← Book details Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 71

Sashe 3

Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Alhaji Audu ya sauke ajiyar zuciya me ƙarfi yana kallon Ma'aikatan gidan da duk suka maida hankali kamar masuyin wani abun ya tabbatar kuma kunnuwa da hankulansu har sannan yana kansu, an gama na ɗazu ga wata an sakeyi kuma, idan ba'ayi sa'a ba kafin kwanciyar bacci se an kuma kafta wata Drama. A sanyaye ya ringa taku ya fita ya shiga Masallacin dake manne da gidan tunda Magriba ta kawo kai saura mintina kaɗan a kira. Carbi yake ja amma ya lula cikin tunanin daya aureshi, bashi da damar yayi shiru haka nan ko yayi tunanin abu me daɗi kullum se damuwa se ɓacin rai daga wannan se wannan.

Wayar sa dake gaban Aljihu ta ɗauki Ƙara ya zarota, Alƙali Yakubu ne, miƙewa yayi ya fice daga cikin masallacin ya tsaya daga gefe lokacin wayar ta katse dan haka yabi bayan kiran. A taƙaice suka gaisa, Yakubun ya tambayeshi yanda Zaman su ya ƙare da matsaya akan zancen kuɗin.

"Mun rigada mun gama magana yayi rantsuwa akan bashi ya ɗauka ba kuma na yarda amma na sauke shi daga kujerar Takwaranka ze riƙe na lokacin kafin musan abinyi" Audun ya faɗa masa. Daga ɗaya ɓangaren Yakubu yace
"Idan har ka yarda dashi menene dalilin daya saka ka dakatar dashi daga aiki kuma?"

"Haka dokar take a rubuce, duk wanda aka kama da laifin cin hanci ko yiwa Kamfani zamba hukuncinsa korace sannan ze maido da duk abinda aka rasa, bamu baƙaci ya mayar da komai ba amma an dakatar dashi saboda idan banyi haka ba kamar na buɗe Ƙofa ne ga sauran kowa ze iya wasarere da dukiyar Kamfani saboda yasan babu matakin da za'a ɗauka akansa, kuma dalilin daya saka bamu buƙaci ya maido da kuɗin ba saboda Bincike ya tabbatar da basu shiga account ba, a rubuce ne kawai akwai su kuma idan aka tattara lissafi ya kamata ace suna ciki sedai am rasa ta inda suka maƙale".

Dariya jawabin Audun ya bawa Yakubu ya dara kafin yace
"Ai shikenan, tunda har ka gano da kanka inda matsalar take ina ganin babu laifin Aminu kamata yayi ka tattara shuwagabannin kowanne ɓangate su gabatar maka da lissafinsu da kansu sannan ka haɗa dashi wamda suka bashi daga nan za'a tantance me laifi da me gaskiya, most especially guraren da kuke generating kuɗi sosai Oil da sauran Mineral su ya kamata ka tsananta bincike akai na tabbata daga nan matsalar take" Yakubun ya bashi shawara daga nan suka ɗan tattauna wasu batutuwan kafin sukayi sallama dalilin sallah da aka kira.

A cikin gida kuwa a tsakar gida Hakiya ta kafa kujera tana zazzaga bala'i, daga Momy Har Anty babu wadda ta leƙo ballantana ta tanka mata daman da Baba Bilki tana nan ne itace zata kulata to tana gidan Sarki matarsa ta haihu ita take zauna mata. Har aka kira sallar Magriba batayi shiru ba bakinta har kumfa yake yawu na sarƙeta amma taƙi haƙura ita kanta Hajiya ƙaramar datayi iyakar yinta akan Hajiyar tayi shiru taƙi ɗaki ta shige tana cigaba da kukan Asarar da Yaya Yakubu ya janyo mata, ita ai bata ce masa zata biye ta zancen Hajiya ba domin da tana hawa layin data ke ɗorata da tuni ta daɗe da zama riƙaƙƙiyar karuwa a cikin gida domin abinda Hajiyar take nuna mata kullum shine tayi komai ba komai bane muddinba bude ƙafa zatayi ba. Ta rasa irin tunani da son zuciyar Hajiya, bata duba mutunchinta ko zunubin da zasu ɗauka da ita me aikatawar da ita data turata burinta kawai ta cafko musu Dan Attajiri wanda ya kere Mijim Anna dana Khadija da kuma saurayin da yake neman Aslamiyya tunda bata samu yanda take so akan Nazira data janyowa Nakasar data so ta hanata Auruwa daga ƙarshe Audun ya haɗata da wani Yaronsa babu laifi yana da abin hannunsa daidai Misali shima kuma yana sonta.

