Sashe 39
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sannu a hankali soyayya da shaƙuwa me ƙarfi ta shiga tsakaninta da Jay, wani irin so take masa da bata san iyakarsa ba, kodan ya dace da duk wani mafarki nata akan Mijin da take so t aura ne oho?
Ahmad da kansa ya gane cewar akwai wani al'amari a gabanta wanda ya sake karkatar da hankalinta daga kansa saboda yar hirar da yake samun dama sunayi ma yanzu gagara takeyi, duk sanda ze kirata uzuri zata bashi na tana wani abun musamman da suka fara Second semester exam daga tace masa karatu takeyu se ta gaji zata huta alhalin lokacinta karankaf yanzun na Jay ne, karatun kansa ba wani mayar da hankali takeyi kamar da ba da idan akace zasu fara exam da sati ɗaya ma ta dena hawa Social media tattara hankalinta take tsaf har se sun gama sannan to wannan karon kuwa se a hankali, idan tana waya da Jay manta kowa da komai takeyi bata ma son abinda ze katseta se su raba dare suna magana har se da kansa yace ta kwanta tayi bacci dan bata faɗa masa ma mun fara exam ba seda sukayi guda huɗu ya rage uku su gama sannan ranar kuwa tasha fada ta kuma ƙara tabbatar da Jay baya ɗaukar nonsense dagaske kamar yanda yake cewa.
Har yajin kiranta yayi na wuni guda aikuwa taji a jikinta dan ya mata mugun sabo da soyayyarsa me tsayawa a rai. Jay ya iya soyayya, ya iya saka mace ta manta kanta duk taurin zuciyar Mace idan ta shiga hannun Jay tilas ta sallama dan yasan duk wani lago na mace da ze karya ta dashi, ita da kanta ta kance salon Jay da Ahmad yana kama. Tabbas da ta bawa Ahmad dama ta buÉ—e masa zuciyarta ze mallaketa tsaf ta yanda wani baze samu matsuguni ba amma ta rasa abinda ya hanata yin hakan, ta yuwu dalilin zuwan Jay ne, wani lokacin se taji muryoyinsu har kamanceceniya yake mata kawai dai ta Jay tafi ta Ahmad tashi, haka idanunsu iri É—ayane, seda tayiwa hoton Jay kallo na tsanaki ta fahimci haka idanunsu iri É—ayane, shape É—insu, kalar kwayar idon da komai Badar tace mata wai Sexy Eyes kenan masu irin idanun sun iya soyayya kuma dasu suke cafke zukatan Yammata ta yarda da hakan dan bata iya haÉ—a ido da Ahmad se taji gabanta na faÉ—uwa duk sanda ta kalli idonsa ji take kamar ta sallama masa amma taurin kai irin nata ya sa har aka kawo i yanzu.
Saura kwana biyu su gama Exam ranar Ahmad ya kirata, kwana biyu ya bata space tunda tace masa Exam sukeyi idan ya kira bata ɗaga ba kota amsa ta bashi uzuri sosai ransa yake sosuwa shiyasa ya zaɓi daya barta ta gama exam ɗin idan har da gaske itace uzurin daya saka baya samun lokacinta. Tana kwance duk batajin daɗin dalilin yajin kiran wayar da Jay ta daka mata, tunda ya fahimci Exam suke kuma take wasa da karatunta tana biye masa shine yayi fushi. Ya gaya mata baya son mutumin da bashida focus, yana sonta amma baze taɓa haɗa lokacinta da Aikinsa ba me yasa ita zatayi wasa da Karatunta saboda shi?
Yace baze sake kiranta ba se sun gama kuma ta tura masa da Time table sannan idan ma ta kirashi baze amsa baz kullum da safe ze mata text haka da rana da dare amma babu phone call saboda magana dashi yasa takeji kamar wata mashashshara ce ta kamata duk ta rasa gane kanta. Tana ganin wayarta na ringing ganin Ahmad ne kamar ba zata amsa ba se kuma ta É—aga dalilin tunanin da tayi a ranta, tabbas Alhakin Ahmad ne tun ba'a je ko ina ba Allah ya jarabceta da Jay.
