Sashe 50
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tun daren da aka kwantar dashi Likitansa me kula da lafiyarsa yaje akan ze maidashi can Asibitinsa kafin ya shirya masa su fita can UK inda ya saba zuwa a duba lafiyar tasa amma yace Aa ze zauna a Asibitin Ɗansa, Asibitin da tun da aka assashi sau ɗaya ya taɓa taka ƙafarsa ranar da aka buɗe se wannan karon da jinyar bagatatan ta kawoshi ya kuma ga gata, shi da kansa ya yarda da Ƙwarewar Dr Hassan tareda ingancin Ma'aikata da kayan aikinsa. Idan Dr Hassan ɗin na Assessing ɗinsa ya ringa binsa da kallo kenan duk inda yayi, a zuciyarsa yanajin wani irin nauyi tareda kunyarsa, wai fa Ɗan Zubaida ne, Ɗan daya kusa shegantawa wanda a silar samuwarsu ya rabu da mahaifiyarsu yau gashi shine yake tsaye akan ganin lafiyarsa ta daidaita.
Har wayau shida Ahmad ne tare dashi, su suke kula dashi da jikinsu da dukiyarsu domin dai sile biyar ba'ace ya kawo ba, bayaga Yayansa mata Mazan babu ƙeyar wanda ya gani a Asibitin har ya kwana huɗu aka sallameshi ya koma gida. Tunda Hajiya ta bar Asibitin dama bata koma ba, tana gida tana saƙa da warwarar yanda zatayi, ta dai turawa Turai kuɗaɗe masu nauyi wanda tace zataje mata gurin Malamin da ze mata maganin Yakubu take yanke, baze wulaƙan tata a bainar nasi yaci banza ba, dole su tashi tsaye akansa domin akwai gagaruwar matsala idan akace Alhaji Audu ya riga Yakubu mutuwa, tabbas yanda baya ƙaunarta se yayi duk yanda ya iya ya cuceta ita kuma ba zata lamunchi wannan abu ba.
Ta manta ma da wani Alhaji na Asibiti seda taji ance ya dawo. Ta zurma Hijabi a baibai ta fita tana casgaɗa ƙafa yanda kasan wata sabuwar cogal a haka ta isa Falon Alhaji na ƙasa. Yana zaune tareda baƙi, gama sallamar ma'aikatan gidan kenan da suka bishi suna sake masa sannu da zuwa dan duk sunje Asibiti sun dubashi suna fita wasu mutanensa suka zo dubashi sunje can Asibiti aka ce an sallameshi shine suka bishi gida. Manyan mutane ne sosai, suna tsaka da tattaunawa se ganin Hajiya sukayi kamar an jehota tana cangala ƙafa tareda numfarfashi yanda kasan wadda ta tashi daga wani ciwo.
"Alhaji ashe ka dawo? Da rabon fuskokinmu zasu gamu ka ganni nima tun ranar nake a kwance, sabili kawai da nace zan shiga na dubaka a Asibiti Alƙali ya koreni na dawo gida duk ba'a hayyacina ba na zame na faɗi a bakin ƙofa tun ranar se yanzu na iya yunƙurawa na fito da naji ance kun dawo nace gara na zo mu haɗu karna mutu a ɗaki har se nayi wari sannan aji a dubani tunda kowa ya tsaneni Matanka babu wadda tako leƙa taga ya nake ace dai kwanaki huɗu ba'a ga giftawata ba ai yaci a tuhumi lafiya dai amma babu wadda tayi" Hajiya Binta ta ringa rattaba zancen da seda ta kai ayarsa kafin ta lura da cewa ba Alhajin ne kaɗai a gurin ba, tayi sak kafin ta shiga rirriƙe hijabi duk ta diririce da gani base an faɗa ba kunya ce tayi mata rubdugu.
