Sashe 58
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Haba Ruƙayya shin wai maganar nan ba zata mutu haka ba?" Baffa da tun daga soro ya tsinkayi mitar Umman ya faɗa bayan dayayi sallama. Ta kalleshi kafin tayi murmushi irin na zallar takaici tace
"Malam kenan, ai ba'a ma haifi maganar ba balle ta mutu, yanda mutanen unguwar nan basa raina abin magana idan bamuyi wasa ba ai fita seta gagaremu na wani lokaci saboda yanda za'a ringa zunÉ—en mu. A haka ma meye ba'a cewa duk akanta balle kuma aji wannan shegantakar Allah dai ya rufa asiri" ta fice daga falon ta barsu shida Afeeyah dake aikin kuka har sannan.
"Tashi kije ki kwanta" ya faɗa mata a sanyaye, tabbas Umman batayi ƙarya ba, tarayyar Afeeyah da Ahmad ba abinda mutanen unguwa basa faɗi wasu ma cewa suke lalatarsu kawai sukeyi amma idan ba haka ba Ƙanin uwarta ne kona ubanta ze ringa mata hidima haka?.
Jay kuwa da tunani kala kala fal kansa ya bar gidansu Afeeyah, ya ringa bulayi a loko dan ya manta ta inda suka shiga kuma shi kaÉ—ai ya fito, daidai Allah yasa ya ganshi a titi sedai ya banbanta da inda ya ajiye motarsa dakyar da tambaya ya koma kan Titin daya ajiyeta ya figi motar a tsiyace ya bar unguwar.
Abu goma da ashirin haka ya ringa saƙa da warwara. Be taɓa koda a hasashe hango Afeeyah ta fito daga irin low class family haka ba. Dukda bata yi masa ƙaryar ita yar masu Arziƙi bace dan ko magana sukeyi takan nuna masa batasan abubuwa da yawa da yake maganarsu ba seya ɗauka wasa takeyi seyau ya tabbatar ya kuma ganewa idanuwansa.
Asalinta ko matsayin mahaifinta be girgiza komai daga Son da yakeyi mata ba amma ƙaryar daya kamata dumu tayi masa ita ta hasalashi, seda ya tambayeta idan da wanda yake nemanta har iyayenta sun sani ta gaya masa tace babu. A duniya idan akwai abinda ya tsana be wuci wulaƙanci da ƙarya ba gashi ya kama wadda yake mutuwar so da dukka laifukan saboda shi ta masa ƙarya ta kuma wulaƙanta koma wanene take tare dashi bayan tsayin lokaci daya ɗauka lokaci yana hidima da ita, daga irin suturun da take sakawa kai ko fatarta ka kalla kasanba ƙaramar kulawa take samu ba ta mayuka masu inganci tabbacin koma wanene yana da buruka masu yawa akanta shiyasa baya ƙyashin kashe mata ko nawa ne amma ace lokaci ɗaya ta sutaleshi.
Tabbacin da yake dashi shine tana sonsa tunda gashi har mahaifinta ya faɗa shima kuma ya yarda da hakan domin ya gani a idonta ya kuma fahimci hakan daga ayyukanta badan haka ba shima ze ce tana da target akansa idan ta samu wanda ya fishi watsar dashi zatayi. Allah kenan, wato tasu ƙaddarar kenan shida Yah Ahmad soyayya da irin waɗannan yaran. Dalilin abinda yakeji akan Afeeyah yasa yaji ya farayiwa Ahmad uzuri bisa jure cin kashin da Fatima takeyi masa domin yanda yakejin Afeeyah a ransa ya tabbatar shidai baze zama sullutu irin Ahmad ba amma fa ko taƙi Allah ko bata sonsa se ya aureta a hakan sedai ta mutu tunda dai ya samu cikar burinsa amma shi ya zauna yana lallaɓata tana wulaƙantashi bayan yana da makaman da ze iya juya komai dasu se yanda ya tsara za'ayi.
PAGE 21
Ya isa gida yana fitowa daga mota ya hango Hajiya daga ƙofar shiga gurinsu tana tsaye kome take a daren se Allah dan goma ta gota tana hangoshi ta nufeshi da sauri.
"Hajiya lafiya? Meya fito dake a daren nan?" Ya faÉ—a sanda suka gamu, tace
"Ina fa lafiya, tun Mangariba nake nemanka a gidannan kowa yace besan inda kake ba na kira wayarka yafi sau shurin masaki baka amsawa".