A sanyaye suka gaisa daga ita harshi babu wani me karsashi,
"Yaya Exam ɗin? Saura guda nawa ku gama?" Ya kauda shirun da sukayi bayan gaisuwa ta bashi amsa a taƙaice da
"Lafiya lau, saura biyu"
"Masha Allah, Allah ya bada sa'a" daga nan suka sakeyin wani shirun. Ya sani idan zasu kwana a haka ba lallai ta sake cewa komai, wlh daze iya da ya rabu da yarinyar nan dan duk wata hanya da mace zata nuna bata ra'ayin mutum ta nuna masa amma zuciyarsa ta kasa haƙura da ita. A kullum cikin Addu'a yake akan idan babu Alkhairi a tarayyarsu Allah ya cire masa ita daga zuciyarsa ya musanya masa da wadda ta fita amma abun kamar ana rura wuta ƙaruwa yakeyi.
Idan Jafar yana bashi labarin sabuwar soyayyar daya gamu da ita se yace shi kam bashida sa'a ne a soyayya da Alama. Bega Yarinyar da Jay yake so ba, amma yanda har Jay yake labarinta ya sani ba ƙaramin sonta yakeyi ba itama kuma tana riritashi, ze iya cewa be taɓa ganin Jafar a yanayi na soyayyar gaskiya irin wannan ba, yace masa auran yarinyar zeyi, Bahaushiyace yar Nigeria a Zaria suka haɗu. Yaƙi ko gaya masa sunanta dayace ya tura masa hotonta ya nunawa Fatima ko ta santa nan ya fitittike ya ringa zuba masa Tijara yace kuma baze tura ba se ya dawo zasuje ya ganta face to face ko sunanta baze gaya masa ba balle ya faɗawa Fatiman.
"Tana da Friends haÉ—aÉ—É—u irinta zan samo maka guda É—aya ka fita daga sabgar waccen Ajawon Fatiman da take wahalar da kai Yaya Ahmad" abinda Jay ya gaya masa.
Ahmad yaja numfashi, kusan minti bakwai daga shi har Fatima babu wanda yace wani abu. A sanyaye yace
"Fatima, idan wani laifi nayi miki kiyiwa girman Allah ki sanar mun na baki haƙuri, na gaji da azabatar da zuciyata da kikeyi kusan sati uku kenan kin hanani zaman lafiya nace zanzo kince Aa, idanna kiraki a waya koda yaushe cikin bani Excuse kike me nayi miki? Idan maganar kai gaisuwa da nayi ce kince Aa kuma na haƙura bayan wannan wane laifi nayi miki da kike hukuntani ta hanyar azabtar da zuciyata haka?"
A maimakon ta sassauta se maganganunsa suka sake ƙukar da ita, ta tsani Namiji da bashida ra'ayin kansa se abinda mace tace yayi wannan yana daga abinda bata so da Ahmad yanda yake mata wani lako lako kamar ita ce Namijin shine macen, to tun yanzu baya iya taɓuka komai daga abu ya haɗa m
Su ya fara kamar zeyi kuka yana lallaɓata idan sunyi auren kenan baze ringa tsawatar mata ba idan tayi masa laifi. Haɗuwarta da Jay tasa ta ƙara fahimtar banbancin Namiji da muna Maza, duk yanda yake nuna So ta yake riritata idan tayi masa abinda be gamshe shi ba murɗewa yakeyi ita ce zatayi ta lallashinsa da ban baki kafin ya sakko kamar dai yanzu daya yi fushi saboda bata maida hankali akan Exam ɗinta ba ta tabbata da Ahmad ne tsayawa zeyi yana lallashinta akan tayi kaza ko kartayi.
"Dan Allah Fatima ki tausaya mun. Na sani bakya sona Alfarma kike mun ina roƙon da ki daure kici gaba, ki dubi kalar jarabawar da nake ciki ta Sonki ki tausaya mun. Wlh Fatima da zan iya da tuni na cireki daga raina na rabu dake, koda baki taba buɗe baki kin gaya mun ba nida kaina nasan bakya sona kina kulani ne kawai saboda wulaƙnta ɗan Adam ba tarbiyyarki bace kuma na gode da hakan. Bazan gaji da roƙonki na akan ki bani dama, ki bude mun zuciyarki ko yaya ne in Allah ya yarda ba zakiyi nadamar tarayya dani ba" Ahmad ya sake faɗa a sanyaye.
Zuciyarta tayi rauni da jin abinda ya ke cewa, wato shi da kansa yasan bata sonsa amma ya gaza haƙura da ita tashi jarabawar Sonta ita kuma tata Son Jay Allah kenan.
Ajiyar zuciya ta sauke na shaking tace
"Nifa Ahmad ba haka bane ba, na gaya maka exam mukeyi ina buƙatar isashshen lokaci saboda nayi karatu shiyasa duk wani waya da wani chat na ajiye su amma mun kusa gamawa nan da Three days In sha Allah".
