← Book details Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 38 OF 71

Sashe 38

Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Duk ku ba zaku gane ba"
"Daman ba zamu gane ba mana se ke da kika sakawa kanki abinda yafi ƙarfinki kece zaki gane ai" Islam ta faɗa. Afeeyah tayi shiru me tsayi tana saƙa da warwara. Tabbas auran Ahmad ze fi zama abu me sauƙi fiye dana sabon masoyinta. Amma Jafar take so, ta yarda zuciyarta ta mace akansa Ahmad kuwa koda ta aureshi sedai ta zauna dashi tukuicin kyautatawarsa gareta da iyayenta. Cikin rauni tacewa Islam

"Amma yana sona, shifa ya tareni kuma ya nemi number na ya kirani yace yana sona aurena zeyi"
"Shi wa?"
"Jafar"
"Afeeyah kenan, daman zece yana sonki mana, kuma zata yuwu da gaske yakeyi amma kuma ba iyakar son ba kiyi tunanin me soyayyar zata haifar miki? Amma tayaya za'ayi mutumin daga haÉ—uwa lessthan sati guda ki kamu da soyayyarsa har haka? Ko daman kin sanshi ne?" Islam ta tambayeta. Ta rintse ido fuskar Jafar nayi mata gizo kafin ta buÉ—e tace
PAGE 14

"Ban san shi ba ban kuma taɓa ganinsa ba se ranar. Ni kaina Islam bansan ya akayi ba na kamu da sonsa har haka ba. Ta yuwu kodan yayi daidai da tsari da kuma mafarki na akan Abokin rayuwa shiyasa"

"Kiyi addu'a idan da Alkhairi a tsakaninku Allahya tabbatar amma ki cire son rai a yayin da zaki nemi zaɓi a gurin Allah kuma ki dena wannan halin na zargin wata zata kwace miki abinda kike so sannan ki lallaɓa Badar wlh Afeeyah samun mutum da ze soki tsakani da Allah kamar ita a yanzu yana da wahala"

"To ni yanzu taya zan bata haƙuri kinsan dai Badar sanda kake lallaɓata sannan zata botsare ta fara rashin mutunchi ni kuma ba zan jure ba sena tanka mata"

"Tunda kece baki da gaskiya kuwa haka zaki yi shiru ko zaginki zatayi, yanzu ki kirata tazo nan ku sasanta tun wuri ma ba se kun koma ɗaki ku sake raba hali ba a ringa yawo daku a baki" Islam ta sake faɗa ta kalleta da son jin ƙarin bayani ta yamutsa fuska tace
"Eh mana, ce miki akayi duk wanda kake dariya dashi me sonka ne tsakani da Allah? A aji ranar ina jin Ummi na hirar kuna ce mata tana yawo bayan kuma abinda kukeyi kenan ko kuwa samarin da suke kashe muku kuɗi ƙannen babanki ne da zasu ringa muku bauta ba tareda suna benefiting komai a gurinku ba"

Take ta sake hasala tace
"Ita Ummin take cewa haka?"
"Bana faÉ—a miki bane saboda kije kiyi tashin hankali, ke matsalarki kenan bakya cin ribar zance da an faÉ—i abu kamar wuta fuu zaki tashi se daga baya kizo kina regretting action naki I'm only telling you so that kusan zaman da kukeyi da kowa kuma ba komai zakuci gaba da sakin baki duk sirrinku kuyi ta faÉ—a a É—aki ba, ai dai tun muna tare nake muku wannan faÉ—an daga ke har Badar kun fiya saurin yarda da mutane baku da sirri".

Tilas ta kira Badar dan ta yarda da gaske bata kyauta ba ta ringa bata haƙuri bayan tazo, Badar bata da ruƙo, sha yanzu magani yanzu ce dan haka take ta zazzage mata abinda yaje ranta maganar ta wuce. Ta dai gaya mata wlh koda wasa ta sake maimaita mata abinda tayi zata nuna mata bawai bata da zuciya bane ko kuma ita kaɗaice me baƙin rai, zata fita a harkarta dan bazata cigaba da zama da ita Alhalin zuciyarta bata aminta da ita ba. Gurin Islam suka wuni, Badar bata iya boye abinda yake a ranta tayiwa Afeeyah murna akan Soyayyarta da Jay amma tace

"Afee karki sakashi a ranki sosai saboda gudun abinda zeje ya dawo. Muyita addu'a idan shine Alkhairinki Allah ya tabbatar amma magana ta Allah nafi sonki da Ahmad sedai idan kuma za'abi ta suna Jay ɗin nan fa ze ɗaga mana aji, ganinmu za'a ringayi muna cafkewa da world class Celebrities, Allah kenan sega Badar zata haɗu da JAY a ɓagas, kinga su MESSI duk zasu zama Abokanmu wayyo Allah na" suka ringa dariya, Afeeyah jinsu takeyi ta tabbatar gaskiya suke faɗa mata amma kuma zuciyarta ta rigada ta afka ga koginda fitowarta se anyi da gaske.

******************
"Naziru kalleni dakyau nayi kama kama da wawiya da zaka zauna kana tsarawa wannan zancen na kama? Ni ba surutun banza da iska nake so naji ba, kuɗina zaka bani maza ka zuba munsu anan" ta warware ƙaramar Ghana Must Go dataje da ita kafin taci gaba da cewa
"Maza maza kana ɓatamun lokaci daga nan janguza zanje an yanka wasu filaye zanje na siye na ajiye abuna tunda lamarin ƙannenku babu Allah yan iskan yaya sun zama ɓarayi, yaron nan Faisal da Jafaru yaƙi bashi kuɗin shine yabi dare yayi mun sata, ni banma san nawa ya ɗauka ba dan lissafi ya kwace mun tunda naga haka nace toh ba yanzu ya saba ba, daman na daɗe ina ganin kuɗin nayin ƙasa se in ɗauka ajiya ce ta saka sikayi laushi. Kuma fa kwana suke cikin sanyi yanda kace, kaji ɗakin kuwa kamar dusar Ƙanƙara zata zubo....."