Se ya zaro wayar daga Aljihu, tunda ze shiga gidansu Afeeyah ya latseta ta shiga silent shiyasa beji kiran Hajiyar ba. Hajiya data gama ƙare masa kallo daga sama zuwa Ƙasa tace
"Daga ina ka fito haka kaci uwar Gizina kamar wanda yaje gaisuwar surukai?"
"Sadik na raka" ya bata amsa yana shafa kai lokaci guda zuciyarsa ta shiga tsalle, tabbas da akwai gagarumar matsala domin dai ya sani ko sama da ƙasa zata haɗe idan shi yace yaji ya gani tofa Hajiya ba zata yarda da wannan haɗin ba, a tsarin zubi na halitta Afeeyah ta dace da Matar da Hajiyar take hakaito masa sedai yasan an saɓa lamba, yar talaka jikar talaka yace ze aureta tofa ya taro gagarumin yaƙi ne ta shiga wanda be zamar mata dole bama tayi kane kane inaga maganarsa? Ta yuwu shi ba a gida zatayi masa nasa taron ba fili zata siya a gidan Radio ko Jarida ta wanke shi tas ta Ahalin daya ke shirin jajibo mata a matsayin surukai.
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" ya faÉ—a a fili yana dafe kai, Hajiya da tayi magana harta gaji ya zuba mata ido kawai amma alamunsa sun nuna baya tareda ita, cikin hayagaga tace
"Da akayi me kake ja mana Innalillahi? Ina maka magana tuntuni ka tsareni da shegun idanunku na gado ko kuwa kana nufi kaima ba zaka shiga maganar bane?"
"Wace magana kuma Hajiya?" Ya tambaya yana dafe kansa daya shiga sara masa, hasaso Word War III ya tashi a gidan kwai yake da zarar maganar auransa ta fasu. Sati biyun da mahaifin Afeeyah ya bashi sunyi kaÉ—an daya shirya harya saita komai bisa tsari ta yanda koda wani abu ze biyo baya ya zamana bayan cikar burinsa.
"Muje ciki na gaji, rabona da bacci me daɗi har na manta ni kaɗai kamar wadda ta rabawa masifu goron gayyatar biko da wannan ta fita wannan seta shigo" Inji Hajiya ta juya tana jan ƙafafu. Matsalar Hajiya ƙarama ce take neman zautata, Shegen Mijinta da yayi musu lamɓo akayi aure tunda taje gidan nan a kullum sabon Episode yake haska musu na rashin mutunchi. Yanzu wai bata da lafiya sunje Asibiti an ce ciki ne da ita shine yace sedai a zubar ita kuma taƙi yace ta zaɓa ko aurenta ko cikin wai shekararsa Ashirin da takwas be isa ya fara tara yaya su tsufar dashi ba. Tun wancan satin ake jaraba data kirata ta gaya mata tace ta je ta sanarwa Babarsa matar dake bata da mutunchi a faɗar Hajiya Binta wai tacewa Hafsatun ita babu ruwanta bata shiga rayuwar yayanta yanda kowa ya ga dama haka yakeyi tunda yace baya son haihuwar yanzu seta haƙura idan kuma zaman auren ne bata so ga hanya nan yammata da yawa ze samo wata ya aura.
Yau taje gidan Turai suka tattauna shine tace ta samu cikin su Naziru ta saka wani ya kirashi ya masa magana dan tasan Alhaji dai baze shiga wannan batu ba ƙarshe kwancewa kanta zani zatayi a kasuwa kowa yasan halin da ake ciki to ta kira Naziru yace baya Gari, Zakariyyah yace yaron bashida mutunchi baze kirashi ya zageshi a banza ba Yakubu kuwa da tasu a tsakani daman bazata sako shi ba shine take ta neman Jafar wai shi ya shiga ya sasanta dan yanda Hafsatun tace tun jiya ya bar ƙasar ya tafi Dubai bisa rakiyar wata budurwarsa da har gida ta biyo masa suka tafi daman kuma ba baƙon abu bane Ƙawayensa mata sunfi Maza zuwa gidan haka zasu wuni a part ɗinsa idan tayi magana in be dake ta ba se ya gaya mata maganar da zata gwammaci dukan da ita.
"Zan kirashi da safe Hajiya" Jay faÉ—a bayan daya gama sauraronta. Ta muskuta tace
"Gara dai ka kira shi, ta yaya za'ayi banda shi ba ɗan Arziƙi bane yace baza'a haihu ba? Dan uwarsa da ba'a haihuwa shi zezo duniyar ne ko kuwa da ba'a haihuwa da yawa layi zezo na haifa masa yar ya aura ya ringa zuga mata rashin mutunchi? Billahillazi se tayi dozen kuma a ƙalla ciki maza takwas koma goma duk wannan jiji da kan da uwar sa takeyi dan ta haifi Namiji ɗaya tal se mun sauke mata shi Hafsatu zata cika gida musu gida da Yaya ta yanda in ubansu ya mutu aka tashi rabon gado za'a haɗa harda su".
