← Book details Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 45 OF 71

Sashe 45

Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A maimakon tayi masa magana kawai se gani yayi hawaye ya fara mata tsere dan da hasken Nepa tar a ƙofar gidan, ya buɗe baki yana kallonta da mamaki kafin yayi magana ta juya da sauri ta shige gida tana cigaba da kukan. Yayi kasaƙe a gurin, shi ba abin ya bita ciki ba mamakin dalilin kukanta ya rufeshi. Yana tsaye Baffa ya fito be ankate ba seda ya kira sunansa.
"Malam Ahmad lafiya kuwa naga ta shiga gida tana kuka ko wani abu ne ya faru?" Baffan ya tambayeshi. To shi me zece masa yanzu? Gaskiya ze faÉ—a masa ko kuwa yayi shiru Baffan ya zargi wani abun yayiwa yarsa?

"Wlh Baffa babu abinda ya faru, tambayarta kawai nayi ta amince na turo iyayena shine ta fara kuka ko magana batayi bama ta wuce ciki" ya faÉ—a cikin rawar murya. Baffa yayi ajiyar zuciya yace
"Kayi tafiyarka kayi abinda nace maka in har da gaske kake son aurenta ka turo magabatanka"
"Nagode Baffa in sha Allahu zaka jini bada daɗewa ba" daga nan yayiwa Baffa Sallama ya wuce, farin cikin daya samu dalilin ganinta ya gushe, har wani ciwon kai yaji yana neman kamashi kukan Fatima ya tabbatar masa da gaske bata sonsa tilas ya haƙura da wannan yarinyar muddin ba rabuwa da ita ne Ajalinta ba.

A can gidansu Fatima kuwa bayan Baffa ya koma ciki tarar da ita yayi tana sharɓar kuka Umma na tsaye kanta tana faɗa kamar zata rufeta da duka.
"Ya isa Zara'u rabu da ita" Baffa ya faÉ—awa Umman, ta zauna tana tsaki, ji take kamar ta rufe Afeeyar da duka ko zata maidata cikin hayyacinta.

"Duk menene dalilin wannan abun? Me ya sakaki kuka daga yace ze turo magabatansa dama bakya sonsa ne ko kuwa ra'ayi kika canza?" Baffa ya tambayeta. Bata amsashi ba se kuka da takeyi ƙasa ƙasa. Umma ta jefeta da takalmi tana cewa
"Ba magana ake miki ba kinaji kinyi shiru?"
"Nace ki barta Zara'u ko?" Baffa ya faɗa a ɗan fusace. Umma tayi ƙwafa ta wuce ɗakinta. Baffa ya sake duban Afeeyah, yanda taji muryarsa ta tabbata ransa a ɓace yake ta san kuma fushi ba ɗabi'arsa bace tabbas ta kaishi bango ne dan haka yana sake maimaita mata tambayar jiki na rawa taja baya daga kusa dashi kafin tace

"Ni daman Baffa ban taɓa cewa ina sonsa ba kawai bazan iya wulaƙantashi bane amma duk wata alama da ya kamata na nuna masa nayi amma yaƙi ya haƙura".

Baffa ya ringa kallonta har tayi shiru, yafi minti goma kafin ya iya cewa
"Kina nufin tsayin shekara uku da yaron nan yake bibiyarki yana wahalta miki duk ya tashi a banza yanzu zakice ba sonsa kikeyi ba?"

"Wlh Baffa ni ban taɓa cewa yayi mun abu ba, kuma ai ko kai kana hanashi amma se ya dage se yayi kuma ni ina gaya masa ya dena kawai shine baya ji"

Umma ta leƙo a fusace tace
"Dan ubanko dole yanzu kice bakya sonsa mana kuma bake kika saka ya ringa miki wahala ba, Kare ne shi da ze shekara uku saboda rashin zuciya yana tare dake kina nuna masa rashin So kuma yaci gaba da zama dake? Kin gama yaudarar sa kin ɓata masa lokaci saboda baki da mutunchi yanzu zakice bakya Son sa me yasa tun farko baki faɗawa Malam ɗin ba shi da kansa ya kirashi ya sallame shi se yanzu da koɗaɗɗiyar fuskarki zakicewa mutane ke daman bakya son sa to wlh baki isa ba" Umma ta shiga sababi harta manta darene ta muryarta a sama.

