Sashe 31
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Momy ta kai zaune tana cewa
"Ai Maimuna Al'amarin Salim a kullum maimakon yayi sauƙi ƙara ta'azzara yakeyi. Ba Salim kadai ba ni yanzu Yayansu shi yafi damuna, ace mutum beyi shashanci ba da ƙuruciya se yanzu daya fara tara iyali? Kuma wannan ƙallababbiyar sabgar siyasar da ya shiga ita take neman canza masa alƙibla, daman ni sam abin be kwanta mun ba. Tunda ya fara yake sakani magana, kullum matarsa na hanyar kawo ƙararsa.
Yanzu shekaran Jiya seda sukazo sulhu da saboda tsabar wulaƙanci Yaron nan wai wancan satin ya kawo mata wasu ɗirka ɗirkan yayan Ƙabilu gida wai Yawon Campaign suka zo basu da masauki duk Hotel da suke Kano bega inda ze kama musu ba se gidansa yace ahine ta zo nan take gaya mun na kirashi nayi masa tatas ya sallamesu be daddaraba shekaran jiyan sega wata ya sake kaiwa wai sati ma zatayi a gidan shi zasu tafi Abuja dan haka zata zauna a gidan har ya dawo data kira waya ta gaya mun na sanarwa ubansa bece komai ba, se Alƙali na kira na gaya masa shi kuma ya kirashi sukaje can aka kashe maganar to Allah yasa dai yaji, Haba Yanda kika san su kaɗai ne Yaya a gidan nan kullum cikin sakani magana da ɗakko mun zance suke Salim da Babana na rasa yanda zanyi dasu".
"Hmmm, Anty Aisha kenan, ai bazangaji da gaya miki ba kin tafka kuskure a baya kuma sakamakon sa kike girba a yanzu. Sufa Yaya kiwo ne Allah ya bamu, ba kuma iyakar wanda ka haifa daga cikinka sune naka ba, Malamai fa suna cewa ranar Lahira hatta akan gidan auranmu da zamantakewar mu se anyi mana Hisabi kinga kenan dole mu yi iyakar iyawarmu gurin ganin mun sauke duk wasu nauyi daya rataya akanmu shine kuma ya haɗa da kula da tarbiyyar yayanmu da duk wand suke zagaye damu. Kinga waɗannan yaran da kika ringa zuba ido ana cutarwa? Rayuwarsu ta ringa gantafalfala alhalin kinada halin taimaka musu ki kwatar musu yancinsu ta yanda koda basu samu dukkan gata ba zasu samu rangwamen halin da suke ciki amma kika naɗe hannu da sunan ba ruwanki baki shiga abinda ba'a sanyaki ba wlh ko kaffara bazanyi ba harda haƙƙinsu cikin abinda ya saka kika gaza ganin daidai a cikin taki zuri'ar.
Kuma irin tarbiyyar da kika bari aka ginasu akanta ita naki yayan da suka tashi suka ɗauka, abinda da yawa muke kasa ganewa kenan a duk sanda kaga Ɗan wani musamman na kishiya yana abinda be kamata ba kar kace babu ruwanka ko bazaka tsawatar masa ba domin ze cuɗanya da naki Yayan, duk bakin tarbiyyar da kika haƙiƙance kina yi musu kuwa kina can ba zaki san lokacin da zasu ɗauki halaye marasa kyau ɗin da kika bari suka ci gaba ba.
Kinzo gidan nan kin tarar da yara da yawa, da ace ke me dabara ce a sannan jan su zakiyi a jiki kiyi musu irin tarbiyyar da Kike fatan yayanki su tashi akanta, haka mata masu wayo sukeyi suja yayan kishiya a jiki su kula dasu da tarbiyyarsu karki taɓa duba halin uwarsu ko abinda zata miki domin taki gaban kike gyarawa, yanzu wa gari ya waya? Banda Ahmad da Matan da kika samu Allah ya duba miki ya sassauta abin akansu dukda suma ɗin da nasu, gaba ɗaya yayan gidan nan babu wata shaƙuwa ko soyayya a tsakaninsu, kowa kansa ya sani wlh ina jiye muku ranar da mutuwa zata fara ɗauki ɗai ɗai tsakanin Iyaye ko yayayen, kar a wayi gari a ce cikin Rayayyun yan uwa a rasa masu duba bayan abinda Ɗan uwansu ya bari.