Cike da mamaki yace
"Hajiya, ina kika taɓa ganin jika ya gaki Kakansa?"
"Za'a fara akansu" ta faɗi irin ko a jikinta seya miƙe bayan daya ce "Allah ya rufa asiri bari naje na kwanta"
'Kai wai se yaushe zaka nunamun surukar tawa ne? Kuma yar wace ƙasace? Ya kamata fa azo ayi abinda za'ayi tunda wuri dan auranka so nakeyi nayi biki na kece raini Wanda ba'a taɓa kamarsa a faɗin Najeriya ba" Hajiya ta dakatar dashi seya koma ya zauna ya lalubo wayarsa daga Aljihu, cikin hotunan da yayiwa Afeeyah ranar dayaje gidan Anty Sauda ya buɗe kunno mata ɗaya, ta fito sosai a tsaye dukda fuskarta babu fara'a amma tayi kyau kwarjininta ya fito sosai.
"Kai kai kai zankaɗi zuƙi, Jafaru a ina ka samo wannan ta Gabas ce ko Yamma?" Hajiya ta faɗa tana zooming hoton kafin tayi gaba tana kallon ragowar da sukayi tare, akan wanda ya rungumeta gaba ɗaya a jikinsa kanta na kafaɗarsa dan haka rabin fuskarta ne ya fito Hajiyar ta tsaya, kamar idanunta zasu faɗo haka take kallon wayar tace
"Kyau iya kyau gaskiya kun dace, turamun wannan shi zan nunasu Turai" ya karɓi wayar da take miƙa masa, kunyar kansa ta kamashi da yaga hoton ita kuwa Hajiya kacaniyar nemo wayarta takeyi tana maimaita a tura mata zata aikawa su Turai suga surukarsu
"Wayar ba caji zan tura miki da safe" ya miƙe,
"Ai shikenan Allah ya kaimu, kai zan iya bacci kuwa? Ganin wannan yarinyar ya wankemun haushin shegen Yaron can ma wlh. Kai Allah dai yayi maka Albarka kai kaÉ—ai ko yaushe baka bani kunya kana biye da tsarina yanda ya kamata.
"Malam kenan, ai ba'a ma haifi maganar ba balle ta mutu, yanda mutanen unguwar nan basa raina abin magana idan bamuyi wasa ba ai fita seta gagaremu na wani lokaci saboda yanda za'a ringa zunÉ—en mu. A haka ma meye ba'a cewa duk akanta balle kuma aji wannan shegantakar Allah dai ya rufa asiri" ta fice daga falon ta barsu shida Afeeyah dake aikin kuka har sannan.
"Tashi kije ki kwanta" ya faɗa mata a sanyaye, tabbas Umman batayi ƙarya ba, tarayyar Afeeyah da Ahmad ba abinda mutanen unguwa basa faɗi wasu ma cewa suke lalatarsu kawai sukeyi amma idan ba haka ba Ƙanin uwarta ne kona ubanta ze ringa mata hidima haka?.
Jay kuwa da tunani kala kala fal kansa ya bar gidansu Afeeyah, ya ringa bulayi a loko dan ya manta ta inda suka shiga kuma shi kaÉ—ai ya fito, daidai Allah yasa ya ganshi a titi sedai ya banbanta da inda ya ajiye motarsa dakyar da tambaya ya koma kan Titin daya ajiyeta ya figi motar a tsiyace ya bar unguwar.
Abu goma da ashirin haka ya ringa saƙa da warwara. Be taɓa koda a hasashe hango Afeeyah ta fito daga irin low class family haka ba. Dukda bata yi masa ƙaryar ita yar masu Arziƙi bace dan ko magana sukeyi takan nuna masa batasan abubuwa da yawa da yake maganarsu ba seya ɗauka wasa takeyi seyau ya tabbatar ya kuma ganewa idanuwansa.