Yayi murmushi da jin abinda tace shima yace
"Ranar Thursday kenan zaku gama?" Ta yatsina fuska kamar yana kallonta tace eh, se ya sake cewa a sanyaye
"To yaushe zaki dawo Kano?"
"Paper safe ce, in har na gama komai kafin 12 ma zan taho a ranar in Allah ya yarda"
"To nazo na ɗakko ki?" Ya faɗa da sigar roƙo kamar wani me magana da ogarsa a gurin aiki, bata san sanda tsaki ya subuce mata ba tace
"Zan dawo da kaina, kasan Baffa ya hana ai ka ringa barin aikinka kana tahowa hidimata".
"Dan Allah Fatima karkice Aa kar kuma ki jingina maganar nan da Baffa sedai idan bakya sone kawai sena haƙura" ya sake faɗa gwanin ban haushi kuma ban tausayi kamar ze mata kuka, babu yanda ta iya haka ta yarda akan yazo ya ɗauketa, ita kanta zata ji daɗin hakan saboda hutun Session ne zata tafi da duka kayanta.
Ya ringa zabga mata godiya kamar wanda tayiwa kyauta daga ƙarshe sukayi sallama bayan ya sake roƙarta akan dan Allah ko sau ɗaya ne a rana idan ya kirani ta ringa amsawa gaisawa kaiwai zasuyi baze ja mata lokaci ba tace Toh.
"Allah sarki Ahmad, wlh yana bani tausayi na daÉ—e banga soyayya me zafi irin wadda yakeyi miki ba Afeeyah,dan Allah ki tausayawa mutumin nan yaci Albarkacin so wlh na tabbatar ba zaki yi nadamar auransa ba saboda yana sonki" Badar ta faÉ—a, Afeeyah ta hararaeta tace
"Kyaji da fuska biyunki anjima idan Jay ya kira waya jikinki na rawa zakiyita karaÉ—i kina bashi assurance na ze sameni ke ga campaign coordinator kuma se na gaya masa abinda kike cewa yanzu"
"Amma Thruth to be told Afeeya wlh Ahmad yafi sonki, ki gani fa shekara biyu yana binki kina jansa a ƙasa na tabbata Jay baze ɗauki haka ba Mace ta ringa wasa dashi kamar wani Toy, da yanzu ya daɗe da sallama ki" Badar ta sake faɗa. Afeeyah ta tashi zaune daga kwanciyar da take tace
Ahmad da kansa ya gane cewar akwai wani al'amari a gabanta wanda ya sake karkatar da hankalinta daga kansa saboda yar hirar da yake samun dama sunayi ma yanzu gagara takeyi, duk sanda ze kirata uzuri zata bashi na tana wani abun musamman da suka fara Second semester exam daga tace masa karatu takeyu se ta gaji zata huta alhalin lokacinta karankaf yanzun na Jay ne, karatun kansa ba wani mayar da hankali takeyi kamar da ba da idan akace zasu fara exam da sati ɗaya ma ta dena hawa Social media tattara hankalinta take tsaf har se sun gama sannan to wannan karon kuwa se a hankali, idan tana waya da Jay manta kowa da komai takeyi bata ma son abinda ze katseta se su raba dare suna magana har se da kansa yace ta kwanta tayi bacci dan bata faɗa masa ma mun fara exam ba seda sukayi guda huɗu ya rage uku su gama sannan ranar kuwa tasha fada ta kuma ƙara tabbatar da Jay baya ɗaukar nonsense dagaske kamar yanda yake cewa.
Har yajin kiranta yayi na wuni guda aikuwa taji a jikinta dan ya mata mugun sabo da soyayyarsa me tsayawa a rai. Jay ya iya soyayya, ya iya saka mace ta manta kanta duk taurin zuciyar Mace idan ta shiga hannun Jay tilas ta sallama dan yasan duk wani lago na mace da ze karya ta dashi, ita da kanta ta kance salon Jay da Ahmad yana kama. Tabbas da ta bawa Ahmad dama ta buÉ—e masa zuciyarta ze mallaketa tsaf ta yanda wani baze samu matsuguni ba amma ta rasa abinda ya hanata yin hakan, ta yuwu dalilin zuwan Jay ne, wani lokacin se taji muryoyinsu har kamanceceniya yake mata kawai dai ta Jay tafi ta Ahmad tashi, haka idanunsu iri É—ayane, seda tayiwa hoton Jay kallo na tsanaki ta fahimci haka idanunsu iri É—ayane, shape É—insu, kalar kwayar idon da komai Badar tace mata wai Sexy Eyes kenan masu irin idanun sun iya soyayya kuma dasu suke cafke zukatan Yammata ta yarda da hakan dan bata iya haÉ—a ido da Ahmad se taji gabanta na faÉ—uwa duk sanda ta kalli idonsa ji take kamar ta sallama masa amma taurin kai irin nata ya sa har aka kawo i yanzu.