Wlh ki farka ki dage da Addu'a ki kuma sa a miki Allah ya haÉ—a miki kan zuri'arki dan wlh cikin waÉ—annan Yayan naki Ahmad kaÉ—ai nake da tabbacin yau idan wani cikin sauran ya faÉ—i ya mutu baze bar zuri'arsa tayi kukan maraici ba, amma kinga wannan Uban namu da Salim? Allah ya rufa asiri kawai kawunansu kawai suka sani sedai Allah ya duba ya shiga cikin Lamarin".
Jikin Momy yayi laƙwas kamar an zubawa Salak gishiri, maganganin Maimuna sun shigeta kuma ta sani gaskiya ta faɗa a yanzu ne take nadamar rayuwar baya data zama kamar hoto bata taɓuka komai gurin gyaranmakauniyar tafiyar da akeyi a cikin gidan ba, a lissafinta idan taja nata yayan sun isa suyi rayuwarsu sedai kuma ta tafka kuskure gashi kuma yanzu tana girbar abinta saboda wannan hanyar da Yayayen nata suka ɗauka ta kowa kansa ya sani ta samo Asali daga abinda suka tashi suka gani anayi a gidan nasu ne.
Maimuna na kurbar shayi tace
"Gara dai ki yi ta kanki kina kallo ita Harbutsatstsiyar gidan naku duk da rashin kan gadonta batayi saken da kan yayanta ya rabu ba kuma komai da ita suke shawara bakinsu ɗaya ke kuwa fa? Banda Ahmad wa yake zuwa ya durƙusa gabanki ya faɗa miki halin da yake ciki ko ga wani abu da zeyi?"
"Allah ya rufa asiri dai Maimuna, gama cin abincin mu fita rana ta farayi kuma yai Juma'a ki samu ki gama da wuri" da haka suka bar zancen.
Ahmad kuwa bayan fitarsa Kusan karo sukaci da Hajiya dake fitowa daga É—akinta da tabarma a hannunta da alama shimfiÉ—a zatayi ta zaunasana'ar tata ta sakawa masu shiga da fice idanu.
"Aa, Amadu har ka fito kenan" ta faÉ—a fuska a washe ba kamar É—azu dayace .ata Zasuyi tafiya tareda Alhaji ba.
Cikeda gajiya da tambayoyinta yace
"Na fito Hajiya, na gaya miki Alhaji yana jirana tafiya zamuyi"
"Ayyo to, da ai da Yakubu zasuje,sedaga baya Yakubun yace yana da aiki nace ma suje da Faisal shi kuma wai tes zeyi a makaranta ashe kai ya kira banda Alhaji seya tattagoka tun daga Abuja base ya ɗauki Direba yayi tafiyarsa ba? Shikenan dai, ya akayi yau naga ka shigo mana gida hannu na dukan cinya babu yar tsarabar daka saba riƙowa ne?"
Ahmad yai zuguÉ—i yana kallonta se kuma ya zabura daya tuna abi da yake gabansa ya tafi yana cewa
"Idan mun dawo zan kawo muku" ya wuce da mamakin Hajiyar, tsarabar da kullum ya kawo haka zata amshe tana aibata shi tana masa shaguben Allah sa da kuÉ—in Halal ya siyo shine yau tambayar bata gani ba?.
Hajiya ta bishi da kallon tsana ƙarara tana jan ƙwafa, ta tsani Yaron ya kuma zamar mata ciwon ido dan ta rasa ya zatayi dashi. Yanzu da Alaƙa take ƙara Ƙarfi tsakaninsa da Alhajin ya sake dagula mata lissafi ba kuna zata lamunta ba duk yanda zatayi setabi gurin datseta tun kafin tayi ƙarfi. Ko yanzu da gayya take ta jansa da magana saboda ya ɓata lokaci har Alhajin ya fito yayi masa tijara burinta kenan ba wani abu ba.