Alhaji ya nunata da hannu yana kallon wanda yafi sauran kalar jiƙuwa da kuɗi yace
"Gata nan, ita ce Surukar Ɗan naka". Wanda aka nunawa Hajita ya kalleta babu yabo babu fallasa kakar yanda sauran baƙin suke kallonta kowanne da yanayin da yake kan fuskarta yace
"Sannu Hajiya, ya me jiki? Ya kuma naki jikin?"
Babban abun ma shine bata san uban waye cikin surukan nata ba amma dai iyakar zubar da kai yau tayi ta tafka abin kunyar da ita da kanta yau ta gagara naɗe tabarmar kunya da haukan data saba ae jan Hijabi takeyi ita ba abin ta cire ta maidashi daidai ba duk ta rasa abinda zatayi. Momy tayi sallama cikin kyakykyawar shiga ta Abaya ta yafa yalwataccen Mayafi akai bayanta Maimuna ce da me aikinta Amirah kowacce da dogon Hijabi sun ɗauko manyan Trays. Har ta kalli Binta ta wuce ta samu gurin zama kan kujerun da suke daga gefe kaɗan, su Maimuna suka ajiue kayan hannunsu suka gaida baƙin kafin suka fita sa'annan suka shiga gaisawa da Momy cikin dattako da mutuntaka.
"Itace Matata ta biyu Mahaifiyar Ahmad" Alhaji ya gabatar da ita. Baban Sirikin Binta yayi murmushi yace
"Ga kama nan kuwa har jikin ma irin nata yayi baza'ace ita ta haifesu ba" Alhaji Audu ya É—anyi murmushi sega Hajiya Rabi nan itama ta shigo a kamalance da sallamarta ta zauna suka gaisa.
"Ga kuma Amaryata" Alhaji ya gabatar da ita". Hajiya Binta ta muzanta iya muzanta, wannan abu da Audu ya mata ya kaita wuya amma kamar wadda aka zubawa glue aka liƙe a gurin da take ta kasa gaba ta kasa baya haka ta gagara magana.
Momy da Hajiya Rabi suka miƙe a tare suka musu sallama suka fice, tun a hanya da suna dawowa daga Asibiti ya sanar da Hajiya Rabi, Alhaji Tamim Uban Mijin Hajiya Ƙarama yace yana tafe ze shigo dubashi dan yana Kano, ya sanar masa sun wuce gida basa Asibiti ya sameshi a can, shi yace ta gayawa Momy wadda take fushi dashi kan abinda ya faru. Sau ɗaya taje dubashi Asibiti amma kullum zatayi girki safe rana dare akai masa ita kuma Hajiya Rabi can zata wuni da dare ta dawo Ahmad ya Kwana dashi.
Abinda yasa yace a gaya mata zuwan baƙin yasab ba zata rasa abinda zata fitar dashi kunyarsu ba dan bata rabo da abubuwan motsa baki tunda yamma ce ba lokacin cin abinci bane ba gashi kuwa data tashi zuwa tazo musu da abubuwan taɓawar da ruwa da Lemo. Shi ya manta ma da Hajjajun seda ta shigo, yanda yaji kunya kuwa dai ba'a cewa komai amma ya godewa Allah da ba ita kaɗai yake aure ba, sedai a tafi da ita kaɗai a baki domin sauran matansa sun fitar dashi kunya.
Kamar sun manta da tsayuwar Hajiyar a gurin Alhajin ya musu Bismillah suka ɗan taɓa abinda aka kawo musu. Alhaji Tamim da Abokanan tafiyar tasa wayayyun mutanene suka shiga hirar kasuwanci inda ko wannensu yafi kauri. Hajiya ta gama tsayuwarta kafin ta miƙe ƙafafun da da yake cangalawa ta fice kamar kazar da Ƙwai ua fashewa a ciki. Tana fita ta haɗu da Faisal ta tsareshi da tambayar suwaye a Falon Alhaji.
