta tozarta irin na wannan lokacin ba, a tsaye take amma ji tayi inama ƙasa ta buɗe ta shige ciki ko kuma ta rufe idonta ta ɓace ɓat daga gurin. Maganganun Jafar suna nufin ita ko iyayenta basu isa su mallaka mata ire iren suturu da sauran kayayyakin da take ta'ammali dasu ba, yazo yaga gidansu dole ya samu bakin faɗa mata maganganu ai. Yanda yake magana fushin dake cikin muryarsa ya zarta ace iyakar na disappointment ne, ya wuce ace na ƙaryar da yake iƙirarin tayi masa ne tabbas da akwai wani abu daya tunzurashi bayan wannan.
Jiki a saluɓe ta shiga gida bayan daya sallameta ya tafi ta shige ɗaki ta faɗa kan katifarta tana sakin kuka me sautin da ta kasayi a gabansa se hawaye. Muryar Umma dake kwarara mata kira da hayaniyarsu Yaya Malam ta sakata dole ta tashi, seda ta wanko fuska a bakin famfo kafin ta shiga falon da suke.
"Wannan kuÉ—in fa na menene?" Umma ta tambayeta tana kallonta kafin ta Amsa Sanin Jay ya zaburo yana cewa
"Yana ina Afeeyah? Ni daman nasan ƙarya kakeyi haka kawai ina gurin Babyta ka tasoni yanzu kasa na faɗa mata magana yanzu nayi two zero, ni banyi hira da ita naji daɗi ka yaudareni da sunan Hero".
Malam daya sha wahalar nemo Sani ya galla masa harara yace
"Minti nawa nayi ina gararanba a lokon nan kowa yace besan inda kake ba? Amma dai ko ƙamshin da gidan nan yakeyi ai ya isa kasan yau anyi babban baƙo"
"Ji banza, wane kalar turarene Ahmad be baza mana a Lokon nan ba? Shifa idan yazo tun daga titi ake sanin ya iso gidan nan kuwa a Ƙalla yana kwana uku kafin ƙamshin ya gama bajewa" inji Sani Malam yace
"Zubairu" Umma ta daka musu tsawa jin zasu kaure da musun da suka saba tace au fita su bata guri tunda basu san sun girma ba.
Afeeyah na tsaye har sannan ta sake nuna mata kuÉ—in tana tambayar na menene
"Shine ya ajiye kuma seda nace masa ya É—auke zakiyi faÉ—a amma be jiba" ta bawa Umman amsa. Murmushin takaici Umma tayi tace
"Ba laifi ai tunda shi naga harya harbo jirginki da wurwuri ya fahimci mayadariya ce ke kuma makwaɗaiciya. Shi dayake free ne gashi nan ya buɗe miki ai ya nuna miki kar yake kallonki tunda dai yaga ubanki ya san bashi yake miki hidimar da tasa kike jin kanki kina goga kafaɗa da waɗanda suka tsere miki ba kinga ko auransa kikayi yasan ba dan Allah bane kin aureshi ne saboda abin hannunsa. Ko da dai banga wata sufa ta rashin da'a a tattare dashi ba amma ki sani inda kaso dari ya yarda dake daga kalamansa kin rasa kaso hamsin na ƙima da darajar da yake kallonki dasu ada in ma be zarce hakan ba.
Ga wanda kika daɗe tare dashi yana bauta miki yanzu da kika hango kazar data fishi maiƙo shine kika tubure akan kw baki taɓa cewa kina sonsa ba ai shikenan ni babu abinda zance miki tunda ubaki ya tsaya miki, Allah ya shige gaba" Umma ta faɗa kafin ta maida hankalinta kan Film ɗin Hausan da aka fara a Arewa. Afeeyah na tsaye tana hawaye, jin Umman tayi shiru ta fahimci ta gama maganarta. Wai dan Allah da wane yare zata fahimtar da Umma? Abinda take tambayar kanta bata da amsa dan haka cikin muryar kuka tace
"Kiyi haƙuri Umma"
"Da kika mun me ni kuma? Ai ke ya kamata na bawa haƙurin shiga rayuwarki da nakeyi, ni ai babu abinda zan sake cewa kuma Afeeyah ai magana ta ƙare tunda har kin turoshi kenan ba gudu ba jada baya kina kan bakanki shima kuma Malam naji ya bashi sati biyu ya turo, to dai ku tsananta bincike kar azo ayi abinda daga baya za'a ringa wlh tallahi" Umman ta sake magana, yanda tayi seka rantse da wata Ƙawa ko yar uwarta suke shawara akan auran wata, tamkar ba auran yar cikinta ake magana ba wai su tsananta bincike ita da Baffa kenan ta zame hannunta a ciki kai se a bar Umma dai.