A gurguje ya shirya, wata dakakkiyar shadda kalar sararin samaniya ya saka ta haska Fatarsa dake da duhu bacan ba ɗinkin babbar riga ne, be sakata ba ya riƙe a hannu da hular da ze saka da Agogo, Takalmi da Azurfa, cikin sauri ya fesa turare ya fita da silifas a Ƙafarsa. Alhaji na tsaye bakin motar da zasu tafi a ciki an kawo masa ita daidai Barabder yana waya da alama Ahmad alamu sun nuna Ahmad kawai yake jira kenan.
Cikin tsantsar ladabi jikinsa har rawa yake ya durƙusa yana gaida Alhajin, wata Kafirar Shaddace data sha aiki na Alfarma a jikin Alhajin, yanayin ƙirarsa ga shigar da yayi ta ƙasaita yasa kwarjininsa nunkuwa tamkar wani Basarake. Ba yabi ba fallasa ya amsawa Ahmad gaisuwar kafin yace masa
"Ya haka zaka fito kamar wanda aka koro?"
"Babu komai Alhaji, daman so nake sena shiga mota sena ida shiryawa".
Harara Alhajin ya maka masa, yasan abinda yake nufi dan haka sum sum ya shige falon ya shiga ƙarasa shirinsa. Tsaf ya fito bayan ya kafa hula Babbar rigar ce dai be saka ba saboda karta yamutse kuma takura masa ma zatayi, data son ransa ne ma Normal Kaftan ze saka na yadi ba shadda ba sedai sanin halin Alhajin tsaf idan yayi shigar da bata gamsheshi ba dizgashi zeyi gaban jama'a babu ruwansa. Shi Mamaki yayi ma da Alhajin ya nemi ya rakashi wata unguwa me muhimmanci irin wannan domin be taɓa ba, Yanzu da sabgogi sukawa Su Zakariyya yawa Yakubu ne abokin rakiyarsa ko Faisal, wani Sa'ilin har Lawan ɗauka yakeyi ya rakashi be san dalilin daya saka Alhajin nemansa ba.
A kunne motar take dan haka yayi bismillah ya shiga, Alhaji ya gama sallamar Balarabe me ban ruwan Fulawa kafin ya buɗr gidan gaba kusada Ahmad ya zauna yana hailala, wannan kuma haline klda su Naziru ze fita a gaba yake zama. A ɗarare Ahmad daya gama karanto Addu'ar hawa abin hawa ya taka motar suka tafi, a tare suka ringa ɗagawa masu aiki dake musu Allah ya tsare hannu, Alhajin me halin tsiya dana kirki kenan, a ɓangaren mu'amala da mutanen waje bashida matsala. Duk qanqantar mutum in har musulmi ne yazo giftashi zeyi masa sallama har ya bashi hannu suyi musabiha barshi dai da halinsa idan ya motsa wannan kam kowa ma yi masa yakeyi.
Tafiya sukeyi babu me cewa komai in banda karatun Alƙur'ani da Ahmad ya kunna can ƙasa yana bi a hankali. Jefi jefi Alhajin yake amsa waya, wata ta kasuwanci wata kuma Abokanansa ne masu tambayar ko ze samu halartar ɗaurin auran bikin ɗan Abokinsa ne da sukayi makarantar sakandire tare. Sun miƙe hanya sosai kamar daga sama Ahmad yaji Alhajin yace
PAGE 12
"Rayuwa kenan, duk waɗannan da kaji muna magana dasu a sanda mukayi makaranta ƙyamatarmu sukeyi saboda su lokacin a gaban Iyayensu suke mu kuwa Almajiranci aka kawo mu Kano, naci da dagiya tasa muka Shiga Bokon amma yanzu dubi ka gani kowanne cikinsu so yakeyi yayi alaƙa damu, bakaga roƙon da Alhaji Mustapha ya ringayiwa Babanku Alƙali akan ya ɗaga tafiyarsa Umarah yaje masa ɗaurin aurannan ba, Allah kenan wato shiyasa duk yanda mutum yake karka rainashi dan baka san me ze zama a gaba ba, a lokacin suna ganin su yan gatane se gashi a yanzu da Yan Bokon cikin su da Yan Kasuwar babu wanda ya zarce nida Ɗan uwana" Alhajin ya faɗa cikin Alfaharin abun.