Asalinta ko matsayin mahaifinta be girgiza komai daga Son da yakeyi mata ba amma ƙaryar daya kamata dumu tayi masa ita ta hasalashi, seda ya tambayeta idan da wanda yake nemanta har iyayenta sun sani ta gaya masa tace babu. A duniya idan akwai abinda ya tsana be wuci wulaƙanci da ƙarya ba gashi ya kama wadda yake mutuwar so da dukka laifukan saboda shi ta masa ƙarya ta kuma wulaƙanta koma wanene take tare dashi bayan tsayin lokaci daya ɗauka lokaci yana hidima da ita, daga irin suturun da take sakawa kai ko fatarta ka kalla kasanba ƙaramar kulawa take samu ba ta mayuka masu inganci tabbacin koma wanene yana da buruka masu yawa akanta shiyasa baya ƙyashin kashe mata ko nawa ne amma ace lokaci ɗaya ta sutaleshi.
Tabbacin da yake dashi shine tana sonsa tunda gashi har mahaifinta ya faɗa shima kuma ya yarda da hakan domin ya gani a idonta ya kuma fahimci hakan daga ayyukanta badan haka ba shima ze ce tana da target akansa idan ta samu wanda ya fishi watsar dashi zatayi. Allah kenan, wato tasu ƙaddarar kenan shida Yah Ahmad soyayya da irin waɗannan yaran. Dalilin abinda yakeji akan Afeeyah yasa yaji ya farayiwa Ahmad uzuri bisa jure cin kashin da Fatima takeyi masa domin yanda yakejin Afeeyah a ransa ya tabbatar shidai baze zama sullutu irin Ahmad ba amma fa ko taƙi Allah ko bata sonsa se ya aureta a hakan sedai ta mutu tunda dai ya samu cikar burinsa amma shi ya zauna yana lallaɓata tana wulaƙantashi bayan yana da makaman da ze iya juya komai dasu se yanda ya tsara za'ayi.
PAGE 21
Ya isa gida yana fitowa daga mota ya hango Hajiya daga ƙofar shiga gurinsu tana tsaye kome take a daren se Allah dan goma ta gota tana hangoshi ta nufeshi da sauri.
"Hajiya lafiya? Meya fito dake a daren nan?" Ya faÉ—a sanda suka gamu, tace
"Ina fa lafiya, tun Mangariba nake nemanka a gidannan kowa yace besan inda kake ba na kira wayarka yafi sau shurin masaki baka amsawa".
Se ya zaro wayar daga Aljihu, tunda ze shiga gidansu Afeeyah ya latseta ta shiga silent shiyasa beji kiran Hajiyar ba. Hajiya data gama ƙare masa kallo daga sama zuwa Ƙasa tace
"Daga ina ka fito haka kaci uwar Gizina kamar wanda yaje gaisuwar surukai?"
"Sadik na raka" ya bata amsa yana shafa kai lokaci guda zuciyarsa ta shiga tsalle, tabbas da akwai gagarumar matsala domin dai ya sani ko sama da ƙasa zata haɗe idan shi yace yaji ya gani tofa Hajiya ba zata yarda da wannan haɗin ba, a tsarin zubi na halitta Afeeyah ta dace da Matar da Hajiyar take hakaito masa sedai yasan an saɓa lamba, yar talaka jikar talaka yace ze aureta tofa ya taro gagarumin yaƙi ne ta shiga wanda be zamar mata dole bama tayi kane kane inaga maganarsa? Ta yuwu shi ba a gida zatayi masa nasa taron ba fili zata siya a gidan Radio ko Jarida ta wanke shi tas ta Ahalin daya ke shirin jajibo mata a matsayin surukai.
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" ya faÉ—a a fili yana dafe kai, Hajiya da tayi magana harta gaji ya zuba mata ido kawai amma alamunsa sun nuna baya tareda ita, cikin hayagaga tace
"Da akayi me kake ja mana Innalillahi? Ina maka magana tuntuni ka tsareni da shegun idanunku na gado ko kuwa kana nufi kaima ba zaka shiga maganar bane?"
"Wace magana kuma Hajiya?" Ya tambaya yana dafe kansa daya shiga sara masa, hasaso Word War III ya tashi a gidan kwai yake da zarar maganar auransa ta fasu. Sati biyun da mahaifin Afeeyah ya bashi sunyi kaÉ—an daya shirya harya saita komai bisa tsari ta yanda koda wani abu ze biyo baya ya zamana bayan cikar burinsa.