Kuka Afeeyah ta fashe mata dashi tana zama a gurin
"Umma magana kikeyi fa tamkar kin zare hannunki daga cikin sabgata kina nufin nayi gaban kaina?" Ta faÉ—a cikin kuka, Umma tace
"Au wai baki sani ba tuntuni? Ai ni tun daga randa kika nuna mun kin girma, kin isa ki yankewa kanki hukunci na zare hannuna daga sabgarki Afeeya ai yanzu kece uwar kanki, abinda kike so ne kuma na barki da zaɓinki
Ke bakiyi ko rabin tashen da nayi a zamanin ƙuruciyata ba, ko rantsuwa nayi bazanyi kaffara ba soyayyar da kike iƙirarin kinawa wancan yaron batavkai zafin wadda nayiwa nawa muradin ran ba, da ace na zamo me kafiya da taurin kai irinki da ban auri ubanki ba har nazo na haifeki kika tsaya gabana kina faɗin ke ga wanda ranki yake so.
Ban fara son ubanki ba seda na zauna dashi domin daya ganni yace yana sona ya samu Mahaifina uffan ban tofa ba nabi abinda nawa uban ya zaɓar mun gashi naga ribar biyayyar danayi masa saboda shekara talatin da biyar Alhamdulillahi babu abinda zancewa ubangiji se godiya domin matsalolin aure sedai naji su gurin mutane badai a cikin gidana ba, ƙila dana bijire nabi zaɓin raina kamar yanda kike shirin aikatawa Allah kaɗai yasan takaicin da zan kwasa a tsayin shekarun nan" Umma tayi maganar cikin zafin rai. Afeeyah dai se kuka take Umman ta miƙe ta nufi Ƙofa tana cewa
"Kukan daɗi kikeyi, Allah ya gani iyakar yi mun kare mutunchinmu, se ki zuba ruwa a ƙasa kisha kin jawo mana abinda za'a yi damu, ba unguwar nan ba na tabbatar duk wanda yaji labarinmu seya zagemu shekara uku kina cinyewa yaro kuɗi yana miki hidima rana tsaka kice baki san zance ba Allah yasa yazo yace a biya shi se ki san ta inda zaki fara tattaro masa kaya da kuɗaɗen daya kashe miki"
"Afeeyah" taji ya kira sunanta ta ɗago a hanzarce kamar tana jira, idanunta da suka fara tara saboda tunane tunanen da takeyi ta sauke a cikin nasa daya zuba mata. Tana kallo ya taune Lips ɗinsa na ƙasa kafin ya kalli gefe alamu sun nuna maganganu ne a bakinsa bama magana ba amna ya haɗiye su se ya miƙe yana ƙaƙalo murmushin data tabbatar na yaƙene yace mata
"Muje ki rakani, kar Umma tace bani da kunya na shige mata falo nayi zamana". Yanda yayi maganar yasa dole ta murmusa lokaci ɗauke ƙwallar data ziraro mata duk akan idonsa. Ya cire rafar Kuɗin ɗazu ya ajiye a inda ya tashi kafin ya juya ya fara tafiya tabi bayansa tana cewa
"Ka ɗauki kuɗinka indai ba faɗa kake so ka janyo mun ba" be amsata ba ya sa kai ya fice. Umma na tsaye gaban ƙatoton Fridge ɗinta tana jera Gororin Zoɓo, dama yanzu take shiri a ranta ta leƙa falon se gasu sun fito. Jafar yayi mata sallama tace ya gaida mutanen gida ta juya taci gaba da aikinta Afeeyah tabi bayansa zalo zalo jiki a saluɓe.
A soro ya tsaya bayan ya tura ƙofar gidan ya jingina bayansa da ita ya harɗe hannu a ƙirji yana mata kallon da yake sakata faɗuwar gaba. Ko a mafarki be taɓa hasashen Afeeyan ta fito daga irin wannan gidan ba, ƙirarta, fatar jikinta, kwalliyarta basuyi kama dana wadda take rayuwa cikin wanna lokon ba. Abubuwa da yawa suke masa yawo a rai amma yayi ƙoƙarin furzo wanda yafi tsaya masa a rai da Baffanta yace masa akwai wanda ta daɗe tare dashi amma tace shi take so. Kamar saukar Aradu haka taji tambayar
"Wanene wanda Baffa yace kun daÉ—e tare dashi?".