Baffa daya kasa magana tuntuni ya kalli Fatima yace ta wuce ɗaki, sum sum ta shige tana jin kamar an sauke mata wani nauyi daga kanta tunda har ta iya furtawa Baffa bata ra'ayin Ahmad tasan magana ta ƙare. A ɗaki Umma ta warwarewa Baffa komai game da zancen Yaron da Afeeyah take so wato Jay ɗan Ƙwallo.
"A ina suka haÉ—u?" Ya tambayi Umman, ta watsa hannu kafin tace
"Wai acan makarantarsu, Malam ka sanarwa Yaron nan kawai ya turo Iyayensa suzo a ɗaura musu aure kawai idan yaso ta mutu ƙarshen rashin Son Sa".

"Ba za'ayi haka ba, za'a bi komai a hankali, magita zata samu da yardar Allah" inji Baffa. Daren raba shi yayi yana sallah da addu'oi, ya kasance me yawan tsayuwar dare amma yau Umma tasan sallar tasa harda ta neman ɗauki gurin Allah kan wannan abin daya tunkaro shi. Baffa na Son Afeeyah, amma abu ɗaya da tayi imani dashi shine baze bi Son rai ya zubar da ƙimar sa ba shiyasa ya maida lamarin ga buwayin sarki gagara Misali wanda duk hukuncin daya yanke babu wanda ya isa yayi inkari akai.

Kwanaki uku Baffa ya jera yana Istikara cikin tareda tsananta Addu'a da roƙon ubangiji akan Al'amarin, Afeeyah kuwa rai fes dan Ahmad be sake kiranta ba tunda ya tafi kuma ta furta abinda yake ranta dan tasan Umma ta gayawa Baffa zancen Jay babban abinda ya sakat nishaɗi da farin ciki kuma shaida mata da Jay yayi yana tafe Nigeria nan da sati biyu masu zuwa. Saura kwana biyar su koma makaranta semester ƙarshe ce babu Lectures da yawa se aikin project da abinda baza'a rasa ba dan haka ta yanke ba zata koma bahar se yazo tukunna abinda bata taɓayi ba ƙarin hutu tunda ta fara University.

Ta gayawa Badar Jay yana tafe, Badar nason Jay da Afeeyah amma ba kamar yanda take sonta da Ahmad ba kamar yanda take ce mata Ahmad Mijin Aurene Jay kuma na rage lokaci da neman suna domin ita dai bataji a jikinta Jay auran Afeeyah zeyi har yanzu ba duk kuwa da tarin ƙaunar da yake nuna mata akan haka har faɗa suka sakeyi ta dai rabu da ita tana kuma yi mata addu'a a matsayinta na ƙawarta.

Takanas taje gidan Anty Sauda tace mata nan zata fara kawo Jay kafin Umma ta sauka daga fushin da takeyi da ita tukunna se ta kaishi gidan.
"Yanzu kina ganin abinda kika zaɓawa kanki daidai ne Afeeyah?" Anty Sauda wadda Umma ta gaya mata duk abinda ya faru ta tambayeta.
"Haba Anty dan Allah wai ana aure dole ne? Naga kema zaɓi aka baki kika kawo wanda kike so me yasa ni ake nema a tauye mun haƙƙi?" Ta jefawa Anty Saudan tambaya. Seta girgiza kai kawai tace mata Allah ya kawo Jafar ɗin lafiya, bata wani jima ba ta koma gida dukda zaman gidan ba wani daɗi yake mata ba yanzu saboda yanda Umma ta canza mata. Daga ita har Baffa babu wanda ya mata zancen ganinbata koma makaranta bama se Yah Malam daya zo hutu ne yace ya ya ganta a gida tace se wani satin zata koma. Baffabe canza mata kamar Umma ba dan ze amsa gaisuwarta har ya sakata aikace aikace kamar yanda ya saba amma Umma ko gaiseta tayi da harara take amsa mata tti duk yanda zatayi Umman ta sakko amma abu yaci tura tasan dai fushin Umma akan Ahmad ne addu'a takeyi Allahya kawo Jafar wanda yace zuwa ɗaya zeyi kafin yayi na biyu za'a tambaya masa auranta dan ya matsu.