"Baban Abba T ne" ya bata amsa, seta ɗora hannu biyu aka kafin kuma ta sauke da sauri har tana neman harɗewa ta wuce cikin gidan da saurin bala'i. Jikinta har rawa yake ta kira Hajiya Ƙarama, bata bari sun gaisa ba ta shiga surfa mata bala'i harda Allah ya isa akan.
"Kin huta yanzu ai se su dawo suyita bada labarin sunzo sun tarar da uwarki kamar mahaukaciya" ta faɗa tana rushewa da kuka kafin tayi cilli da wayar. Audu ya cuceta da be gaya mata su waye zasu zo ba yanzu yaja taje ta zubarda mutunchinta, surukin Hajiya ƙaramar ne kawai ya gaisheta amma tana gani da Aisha da Rabi suka ahiga duka harda sauran Abokanansa suka gaisa a mutunce ba irin tata gaisuqar daya mata ta jeka nayi ka ba. Ta sake zuge tazugen rashin mutunchi ta ayyana yanda zataci kan uban kowa a gidan tunda taga alamar raini ya fara shiga tsakaninta dasu kuma ba zata lamunta ba amma yanzu bari ta fara gamawa da zancen Yakubu tukunna shine Ƙayar da ya tsaya mata a wuya. Ta Alhaji Audu me sauƙi ce saboda tana da maganinsa a hannu, wurudin da Turai ta bata zata cigaba dayi tana banka masa yana sha ya dawo hayyacinsa dan taga alamar yana neman yafi ƙarfinta.
FATIMA
Ko a jikinta lissafin kwanakin zuwan Jay kawai takeyi wanda ita dashi sukeji kamar su janyo kwanakin su rage musu tsaho. Wani irin so da shaƙuwane a tsakaninsu, yanda suka damu da junansu suke tarairayar juna seya baka mamaki ba zaka ce soyayyar gani ɗaya bace kuma a waya akeyinta. Hatsaniyar da kayi a gidansu Jafar ɗin ce ta kawo tsaiko a zuwan nasa ya ƙara kwanakin zuwansa Nigeria da sati ɗaya akan yanda ya tsara dan abin ya faru yaɓa shi ya kuma ɓata masa rai matuƙa, idan yace zezo a lokacin da abun be idasa lafawa ba rigima zata dawo sabuwa ne domin dukda cewar baya son Fatima baya son auranta da Ahmad amma hakan bashi yake nufin ze zuba ido a Tozarta Ahmad ba, shi laifin Fatiman nema ya sake ninkuwa a zuciyarsa domin ta dalilinta ne aka yiwa Ahmad ɗin haka kuma ta zama silar da take neman sake janyo rarrabuwar kawuna a tsakaninsu saboda abinda ya faru dole ze sake tsanata gaba tsakanin Yayan Hajiyarsu da Su Hassan sannan a silar auranta Alhajinsu ya kwanta a Asibiti.
A ƙa'ida saura kwana uku yazo ranar yace mata an samu matsala se wani satin ze zo. Be gaya mata dalili ba, yanayin muryarsa da taji ta sakata tsurewa kodai wani abu tayi masa saya saka ya ɗaga zuwan? Cikin rawar murya kamar me son fashe masa da kuka ta tambayeshi dalili. Ya sassauto daga tunzurin da zuciyarsa take kai yace mata
"Babu komai, gidanmu ne babu lafiya an samu yar hatsaniya shiyasa kawai na ɗaga zuwan nawa saboda ze iya maido da ƙurar data lafa".
Bata fahimce shi ba amma tunda dai ba ita ta masa laifi ba ai da sauƙi. Ta ringa masa shagwaɓa da sangarta harda kukanta akan ya fasa zuwa jibi bayan ta fara shirin tarbarsa, wannan ya sanyaya masa zuciya ya shiga rarrashinta da mata Alƙawarurruka idan yazo kafin sukayi sallama ya ajiye waya.