Seda tayi dagaske kafin ta iya danne firgicinta ta saita kanta ta hanyar marairaice fuska, yanayin da tayin ransa a ɓace yake amma abin ya bigeshi se kawai ya ɗage kai sama yana shaƙa tareda furzar da iska me cakuɗe da Ƙamshin turaren da a yanzu ya tabbatar a jikinta yake jinsa.
"Kai da kanka kana cewa baze yuwu ace mace kamata na rasa saurayi ba, haka ne amma kuma babu wanda nake so cikinsu" ta faÉ—a cikin rawar murya
Idanunta akan fuskarsa, so takeyi ta fahimci abinda yake zuciyarsa amma yaƙi bayyanar da hakan. Zuciyarta ta sake tsinkewa sanda taji yace
"Bana son ƙarya Afeeyah na kuma tsani me yinta. I asked you everything that concerns you me yasa zaki ɓoye mun wannan? Kuma har Baffahnki yasan da zamansa tsakanin ni dashi wa kike shirin ki yaudara?"
"Amma kasan babu batun yaudara tunda har na kawoka gaban Mahaifina, idan ƙarya nakeyi maka bazan taɓa bari kaga tushe na ba zamu ƙare soyayyar mune kawai a waya ba zaka taɓa sanin inda zaka saneni ba idan na gama na sallameka"
"Shi da k ika fara kawowa shi kika yaudara kenan?" Ya tsareta da idanunsa da suka canza kala saboda abinda shi yaɗai yasan menene. Tayi shiru dan gani tayi kamar ze iya kwasa mata mari idan ta sakw faɗin wani abu. Ya dafa ƙofa yana nunata da yatsa yace
"Ki tabbatar da kin sallameshi, karna sake ganinki da duk wani abu daya dangance shi, i mean daga kan sutura, cosmetics har wayar hannunki ki cire Sim yanzu I'm going to send you another one. Ki nemi izini gobe or the next day I'm taking you out to shop, bana so na sake ganin duk wani abu daya siya miki a jikinki har wannan turaren da kike sakawa bana so na sake jinsa a jikinki".
Yanda kasan Ya da Uba haka yake nunata yana zazzaga mata maganganu, tunda take a rayuwarta bata tabajin ta tozarta irin na wannan lokacin ba, a tsaye take amma ji tayi inama ƙasa ta buɗe ta shige ciki ko kuma ta rufe idonta ta ɓace ɓat daga gurin. Maganganun Jafar suna nufin ita ko iyayenta basu isa su mallaka mata ire iren suturu da sauran kayayyakin da take ta'ammali dasu ba, yazo yaga gidansu dole ya samu bakin faɗa mata maganganu ai. Yanda yake magana fushin dake cikin muryarsa ya zarta ace iyakar na disappointment ne, ya wuce ace na ƙaryar da yake iƙirarin tayi masa ne tabbas da akwai wani abu daya tunzurashi bayan wannan.
Jiki a saluɓe ta shiga gida bayan daya sallameta ya tafi ta shige ɗaki ta faɗa kan katifarta tana sakin kuka me sautin da ta kasayi a gabansa se hawaye. Muryar Umma dake kwarara mata kira da hayaniyarsu Yaya Malam ta sakata dole ta tashi, seda ta wanko fuska a bakin famfo kafin ta shiga falon da suke.
"Wannan kuÉ—in fa na menene?" Umma ta tambayeta tana kallonta kafin ta Amsa Sanin Jay ya zaburo yana cewa
"Yana ina Afeeyah? Ni daman nasan ƙarya kakeyi haka kawai ina gurin Babyta ka tasoni yanzu kasa na faɗa mata magana yanzu nayi two zero, ni banyi hira da ita naji daɗi ka yaudareni da sunan Hero".
Malam daya sha wahalar nemo Sani ya galla masa harara yace
"Minti nawa nayi ina gararanba a lokon nan kowa yace besan inda kake ba? Amma dai ko ƙamshin da gidan nan yakeyi ai ya isa kasan yau anyi babban baƙo"
"Ji banza, wane kalar turarene Ahmad be baza mana a Lokon nan ba? Shifa idan yazo tun daga titi ake sanin ya iso gidan nan kuwa a Ƙalla yana kwana uku kafin ƙamshin ya gama bajewa" inji Sani Malam yace
"Zubairu" Umma ta daka musu tsawa jin zasu kaure da musun da suka saba tace au fita su bata guri tunda basu san sun girma ba.