Ita Anna Ɗan Sarkin Zazzau ta aura Khadija kuma Wani Matashin Ɗan Kasuwa me jida Yayan Banki duk su biyun suna cikin daula da jin daɗin rayuwa ita Khadija ma zamansu rabi da rabi ne a Nigeria sunfi zama a Dubai wannan Daula da Yayan Momy suke ciki ta tsolewa Hajiyar Ido, sannan ga Auren da Sarki yayi ya Auro wata halfcast Ambariyya, Mamarya ce Bahaushiya yar Nigeria Babanta kuma Balaraben Qatar ne Hamshaƙin me Arziƙi Bikin Sarkin da yanda Uban Amaryar yayi wasan kuɗi ya gigita Hajiyar, ada tana hura hanci akan Matar Zakariyya da Matar Naziru yan manyan gidaje ne tana habaicin kaf Yayan gidan babu wanda ya auro Ya daga gida kamar nasu se gashi Sarki ya goge mata hadda ya auro Balarabiya wannan yasa ta sake cin buri akan Hafsa seta auri Mijin daya doke nasu Khadija sannan Jafar shi ze wanke mata takaicin Sarki ya samo wata tsaleliyar Baturiya ko Indiya shida yake sananne a Duniya ma ai Matar da ze Aura se an ganta kawai yanzun hankalinta yafi karkata akan Hafsa tayi Aure se kuma ta mayar da hankali kan Autarta Sarah.
PAGE 2
Kiran sallar Magriba ne ya tasheta badan ta gaji da zazzagar da takeyi ba ba kuma ta gama ba zata cigaba. Ta bubbuga sallarta domin babu nutsuwa tattare da ita ko kaÉ—an tana idarwa ko salati bata iya tsayawa tayiwa Annabi ba taja waya ta shiga kiran Tirau.

"Yaushe zaki dawo? Akwai matsala" ta faÉ—a ba tareda ta tsaya sun gaisa ba.
"Jibi in Allah ya yarda, jirgi muka rasa yau shiyasa ma bamu taho ba se jibin muna Jidd ma, wlh ansha dake, da uwa kuɗinki matar nan ki biya mu tafi abi mu kikaƙi, tafiyar nan tayi daɗi yanda baki zato keni ban taɓa umarah me daɗin wannan ba yanzu ma muka dawo daga kanti munyo siyayya naga wasu riguna har zan kiraki idan kinaso a siyo miki na tuna da dai kyautace zaki karba koda yake ko kyautar ce babu lallai ki saka ma sedai ki Ajiye har su daddage su zama gari" Turai ta bata amsa cikin dariyar shaƙiyanci.

Binta taja tsaki tace
"Ai shikenan se kun dawo É—in, idan kuma naga bazan iya jira ba zanje gurin Hajiya Halima kawai muyi maganar ai tasan gidan Malamin nan naki ko?"