'Ga mata nan irin su Afeeyah birjik a duniya akan Me Yah Ahmad ze nacewa waccen yari yar da babu komai tattare da ita se baƙin talauchi da sharri, daga maganar auranta ji abinda ya faru to inaga kuma ya aurota ya ajiyeta a gidansa ai se abinda Allah yayi kawai. Abin haushi da takaici kuma wai duk badaƙalar nan da akayi yanda Ahmad yace ko gezau beji soyayyarta tayi rawa a zuciyarsa ba tana nan daram dam shi dai yayi Allah wadai da So Ɗaya tak irin na Yah Ahmad' Tunanin Jay.
Har wayau shida Ahmad ne tare dashi, su suke kula dashi da jikinsu da dukiyarsu domin dai sile biyar ba'ace ya kawo ba, bayaga Yayansa mata Mazan babu ƙeyar wanda ya gani a Asibitin har ya kwana huɗu aka sallameshi ya koma gida. Tunda Hajiya ta bar Asibitin dama bata koma ba, tana gida tana saƙa da warwarar yanda zatayi, ta dai turawa Turai kuɗaɗe masu nauyi wanda tace zataje mata gurin Malamin da ze mata maganin Yakubu take yanke, baze wulaƙan tata a bainar nasi yaci banza ba, dole su tashi tsaye akansa domin akwai gagaruwar matsala idan akace Alhaji Audu ya riga Yakubu mutuwa, tabbas yanda baya ƙaunarta se yayi duk yanda ya iya ya cuceta ita kuma ba zata lamunchi wannan abu ba.
Ta manta ma da wani Alhaji na Asibiti seda taji ance ya dawo. Ta zurma Hijabi a baibai ta fita tana casgaɗa ƙafa yanda kasan wata sabuwar cogal a haka ta isa Falon Alhaji na ƙasa. Yana zaune tareda baƙi, gama sallamar ma'aikatan gidan kenan da suka bishi suna sake masa sannu da zuwa dan duk sunje Asibiti sun dubashi suna fita wasu mutanensa suka zo dubashi sunje can Asibiti aka ce an sallameshi shine suka bishi gida. Manyan mutane ne sosai, suna tsaka da tattaunawa se ganin Hajiya sukayi kamar an jehota tana cangala ƙafa tareda numfarfashi yanda kasan wadda ta tashi daga wani ciwo.
"Alhaji ashe ka dawo? Da rabon fuskokinmu zasu gamu ka ganni nima tun ranar nake a kwance, sabili kawai da nace zan shiga na dubaka a Asibiti Alƙali ya koreni na dawo gida duk ba'a hayyacina ba na zame na faɗi a bakin ƙofa tun ranar se yanzu na iya yunƙurawa na fito da naji ance kun dawo nace gara na zo mu haɗu karna mutu a ɗaki har se nayi wari sannan aji a dubani tunda kowa ya tsaneni Matanka babu wadda tako leƙa taga ya nake ace dai kwanaki huɗu ba'a ga giftawata ba ai yaci a tuhumi lafiya dai amma babu wadda tayi" Hajiya Binta ta ringa rattaba zancen da seda ta kai ayarsa kafin ta lura da cewa ba Alhajin ne kaɗai a gurin ba, tayi sak kafin ta shiga rirriƙe hijabi duk ta diririce da gani base an faɗa ba kunya ce tayi mata rubdugu.
Alhaji ya nunata da hannu yana kallon wanda yafi sauran kalar jiƙuwa da kuɗi yace
"Gata nan, ita ce Surukar Ɗan naka". Wanda aka nunawa Hajita ya kalleta babu yabo babu fallasa kakar yanda sauran baƙin suke kallonta kowanne da yanayin da yake kan fuskarta yace
"Sannu Hajiya, ya me jiki? Ya kuma naki jikin?"