"Yah Ahmad ka dena sona wlh, yanzu ace zanzo gida amma babu wani murna ko ɗokin gani na daka sabayi kawai Allah ya kaimu shikenan abinda zaka ce?" Jafar ya dasawa Ahmad mita akan beyi murna daya ce masa zezo gida ba. Ahmad daya kwanta zazzaɓin malaria kamar yanda yayiwa Momy ƙarya amma gaskiyar abinda yake damunsa Love sickness ne. Tun ranar daya baro gidansu Fatiman damuwa ta saukar masa da ciwon kai da zazzaɓi me zafi amma haka yake bankar Anti Malaria da Momy tasa dole yaje asibiti aka rubuto masa.

"I told you bani da lafiya Jafar amma kana ta so se ka sakani magana"
"Ni ai bazanyi maka sannu ba saboda wannan ciwon kai ka É—orawa kanka, let me ask you please, is this Fatima made of Gold or some sort of precious stone da tayi deserving wannan soyayyar da kakeyi mata?
Yah Ahmad me yake damunka? For heaven sake kana nema ka kashe kanka akan wata banzar mace? Is she the only living woman on earth? Ko dai asiri tayi maka? Oh na manta mayyace believe me ta cinye maka zuciya kuma wlh bata isa ba. Ko waye ubanta she must leave you, seta fita a rayuwanka let me come back first I'm going to deal with her personally, se ta gane bata da hankali wlh" ya ringa sababi kamar ze aro baki daman kuskure Ahmad yayi daya taso masa da maganar gashi yana neman ya sake ƙara masa ciwo.

"I love her, kuma banajin zan iya dena sonta idan da abinda zakayi kasa ta soni i will appreciate it more zaginta da kakeyi dan baka san abinda nake ji bane ba nidai idan kana sona da gaske just help me fight na samu Fatima" Ahmad ya faɗa. Jafar yayi shiruj irin wanda takaici ya gama tiƙewa kafin yace

"Indai haka ne ze sa ka yarda Ina sonka then I don't love you Yah Ahmad and i will never love you indai se naso wannan yarinyar ne ka cireni a jerin ƙannenka, i hate her, i hate her with all my life kuma ko Allah yasa ka aureta bazan taɓa shiga gidanka ba" yana gama magana ya kashe wayansa yanda Ahmad ya jishi yasan ba ƙaramin zafi ya ɗauka ba. Yayi murmushi, yasan rigimar Jafar na lokaci ne zuwa anjima ze sake kiransa kawai dai wannan ƙiyayyar da yakeyi mata me zafi ce ya rasa dalilinta, saboda shine kuma yanzu so yakeyi ya haƙura da ita ba shikenan ba.

****************

"Alhaji, ni tun kwanaki naji kana zancen Amadu ya samu mata ko? Ashe ma ya taɓa kaiwa Ummu ita, se jiya da muke magana Jafaru yace daya zo za'aje masa neman aure shine tace mun zancen ai taga budurwar Amadun ma ya ɗaukota daga makaranta suka biya gidanta wai ya karɓowa Aisha Leshi, wai a Zaria take makaranta, nace Yayan masu kuɗi suna zuwa wannan makarantar kuwa?"
Chapter 45 · 0% Book details