"Ai Maimuna Al'amarin Salim a kullum maimakon yayi sauƙi ƙara ta'azzara yakeyi. Ba Salim kadai ba ni yanzu Yayansu shi yafi damuna, ace mutum beyi shashanci ba da ƙuruciya se yanzu daya fara tara iyali? Kuma wannan ƙallababbiyar sabgar siyasar da ya shiga ita take neman canza masa alƙibla, daman ni sam abin be kwanta mun ba. Tunda ya fara yake sakani magana, kullum matarsa na hanyar kawo ƙararsa.
Yanzu shekaran Jiya seda sukazo sulhu da saboda tsabar wulaƙanci Yaron nan wai wancan satin ya kawo mata wasu ɗirka ɗirkan yayan Ƙabilu gida wai Yawon Campaign suka zo basu da masauki duk Hotel da suke Kano bega inda ze kama musu ba se gidansa yace ahine ta zo nan take gaya mun na kirashi nayi masa tatas ya sallamesu be daddaraba shekaran jiyan sega wata ya sake kaiwa wai sati ma zatayi a gidan shi zasu tafi Abuja dan haka zata zauna a gidan har ya dawo data kira waya ta gaya mun na sanarwa ubansa bece komai ba, se Alƙali na kira na gaya masa shi kuma ya kirashi sukaje can aka kashe maganar to Allah yasa dai yaji, Haba Yanda kika san su kaɗai ne Yaya a gidan nan kullum cikin sakani magana da ɗakko mun zance suke Salim da Babana na rasa yanda zanyi dasu".
"Hmmm, Anty Aisha kenan, ai bazangaji da gaya miki ba kin tafka kuskure a baya kuma sakamakon sa kike girba a yanzu. Sufa Yaya kiwo ne Allah ya bamu, ba kuma iyakar wanda ka haifa daga cikinka sune naka ba, Malamai fa suna cewa ranar Lahira hatta akan gidan auranmu da zamantakewar mu se anyi mana Hisabi kinga kenan dole mu yi iyakar iyawarmu gurin ganin mun sauke duk wasu nauyi daya rataya akanmu shine kuma ya haɗa da kula da tarbiyyar yayanmu da duk wand suke zagaye damu. Kinga waɗannan yaran da kika ringa zuba ido ana cutarwa? Rayuwarsu ta ringa gantafalfala alhalin kinada halin taimaka musu ki kwatar musu yancinsu ta yanda koda basu samu dukkan gata ba zasu samu rangwamen halin da suke ciki amma kika naɗe hannu da sunan ba ruwanki baki shiga abinda ba'a sanyaki ba wlh ko kaffara bazanyi ba harda haƙƙinsu cikin abinda ya saka kika gaza ganin daidai a cikin taki zuri'ar.
Kuma irin tarbiyyar da kika bari aka ginasu akanta ita naki yayan da suka tashi suka ɗauka, abinda da yawa muke kasa ganewa kenan a duk sanda kaga Ɗan wani musamman na kishiya yana abinda be kamata ba kar kace babu ruwanka ko bazaka tsawatar masa ba domin ze cuɗanya da naki Yayan, duk bakin tarbiyyar da kika haƙiƙance kina yi musu kuwa kina can ba zaki san lokacin da zasu ɗauki halaye marasa kyau ɗin da kika bari suka ci gaba ba.
Kinzo gidan nan kin tarar da yara da yawa, da ace ke me dabara ce a sannan jan su zakiyi a jiki kiyi musu irin tarbiyyar da Kike fatan yayanki su tashi akanta, haka mata masu wayo sukeyi suja yayan kishiya a jiki su kula dasu da tarbiyyarsu karki taɓa duba halin uwarsu ko abinda zata miki domin taki gaban kike gyarawa, yanzu wa gari ya waya? Banda Ahmad da Matan da kika samu Allah ya duba miki ya sassauta abin akansu dukda suma ɗin da nasu, gaba ɗaya yayan gidan nan babu wata shaƙuwa ko soyayya a tsakaninsu, kowa kansa ya sani wlh ina jiye muku ranar da mutuwa zata fara ɗauki ɗai ɗai tsakanin Iyaye ko yayayen, kar a wayi gari a ce cikin Rayayyun yan uwa a rasa masu duba bayan abinda Ɗan uwansu ya bari.