Babban abun ma shine bata san uban waye cikin surukan nata ba amma dai iyakar zubar da kai yau tayi ta tafka abin kunyar da ita da kanta yau ta gagara naɗe tabarmar kunya da haukan data saba ae jan Hijabi takeyi ita ba abin ta cire ta maidashi daidai ba duk ta rasa abinda zatayi. Momy tayi sallama cikin kyakykyawar shiga ta Abaya ta yafa yalwataccen Mayafi akai bayanta Maimuna ce da me aikinta Amirah kowacce da dogon Hijabi sun ɗauko manyan Trays. Har ta kalli Binta ta wuce ta samu gurin zama kan kujerun da suke daga gefe kaɗan, su Maimuna suka ajiue kayan hannunsu suka gaida baƙin kafin suka fita sa'annan suka shiga gaisawa da Momy cikin dattako da mutuntaka.
"Itace Matata ta biyu Mahaifiyar Ahmad" Alhaji ya gabatar da ita. Baban Sirikin Binta yayi murmushi yace
"Ga kama nan kuwa har jikin ma irin nata yayi baza'ace ita ta haifesu ba" Alhaji Audu ya É—anyi murmushi sega Hajiya Rabi nan itama ta shigo a kamalance da sallamarta ta zauna suka gaisa.
"Ga kuma Amaryata" Alhaji ya gabatar da ita". Hajiya Binta ta muzanta iya muzanta, wannan abu da Audu ya mata ya kaita wuya amma kamar wadda aka zubawa glue aka liƙe a gurin da take ta kasa gaba ta kasa baya haka ta gagara magana.
Momy da Hajiya Rabi suka miƙe a tare suka musu sallama suka fice, tun a hanya da suna dawowa daga Asibiti ya sanar da Hajiya Rabi, Alhaji Tamim Uban Mijin Hajiya Ƙarama yace yana tafe ze shigo dubashi dan yana Kano, ya sanar masa sun wuce gida basa Asibiti ya sameshi a can, shi yace ta gayawa Momy wadda take fushi dashi kan abinda ya faru. Sau ɗaya taje dubashi Asibiti amma kullum zatayi girki safe rana dare akai masa ita kuma Hajiya Rabi can zata wuni da dare ta dawo Ahmad ya Kwana dashi.
Abinda yasa yace a gaya mata zuwan baƙin yasab ba zata rasa abinda zata fitar dashi kunyarsu ba dan bata rabo da abubuwan motsa baki tunda yamma ce ba lokacin cin abinci bane ba gashi kuwa data tashi zuwa tazo musu da abubuwan taɓawar da ruwa da Lemo. Shi ya manta ma da Hajjajun seda ta shigo, yanda yaji kunya kuwa dai ba'a cewa komai amma ya godewa Allah da ba ita kaɗai yake aure ba, sedai a tafi da ita kaɗai a baki domin sauran matansa sun fitar dashi kunya.
Kamar sun manta da tsayuwar Hajiyar a gurin Alhajin ya musu Bismillah suka ɗan taɓa abinda aka kawo musu. Alhaji Tamim da Abokanan tafiyar tasa wayayyun mutanene suka shiga hirar kasuwanci inda ko wannensu yafi kauri. Hajiya ta gama tsayuwarta kafin ta miƙe ƙafafun da da yake cangalawa ta fice kamar kazar da Ƙwai ua fashewa a ciki. Tana fita ta haɗu da Faisal ta tsareshi da tambayar suwaye a Falon Alhaji.
"Baban Abba T ne" ya bata amsa, seta ɗora hannu biyu aka kafin kuma ta sauke da sauri har tana neman harɗewa ta wuce cikin gidan da saurin bala'i. Jikinta har rawa yake ta kira Hajiya Ƙarama, bata bari sun gaisa ba ta shiga surfa mata bala'i harda Allah ya isa akan.