Afeeyah na tsaye har sannan ta sake nuna mata kuÉ—in tana tambayar na menene
"Shine ya ajiye kuma seda nace masa ya É—auke zakiyi faÉ—a amma be jiba" ta bawa Umman amsa. Murmushin takaici Umma tayi tace
"Ba laifi ai tunda shi naga harya harbo jirginki da wurwuri ya fahimci mayadariya ce ke kuma makwaɗaiciya. Shi dayake free ne gashi nan ya buɗe miki ai ya nuna miki kar yake kallonki tunda dai yaga ubanki ya san bashi yake miki hidimar da tasa kike jin kanki kina goga kafaɗa da waɗanda suka tsere miki ba kinga ko auransa kikayi yasan ba dan Allah bane kin aureshi ne saboda abin hannunsa. Ko da dai banga wata sufa ta rashin da'a a tattare dashi ba amma ki sani inda kaso dari ya yarda dake daga kalamansa kin rasa kaso hamsin na ƙima da darajar da yake kallonki dasu ada in ma be zarce hakan ba.
Ga wanda kika daɗe tare dashi yana bauta miki yanzu da kika hango kazar data fishi maiƙo shine kika tubure akan kw baki taɓa cewa kina sonsa ba ai shikenan ni babu abinda zance miki tunda ubaki ya tsaya miki, Allah ya shige gaba" Umma ta faɗa kafin ta maida hankalinta kan Film ɗin Hausan da aka fara a Arewa. Afeeyah na tsaye tana hawaye, jin Umman tayi shiru ta fahimci ta gama maganarta. Wai dan Allah da wane yare zata fahimtar da Umma? Abinda take tambayar kanta bata da amsa dan haka cikin muryar kuka tace
"Kiyi haƙuri Umma"
"Da kika mun me ni kuma? Ai ke ya kamata na bawa haƙurin shiga rayuwarki da nakeyi, ni ai babu abinda zan sake cewa kuma Afeeyah ai magana ta ƙare tunda har kin turoshi kenan ba gudu ba jada baya kina kan bakanki shima kuma Malam naji ya bashi sati biyu ya turo, to dai ku tsananta bincike kar azo ayi abinda daga baya za'a ringa wlh tallahi" Umman ta sake magana, yanda tayi seka rantse da wata Ƙawa ko yar uwarta suke shawara akan auran wata, tamkar ba auran yar cikinta ake magana ba wai su tsananta bincike ita da Baffa kenan ta zame hannunta a ciki kai se a bar Umma dai.
Kuka Afeeyah ta fashe mata dashi tana zama a gurin
"Umma magana kikeyi fa tamkar kin zare hannunki daga cikin sabgata kina nufin nayi gaban kaina?" Ta faÉ—a cikin kuka, Umma tace
"Au wai baki sani ba tuntuni? Ai ni tun daga randa kika nuna mun kin girma, kin isa ki yankewa kanki hukunci na zare hannuna daga sabgarki Afeeya ai yanzu kece uwar kanki, abinda kike so ne kuma na barki da zaɓinki
Ke bakiyi ko rabin tashen da nayi a zamanin ƙuruciyata ba, ko rantsuwa nayi bazanyi kaffara ba soyayyar da kike iƙirarin kinawa wancan yaron batavkai zafin wadda nayiwa nawa muradin ran ba, da ace na zamo me kafiya da taurin kai irinki da ban auri ubanki ba har nazo na haifeki kika tsaya gabana kina faɗin ke ga wanda ranki yake so.
Ban fara son ubanki ba seda na zauna dashi domin daya ganni yace yana sona ya samu Mahaifina uffan ban tofa ba nabi abinda nawa uban ya zaɓar mun gashi naga ribar biyayyar danayi masa saboda shekara talatin da biyar Alhamdulillahi babu abinda zancewa ubangiji se godiya domin matsalolin aure sedai naji su gurin mutane badai a cikin gidana ba, ƙila dana bijire nabi zaɓin raina kamar yanda kike shirin aikatawa Allah kaɗai yasan takaicin da zan kwasa a tsayin shekarun nan" Umma tayi maganar cikin zafin rai. Afeeyah dai se kuka take Umman ta miƙe ta nufi Ƙofa tana cewa
"Kukan daɗi kikeyi, Allah ya gani iyakar yi mun kare mutunchinmu, se ki zuba ruwa a ƙasa kisha kin jawo mana abinda za'a yi damu, ba unguwar nan ba na tabbatar duk wanda yaji labarinmu seya zagemu shekara uku kina cinyewa yaro kuɗi yana miki hidima rana tsaka kice baki san zance ba Allah yasa yazo yace a biya shi se ki san ta inda zaki fara tattaro masa kaya da kuɗaɗen daya kashe miki"