Wlh ki farka ki dage da Addu'a ki kuma sa a miki Allah ya haÉ—a miki kan zuri'arki dan wlh cikin waÉ—annan Yayan naki Ahmad kaÉ—ai nake da tabbacin yau idan wani cikin sauran ya faÉ—i ya mutu baze bar zuri'arsa tayi kukan maraici ba, amma kinga wannan Uban namu da Salim? Allah ya rufa asiri kawai kawunansu kawai suka sani sedai Allah ya duba ya shiga cikin Lamarin".
Jikin Momy yayi laƙwas kamar an zubawa Salak gishiri, maganganin Maimuna sun shigeta kuma ta sani gaskiya ta faɗa a yanzu ne take nadamar rayuwar baya data zama kamar hoto bata taɓuka komai gurin gyaranmakauniyar tafiyar da akeyi a cikin gidan ba, a lissafinta idan taja nata yayan sun isa suyi rayuwarsu sedai kuma ta tafka kuskure gashi kuma yanzu tana girbar abinta saboda wannan hanyar da Yayayen nata suka ɗauka ta kowa kansa ya sani ta samo Asali daga abinda suka tashi suka gani anayi a gidan nasu ne.
Maimuna na kurbar shayi tace
"Gara dai ki yi ta kanki kina kallo ita Harbutsatstsiyar gidan naku duk da rashin kan gadonta batayi saken da kan yayanta ya rabu ba kuma komai da ita suke shawara bakinsu ɗaya ke kuwa fa? Banda Ahmad wa yake zuwa ya durƙusa gabanki ya faɗa miki halin da yake ciki ko ga wani abu da zeyi?"
"Allah ya rufa asiri dai Maimuna, gama cin abincin mu fita rana ta farayi kuma yai Juma'a ki samu ki gama da wuri" da haka suka bar zancen.
Ahmad kuwa bayan fitarsa Kusan karo sukaci da Hajiya dake fitowa daga É—akinta da tabarma a hannunta da alama shimfiÉ—a zatayi ta zaunasana'ar tata ta sakawa masu shiga da fice idanu.
"Aa, Amadu har ka fito kenan" ta faÉ—a fuska a washe ba kamar É—azu dayace .ata Zasuyi tafiya tareda Alhaji ba.
Cikeda gajiya da tambayoyinta yace
"Na fito Hajiya, na gaya miki Alhaji yana jirana tafiya zamuyi"
"Ayyo to, da ai da Yakubu zasuje,sedaga baya Yakubun yace yana da aiki nace ma suje da Faisal shi kuma wai tes zeyi a makaranta ashe kai ya kira banda Alhaji seya tattagoka tun daga Abuja base ya ɗauki Direba yayi tafiyarsa ba? Shikenan dai, ya akayi yau naga ka shigo mana gida hannu na dukan cinya babu yar tsarabar daka saba riƙowa ne?"
Ahmad yai zuguÉ—i yana kallonta se kuma ya zabura daya tuna abi da yake gabansa ya tafi yana cewa
"Idan mun dawo zan kawo muku" ya wuce da mamakin Hajiyar, tsarabar da kullum ya kawo haka zata amshe tana aibata shi tana masa shaguben Allah sa da kuÉ—in Halal ya siyo shine yau tambayar bata gani ba?.
Hajiya ta bishi da kallon tsana ƙarara tana jan ƙwafa, ta tsani Yaron ya kuma zamar mata ciwon ido dan ta rasa ya zatayi dashi. Yanzu da Alaƙa take ƙara Ƙarfi tsakaninsa da Alhajin ya sake dagula mata lissafi ba kuna zata lamunta ba duk yanda zatayi setabi gurin datseta tun kafin tayi ƙarfi. Ko yanzu da gayya take ta jansa da magana saboda ya ɓata lokaci har Alhajin ya fito yayi masa tijara burinta kenan ba wani abu ba.