Saura kwana biyu su gama Exam ranar Ahmad ya kirata, kwana biyu ya bata space tunda tace masa Exam sukeyi idan ya kira bata ɗaga ba kota amsa ta bashi uzuri sosai ransa yake sosuwa shiyasa ya zaɓi daya barta ta gama exam ɗin idan har da gaske itace uzurin daya saka baya samun lokacinta. Tana kwance duk batajin daɗin dalilin yajin kiran wayar da Jay ta daka mata, tunda ya fahimci Exam suke kuma take wasa da karatunta tana biye masa shine yayi fushi. Ya gaya mata baya son mutumin da bashida focus, yana sonta amma baze taɓa haɗa lokacinta da Aikinsa ba me yasa ita zatayi wasa da Karatunta saboda shi?
Yace baze sake kiranta ba se sun gama kuma ta tura masa da Time table sannan idan ma ta kirashi baze amsa baz kullum da safe ze mata text haka da rana da dare amma babu phone call saboda magana dashi yasa takeji kamar wata mashashshara ce ta kamata duk ta rasa gane kanta. Tana ganin wayarta na ringing ganin Ahmad ne kamar ba zata amsa ba se kuma ta É—aga dalilin tunanin da tayi a ranta, tabbas Alhakin Ahmad ne tun ba'a je ko ina ba Allah ya jarabceta da Jay.
A sanyaye suka gaisa daga ita harshi babu wani me karsashi,
"Yaya Exam ɗin? Saura guda nawa ku gama?" Ya kauda shirun da sukayi bayan gaisuwa ta bashi amsa a taƙaice da
"Lafiya lau, saura biyu"
"Masha Allah, Allah ya bada sa'a" daga nan suka sakeyin wani shirun. Ya sani idan zasu kwana a haka ba lallai ta sake cewa komai, wlh daze iya da ya rabu da yarinyar nan dan duk wata hanya da mace zata nuna bata ra'ayin mutum ta nuna masa amma zuciyarsa ta kasa haƙura da ita. A kullum cikin Addu'a yake akan idan babu Alkhairi a tarayyarsu Allah ya cire masa ita daga zuciyarsa ya musanya masa da wadda ta fita amma abun kamar ana rura wuta ƙaruwa yakeyi.
Idan Jafar yana bashi labarin sabuwar soyayyar daya gamu da ita se yace shi kam bashida sa'a ne a soyayya da Alama. Bega Yarinyar da Jay yake so ba, amma yanda har Jay yake labarinta ya sani ba ƙaramin sonta yakeyi ba itama kuma tana riritashi, ze iya cewa be taɓa ganin Jafar a yanayi na soyayyar gaskiya irin wannan ba, yace masa auran yarinyar zeyi, Bahaushiyace yar Nigeria a Zaria suka haɗu. Yaƙi ko gaya masa sunanta dayace ya tura masa hotonta ya nunawa Fatima ko ta santa nan ya fitittike ya ringa zuba masa Tijara yace kuma baze tura ba se ya dawo zasuje ya ganta face to face ko sunanta baze gaya masa ba balle ya faɗawa Fatiman.
"Tana da Friends haÉ—aÉ—É—u irinta zan samo maka guda É—aya ka fita daga sabgar waccen Ajawon Fatiman da take wahalar da kai Yaya Ahmad" abinda Jay ya gaya masa.
Ahmad yaja numfashi, kusan minti bakwai daga shi har Fatima babu wanda yace wani abu. A sanyaye yace
"Fatima, idan wani laifi nayi miki kiyiwa girman Allah ki sanar mun na baki haƙuri, na gaji da azabatar da zuciyata da kikeyi kusan sati uku kenan kin hanani zaman lafiya nace zanzo kince Aa, idanna kiraki a waya koda yaushe cikin bani Excuse kike me nayi miki? Idan maganar kai gaisuwa da nayi ce kince Aa kuma na haƙura bayan wannan wane laifi nayi miki da kike hukuntani ta hanyar azabtar da zuciyata haka?"