"Daɗina dake rashin saiti wani sa'ilin wlh Binta, ce miki nayi ina haɗen Malami da ƙawaye? To ai ko ke abinda yasa kikaga ina kai matsalarki gurin Malamina saboda nasan ba layinki bane dole tasa kike leƙawa kuma ba zakimun yankan baya ba. Ki kuskura ki kaiwa Halima matsalarki zaki gane baki da wayo wlh ke baki san da yawa neman hanyar ganin bayan mu akeyi bako? To idanbata kaiki inda za'ayi miki magani ba ta kaiki inda za'a ƙara dagula miki lissafi ai. Maganar Hafsatun ce ko yaya? Ba jiya kince mun yau yaron zezo ba? Be zo bane ko yaya? Amma abin da kamar wuya ace be zo ba dan kiranyen da Malam ya masa idan kinga be zo ba to a kabari yake dan wlh aikin da aka masa irinsa akeyiwa Riƙaƙƙun masu laifo kiji ance sun gudu daga Magarƙama to Aljanu ake turawa su ɗauko su, yauwa ya wancan zancen kuɗin komai ya tafi daidai ko? Dan ko ɗazu seda Malam ya mun tunin kasonsa nace masa ban dawo ba bamu zauna naji yanda ake ciki ba tukunna".

"Uhm kedai Turai Allah ya kaimu jibin ku dawo ma zanta, maganganun da yawa ni na rasa ma abinda zanyi wlh" Bintan ta faɗa kamar abar tausayi, Tirai ta sheƙe da dariya tace
"Ai Binta lamuranki kamar me bakin uwa, kiga abu rumi rumi an ƙullashi se yayi kamar yaci komai ya watse gaskiya ki tashi tsaye magauta sunga gadon barcinki lokacin daya kamata ki huta yazo, Yayanki sun kawo ƙarfi amma kuma kwanciyar hankali taƙi samuwa? Allah ya kaimu jibin to mu dawo zuwa gata seki shigo muji yanda ake ciki" daga nan sukayi sallama ta rafka tagumi tana tunani.

Masifar gidan da kullum gaba takeyi ba baya ba ta sakata fara abinda bata da ra'ayi akai kwata kwata wato Bin Malamai, tun Kissar tana ci a sannu ta dena tasiri saboda an kai gaɓar da wata kwarkwasa ko kisisina ta dena tasiri akan Audun, sabgar Kasuwancinsa kawai ya saka a gaba, shekarun baya lokacin da yake ta tiri tiri da ƙoƙarin ganin BECHI GROUP OF COMPANIES ya tsaya da ƙafarsa lokacinsu ma wahala yake masa, ga tafiye tafiye ko yana ƙasar ma se su kwana su wuni basu sakashi a ido ba a wannan lokacin ne kuma tayi Arziƙi domin itace akan komai, Ashana idan babu a gidan gurinta za'a nema cefane se abinda taga dama za'a kawo ta ringa tara kuɗi tana siyar Kadarori, Filaye, gidaje ta zuba yan haya da kuma sarƙoƙin gwal wanda ba sakawa take ba suna nan narke a drawer wani Design dinma wanda suka ƙirkireshi sun manta da Kalarsa.

Da su Zakariyya suka gama makaranta kuma dukda daman tun suna ciki take cusa su akan harkokin Audun kullum tana nuna masa ya kamata ace ya sakasu domin sune magadansa tun yanzu ya kamatu su san komai da yanda ake gudanar dashi ba wai se rana tsaka ne zasu kama abin ba, tun baya sakar musu har yazo dakansa ya yarda yana da buƙatar su horu akan sabgar kasuwancin nasa domin Bare ze iya ha'intarsa wata rana kamar yanda yake gani ga Abokanan kasuwancinsa da suka tashi tare da yawa sun durƙushe kuma idan aka bi kadi daga ƙarshe yakan kasance wasu daga cikin ma'aikatan gurin ne da suka fitar da sirrunsu ga abokanan Hamayya har hakan ya janyo durƙushewar gurin amma se tunanin sa be kawo masa cewar ba su kaɗaine yayansa ba ko kuma ba su kaɗai ne magadan nasa ba kamar yanda take faɗa, burinta ya cika suka samu gurin zama dukda da farko sun fara ne a ƙanana ma'aikata tafi tafi suna haɗa tuggu da manaƙisa irin wadda suka sha a Nono har suka saka aka tunɓuke asalin waɗanda suka da muƙamansu na yanzu suka maye gurbinsu.
Chapter 3 · 0% Book details