"Kin huta yanzu ai se su dawo suyita bada labarin sunzo sun tarar da uwarki kamar mahaukaciya" ta faɗa tana rushewa da kuka kafin tayi cilli da wayar. Audu ya cuceta da be gaya mata su waye zasu zo ba yanzu yaja taje ta zubarda mutunchinta, surukin Hajiya ƙaramar ne kawai ya gaisheta amma tana gani da Aisha da Rabi suka ahiga duka harda sauran Abokanansa suka gaisa a mutunce ba irin tata gaisuqar daya mata ta jeka nayi ka ba. Ta sake zuge tazugen rashin mutunchi ta ayyana yanda zataci kan uban kowa a gidan tunda taga alamar raini ya fara shiga tsakaninta dasu kuma ba zata lamunta ba amma yanzu bari ta fara gamawa da zancen Yakubu tukunna shine Ƙayar da ya tsaya mata a wuya. Ta Alhaji Audu me sauƙi ce saboda tana da maganinsa a hannu, wurudin da Turai ta bata zata cigaba dayi tana banka masa yana sha ya dawo hayyacinsa dan taga alamar yana neman yafi ƙarfinta.
FATIMA
Ko a jikinta lissafin kwanakin zuwan Jay kawai takeyi wanda ita dashi sukeji kamar su janyo kwanakin su rage musu tsaho. Wani irin so da shaƙuwane a tsakaninsu, yanda suka damu da junansu suke tarairayar juna seya baka mamaki ba zaka ce soyayyar gani ɗaya bace kuma a waya akeyinta. Hatsaniyar da kayi a gidansu Jafar ɗin ce ta kawo tsaiko a zuwan nasa ya ƙara kwanakin zuwansa Nigeria da sati ɗaya akan yanda ya tsara dan abin ya faru yaɓa shi ya kuma ɓata masa rai matuƙa, idan yace zezo a lokacin da abun be idasa lafawa ba rigima zata dawo sabuwa ne domin dukda cewar baya son Fatima baya son auranta da Ahmad amma hakan bashi yake nufin ze zuba ido a Tozarta Ahmad ba, shi laifin Fatiman nema ya sake ninkuwa a zuciyarsa domin ta dalilinta ne aka yiwa Ahmad ɗin haka kuma ta zama silar da take neman sake janyo rarrabuwar kawuna a tsakaninsu saboda abinda ya faru dole ze sake tsanata gaba tsakanin Yayan Hajiyarsu da Su Hassan sannan a silar auranta Alhajinsu ya kwanta a Asibiti.
A ƙa'ida saura kwana uku yazo ranar yace mata an samu matsala se wani satin ze zo. Be gaya mata dalili ba, yanayin muryarsa da taji ta sakata tsurewa kodai wani abu tayi masa saya saka ya ɗaga zuwan? Cikin rawar murya kamar me son fashe masa da kuka ta tambayeshi dalili. Ya sassauto daga tunzurin da zuciyarsa take kai yace mata
"Babu komai, gidanmu ne babu lafiya an samu yar hatsaniya shiyasa kawai na ɗaga zuwan nawa saboda ze iya maido da ƙurar data lafa".
Bata fahimce shi ba amma tunda dai ba ita ta masa laifi ba ai da sauƙi. Ta ringa masa shagwaɓa da sangarta harda kukanta akan ya fasa zuwa jibi bayan ta fara shirin tarbarsa, wannan ya sanyaya masa zuciya ya shiga rarrashinta da mata Alƙawarurruka idan yazo kafin sukayi sallama ya ajiye waya.
'Ga mata nan irin su Afeeyah birjik a duniya akan Me Yah Ahmad ze nacewa waccen yari yar da babu komai tattare da ita se baƙin talauchi da sharri, daga maganar auranta ji abinda ya faru to inaga kuma ya aurota ya ajiyeta a gidansa ai se abinda Allah yayi kawai. Abin haushi da takaici kuma wai duk badaƙalar nan da akayi yanda Ahmad yace ko gezau beji soyayyarta tayi rawa a zuciyarsa ba tana nan daram dam shi dai yayi Allah wadai da So Ɗaya tak irin na Yah Ahmad' Tunanin Jay.