A maimakon ta sassauta se maganganunsa suka sake ƙukar da ita, ta tsani Namiji da bashida ra'ayin kansa se abinda mace tace yayi wannan yana daga abinda bata so da Ahmad yanda yake mata wani lako lako kamar ita ce Namijin shine macen, to tun yanzu baya iya taɓuka komai daga abu ya haɗa m
Su ya fara kamar zeyi kuka yana lallaɓata idan sunyi auren kenan baze ringa tsawatar mata ba idan tayi masa laifi. Haɗuwarta da Jay tasa ta ƙara fahimtar banbancin Namiji da muna Maza, duk yanda yake nuna So ta yake riritata idan tayi masa abinda be gamshe shi ba murɗewa yakeyi ita ce zatayi ta lallashinsa da ban baki kafin ya sakko kamar dai yanzu daya yi fushi saboda bata maida hankali akan Exam ɗinta ba ta tabbata da Ahmad ne tsayawa zeyi yana lallashinta akan tayi kaza ko kartayi.
"Dan Allah Fatima ki tausaya mun. Na sani bakya sona Alfarma kike mun ina roƙon da ki daure kici gaba, ki dubi kalar jarabawar da nake ciki ta Sonki ki tausaya mun. Wlh Fatima da zan iya da tuni na cireki daga raina na rabu dake, koda baki taba buɗe baki kin gaya mun ba nida kaina nasan bakya sona kina kulani ne kawai saboda wulaƙnta ɗan Adam ba tarbiyyarki bace kuma na gode da hakan. Bazan gaji da roƙonki na akan ki bani dama, ki bude mun zuciyarki ko yaya ne in Allah ya yarda ba zakiyi nadamar tarayya dani ba" Ahmad ya sake faɗa a sanyaye.
Zuciyarta tayi rauni da jin abinda ya ke cewa, wato shi da kansa yasan bata sonsa amma ya gaza haƙura da ita tashi jarabawar Sonta ita kuma tata Son Jay Allah kenan.
Ajiyar zuciya ta sauke na shaking tace
"Nifa Ahmad ba haka bane ba, na gaya maka exam mukeyi ina buƙatar isashshen lokaci saboda nayi karatu shiyasa duk wani waya da wani chat na ajiye su amma mun kusa gamawa nan da Three days In sha Allah".
Yayi murmushi da jin abinda tace shima yace
"Ranar Thursday kenan zaku gama?" Ta yatsina fuska kamar yana kallonta tace eh, se ya sake cewa a sanyaye
"To yaushe zaki dawo Kano?"
"Paper safe ce, in har na gama komai kafin 12 ma zan taho a ranar in Allah ya yarda"
"To nazo na ɗakko ki?" Ya faɗa da sigar roƙo kamar wani me magana da ogarsa a gurin aiki, bata san sanda tsaki ya subuce mata ba tace
"Zan dawo da kaina, kasan Baffa ya hana ai ka ringa barin aikinka kana tahowa hidimata".
"Dan Allah Fatima karkice Aa kar kuma ki jingina maganar nan da Baffa sedai idan bakya sone kawai sena haƙura" ya sake faɗa gwanin ban haushi kuma ban tausayi kamar ze mata kuka, babu yanda ta iya haka ta yarda akan yazo ya ɗauketa, ita kanta zata ji daɗin hakan saboda hutun Session ne zata tafi da duka kayanta.
Ya ringa zabga mata godiya kamar wanda tayiwa kyauta daga ƙarshe sukayi sallama bayan ya sake roƙarta akan dan Allah ko sau ɗaya ne a rana idan ya kirani ta ringa amsawa gaisawa kaiwai zasuyi baze ja mata lokaci ba tace Toh.
"Allah sarki Ahmad, wlh yana bani tausayi na daÉ—e banga soyayya me zafi irin wadda yakeyi miki ba Afeeyah,dan Allah ki tausayawa mutumin nan yaci Albarkacin so wlh na tabbatar ba zaki yi nadamar auransa ba saboda yana sonki" Badar ta faÉ—a, Afeeyah ta hararaeta tace
"Kyaji da fuska biyunki anjima idan Jay ya kira waya jikinki na rawa zakiyita karaÉ—i kina bashi assurance na ze sameni ke ga campaign coordinator kuma se na gaya masa abinda kike cewa yanzu"
"Amma Thruth to be told Afeeya wlh Ahmad yafi sonki, ki gani fa shekara biyu yana binki kina jansa a ƙasa na tabbata Jay baze ɗauki haka ba Mace ta ringa wasa dashi kamar wani Toy, da yanzu ya daɗe da sallama ki" Badar ta sake faɗa. Afeeyah ta tashi zaune daga kwanciyar da take tace