"Muje ciki na gaji, rabona da bacci me daɗi har na manta ni kaɗai kamar wadda ta rabawa masifu goron gayyatar biko da wannan ta fita wannan seta shigo" Inji Hajiya ta juya tana jan ƙafafu. Matsalar Hajiya ƙarama ce take neman zautata, Shegen Mijinta da yayi musu lamɓo akayi aure tunda taje gidan nan a kullum sabon Episode yake haska musu na rashin mutunchi. Yanzu wai bata da lafiya sunje Asibiti an ce ciki ne da ita shine yace sedai a zubar ita kuma taƙi yace ta zaɓa ko aurenta ko cikin wai shekararsa Ashirin da takwas be isa ya fara tara yaya su tsufar dashi ba. Tun wancan satin ake jaraba data kirata ta gaya mata tace ta je ta sanarwa Babarsa matar dake bata da mutunchi a faɗar Hajiya Binta wai tacewa Hafsatun ita babu ruwanta bata shiga rayuwar yayanta yanda kowa ya ga dama haka yakeyi tunda yace baya son haihuwar yanzu seta haƙura idan kuma zaman auren ne bata so ga hanya nan yammata da yawa ze samo wata ya aura.
Yau taje gidan Turai suka tattauna shine tace ta samu cikin su Naziru ta saka wani ya kirashi ya masa magana dan tasan Alhaji dai baze shiga wannan batu ba ƙarshe kwancewa kanta zani zatayi a kasuwa kowa yasan halin da ake ciki to ta kira Naziru yace baya Gari, Zakariyyah yace yaron bashida mutunchi baze kirashi ya zageshi a banza ba Yakubu kuwa da tasu a tsakani daman bazata sako shi ba shine take ta neman Jafar wai shi ya shiga ya sasanta dan yanda Hafsatun tace tun jiya ya bar ƙasar ya tafi Dubai bisa rakiyar wata budurwarsa da har gida ta biyo masa suka tafi daman kuma ba baƙon abu bane Ƙawayensa mata sunfi Maza zuwa gidan haka zasu wuni a part ɗinsa idan tayi magana in be dake ta ba se ya gaya mata maganar da zata gwammaci dukan da ita.
"Zan kirashi da safe Hajiya" Jay faÉ—a bayan daya gama sauraronta. Ta muskuta tace
"Gara dai ka kira shi, ta yaya za'ayi banda shi ba ɗan Arziƙi bane yace baza'a haihu ba? Dan uwarsa da ba'a haihuwa shi zezo duniyar ne ko kuwa da ba'a haihuwa da yawa layi zezo na haifa masa yar ya aura ya ringa zuga mata rashin mutunchi? Billahillazi se tayi dozen kuma a ƙalla ciki maza takwas koma goma duk wannan jiji da kan da uwar sa takeyi dan ta haifi Namiji ɗaya tal se mun sauke mata shi Hafsatu zata cika gida musu gida da Yaya ta yanda in ubansu ya mutu aka tashi rabon gado za'a haɗa harda su".
Cike da mamaki yace
"Hajiya, ina kika taɓa ganin jika ya gaki Kakansa?"
"Za'a fara akansu" ta faɗi irin ko a jikinta seya miƙe bayan daya ce "Allah ya rufa asiri bari naje na kwanta"
'Kai wai se yaushe zaka nunamun surukar tawa ne? Kuma yar wace ƙasace? Ya kamata fa azo ayi abinda za'ayi tunda wuri dan auranka so nakeyi nayi biki na kece raini Wanda ba'a taɓa kamarsa a faɗin Najeriya ba" Hajiya ta dakatar dashi seya koma ya zauna ya lalubo wayarsa daga Aljihu, cikin hotunan da yayiwa Afeeyah ranar dayaje gidan Anty Sauda ya buɗe kunno mata ɗaya, ta fito sosai a tsaye dukda fuskarta babu fara'a amma tayi kyau kwarjininta ya fito sosai.
"Kai kai kai zankaɗi zuƙi, Jafaru a ina ka samo wannan ta Gabas ce ko Yamma?" Hajiya ta faɗa tana zooming hoton kafin tayi gaba tana kallon ragowar da sukayi tare, akan wanda ya rungumeta gaba ɗaya a jikinsa kanta na kafaɗarsa dan haka rabin fuskarta ne ya fito Hajiyar ta tsaya, kamar idanunta zasu faɗo haka take kallon wayar tace
"Kyau iya kyau gaskiya kun dace, turamun wannan shi zan nunasu Turai" ya karɓi wayar da take miƙa masa, kunyar kansa ta kamashi da yaga hoton ita kuwa Hajiya kacaniyar nemo wayarta takeyi tana maimaita a tura mata zata aikawa su Turai suga surukarsu
"Wayar ba caji zan tura miki da safe" ya miƙe,
"Ai shikenan Allah ya kaimu, kai zan iya bacci kuwa? Ganin wannan yarinyar ya wankemun haushin shegen Yaron can ma wlh. Kai Allah dai yayi maka Albarka kai kaÉ—ai ko yaushe baka bani kunya kana biye da tsarina yanda ya kamata.