"Haba Hajiya, ki tsahirta mana karki ƙware" Naziru ya dakatar da hajiyar dake ta zuba kamar nunanniyar kanya kafin yaci gaba da cewa
"Na gaya miki Hajiya yawan shige da ficen da kuɗi sukeyi a personal account ɗina yana neman ya jawo mun matsala. Kinsan dai yanda EFCC yanzu suke saka idanu kan duk wani motsin manyan kuɗi a ƙasar nan, na gaya miki ba'a account ɗin company suke ba kuma ko a nan ne ke account ɗinki idan aka tura kuɗaɗen nan wlh suna iya rufeshi azo bincike ki saka kanki a matsala. Haƙuri zakiyi kamar yanda nace zan ringa ciresu a hankali ana juyawa se a ringa tura miki da kaɗan ko Miliyan ɗaya ce duk wata".

"Ai shiyasa nazo da jaka tashi zakayi mu tafi bankin ka ciremun kuɗina na gaji da wannan ƙarairayin naka kullum bayan Alhaji Zakariyya ya gaya mun ya karɓi nasa ni kake so ka cuta kenan ka cinye mun kuɗi to baka isa ba" Hajiyar ta faɗa cikin ɗaga murya. Naziru ya dafe kai, ya rasa bayanin da zeyiwa Hajiya ta fahimceshi, saboda Allah tayaya ze tura mata Miliyan ɗari uku ko kuma ya cirosu ya zuba mata a Ghana Must Go a wannan halin da EFCC ta matsa ko da account ɗin kamfani cikin takatsan tsan suke abubuwa balle aga kuɗi irin haka suka fita daga personal account ɗinsa ai tona masa asiri zatayi.

"Hajiya shima kayan kuɗi ya karɓa ba zallarsu ba kuma kiyi haƙuri ki dena ɗaga murya mutanen gidan sunajinki" ya faɗa a tausashe. Ta zabga masa harara tace
"Ni kuɗi na nake so, waima kayan uban wane kuɗi kuke magana akai kamar wasu marasa gaskiya haka yace mun wai kaya ya karɓa su kayan basu da suna ne bayan Mai akwai abinda ka fara siyarwa ban sani bane da ake samun kuɗi saboda mugunta baka gaya mun ba balle na gwada nima?"

"Zinare ya karɓa na gaya miki na fara haƙar zinare a Zamfara ai"

"Dan ubanka da akace dutse yana ruftowa mutane so kake ka mutu saboda rashin godiyar Allah zaka zurƙuma cikin rami wai haƙar zinare Naziru?" Hajiya ta faɗa tana zare ido kamar ance mata dutsen ya rufta dashi. Ya kalleta, da ace watace daban daya tambayeta a duniya waya kaita son zuciya amma uwarsa ce duk iskancinsa baze kwatanta haka ba se yayi murmushi yace

"Bafa da kaina nake shiga ba Hajiya kamfani ne suke haƙan da injina kuma jari kawai na saka ina karɓan ɗanyan gold se na fitar a sarrafashi"

"To nima ina so a saka kuɗin, amma ni idan an haƙo gida za'a kawomun abuna in ajiye se yayi tsada sannan na fitar na siyar sarƙoƙina ma zan kwashe su idan zan tafi Umarah Turai tace sunfi daraja yanzu acan zan siyar se in baka kuɗin a ƙara jarin yanda za'a ringa samu da yawa. Wallahi fa ance kuɗi akeyi sosai da harkar nan, kaga yaro bashi da ko taro amma dayaje ya shiga rami ya dawo kaga ya zama Miloniya wannan tubda da Inji nema za'a haƙo sedai muna zaune muyita karɓar kaya toh haka za'ayi, amma bani ko Goma ce yanzu na tafi da ita dan na saka rai zan siyi filayen nan har nace a dubamun na bakin Titi zasu fi daraja idan an kwana biyu".

Naziru ya sauke ajiyar zuciya jin ya tsarata kuma ta hau kafin ta sake botsarewa ze san abinyi. Dole ya shirya suka fita Banki ya cire 10M aka saka mata a Ghanarta ko tsoro bataji ta haye Napep wai ta tafi Janguza, dayace ze kaita cewa tayi Aa, a dabararta karyaje yaga inda Filayen suke. Yakubu sau biyu yana sace mata Takardun Manyab Fikaye yaje ya siyar, dake bata mantawa da komai nata har gewaya take zuwa taga lafiyar kadarorinta ɗaya taje taga an yi gini har An saka Amarya ɗayan kuma Plaza akayi tayi masifar tayi bala'in ƙarshe tayi Allah ya isa dan Yakubun taurin kaine dashi kamar me kuma hauragiyarta ba tsorata shi take ba, sa'idar data samu yanzu matsayinsa daya ƙaru a Kamfani, sedai shegen Yaron kamar yanda take faɗa kansa kawai yake Azurtawa. Ko sun so ayi cuwa cuwar da aka saba ya kankane komai ya hana ta tabbatar idan suka matsa kuma kamar yanda yake cewa tsaf ze fasa ƙwai, rabuwa dashi tayi yanzu amma tana nan zatayi maganinsa yanzu maganar auran Hajiya ƙarama data taso ce a gabanta daia Abba Tee har iyayensa sunzo anyi tambaya shima Yakubun Aure zeyi.

AFEEYAH
Chapter 38 · 0% Book details