A gurguje ya shirya, wata dakakkiyar shadda kalar sararin samaniya ya saka ta haska Fatarsa dake da duhu bacan ba ɗinkin babbar riga ne, be sakata ba ya riƙe a hannu da hular da ze saka da Agogo, Takalmi da Azurfa, cikin sauri ya fesa turare ya fita da silifas a Ƙafarsa. Alhaji na tsaye bakin motar da zasu tafi a ciki an kawo masa ita daidai Barabder yana waya da alama Ahmad alamu sun nuna Ahmad kawai yake jira kenan.
Cikin tsantsar ladabi jikinsa har rawa yake ya durƙusa yana gaida Alhajin, wata Kafirar Shaddace data sha aiki na Alfarma a jikin Alhajin, yanayin ƙirarsa ga shigar da yayi ta ƙasaita yasa kwarjininsa nunkuwa tamkar wani Basarake. Ba yabi ba fallasa ya amsawa Ahmad gaisuwar kafin yace masa
"Ya haka zaka fito kamar wanda aka koro?"
"Babu komai Alhaji, daman so nake sena shiga mota sena ida shiryawa".
Harara Alhajin ya maka masa, yasan abinda yake nufi dan haka sum sum ya shige falon ya shiga ƙarasa shirinsa. Tsaf ya fito bayan ya kafa hula Babbar rigar ce dai be saka ba saboda karta yamutse kuma takura masa ma zatayi, data son ransa ne ma Normal Kaftan ze saka na yadi ba shadda ba sedai sanin halin Alhajin tsaf idan yayi shigar da bata gamsheshi ba dizgashi zeyi gaban jama'a babu ruwansa. Shi Mamaki yayi ma da Alhajin ya nemi ya rakashi wata unguwa me muhimmanci irin wannan domin be taɓa ba, Yanzu da sabgogi sukawa Su Zakariyya yawa Yakubu ne abokin rakiyarsa ko Faisal, wani Sa'ilin har Lawan ɗauka yakeyi ya rakashi be san dalilin daya saka Alhajin nemansa ba.
A kunne motar take dan haka yayi bismillah ya shiga, Alhaji ya gama sallamar Balarabe me ban ruwan Fulawa kafin ya buɗr gidan gaba kusada Ahmad ya zauna yana hailala, wannan kuma haline klda su Naziru ze fita a gaba yake zama. A ɗarare Ahmad daya gama karanto Addu'ar hawa abin hawa ya taka motar suka tafi, a tare suka ringa ɗagawa masu aiki dake musu Allah ya tsare hannu, Alhajin me halin tsiya dana kirki kenan, a ɓangaren mu'amala da mutanen waje bashida matsala. Duk qanqantar mutum in har musulmi ne yazo giftashi zeyi masa sallama har ya bashi hannu suyi musabiha barshi dai da halinsa idan ya motsa wannan kam kowa ma yi masa yakeyi.
Tafiya sukeyi babu me cewa komai in banda karatun Alƙur'ani da Ahmad ya kunna can ƙasa yana bi a hankali. Jefi jefi Alhajin yake amsa waya, wata ta kasuwanci wata kuma Abokanansa ne masu tambayar ko ze samu halartar ɗaurin auran bikin ɗan Abokinsa ne da sukayi makarantar sakandire tare. Sun miƙe hanya sosai kamar daga sama Ahmad yaji Alhajin yace
PAGE 12
"Rayuwa kenan, duk waɗannan da kaji muna magana dasu a sanda mukayi makaranta ƙyamatarmu sukeyi saboda su lokacin a gaban Iyayensu suke mu kuwa Almajiranci aka kawo mu Kano, naci da dagiya tasa muka Shiga Bokon amma yanzu dubi ka gani kowanne cikinsu so yakeyi yayi alaƙa damu, bakaga roƙon da Alhaji Mustapha ya ringayiwa Babanku Alƙali akan ya ɗaga tafiyarsa Umarah yaje masa ɗaurin aurannan ba, Allah kenan wato shiyasa duk yanda mutum yake karka rainashi dan baka san me ze zama a gaba ba, a lokacin suna ganin su yan gatane se gashi a yanzu da Yan Bokon cikin su da Yan Kasuwar babu wanda ya zarce nida Ɗan uwana" Alhajin ya faɗa cikin Alfaharin abun.