Sashe 41
Matar Mutum Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Idan ba sauri kakeyi ba ka jira kawai mu tafi tare se mu kai Badar gida" ta faɗa masa, Badar ta ƙwalalo ido tana kallonta tace
"Ni nace miki yau zan tafi?"
"Nima ai ba yau nayi niyyar tafiyar ba saboda ya rigada yazo yasa dole zan tafi, ki tashi dan Allah karmu tsayar dashi" Afeeyah ta gaya mata. Dole Suka kashi kaya dan shirin da basu ƙarasa ba kaɗan ne, Badar nata mitar batayi sallama da Sweetynta Nurain ba kuma sunyi yau ze kaita yawo yanzu tasakata tafiya gida ita dai ta toshe kunne har suka kama hanya.
Badar da Ahmad keta hirar su ba tareda sun damu da Afeeyah ba dan daman sun saba muddin tafiya ztacehaɗa irin haka shiru takeyi tabarsu idan ma daga shi se itane sedai ya gaji da magana ya kunna Radio. A gidan Hajiya Ummu Yayar Hajiya Binta ya karɓi saƙon Laces ne ya siyawa Momy, a mota ya barsu ya shiga shi kaɗai da ze fito Hajiya Ummu da itama zata fita daman shi take jira ta biyo shi suka fito tare.
"Au daman tare kake sa baƙi shine ka barsu a Mota Ahmad? Rowar yar tawa kakeyi mun ko kuma baka riƙeni uwa ba shiyasa ka hanasu shigowa?" Hajiya Ummu ta faɗa. Ahmad ya duburburce, sam be kawo zata fito ba kuma shi be ƙiyi musu tayin shiga ba sedan baya so su ɓata lokaci dan yasan Antyn Ummun cewa zatayi se sun zauna sunci abinci dan shi kansa daƙyar ta barshi ya fito shaf shaf ɗin gashi kuma yanzu yayi complicating abun.
"Wlh Mama ba haka bane, ita wannan gida zamu sauketa Fatima kuma mu wuce Kano tare. Naga rana tayine bana so mu ɓata lokaci amma kiyi haƙuri bari su shigo". Yanda duk ya rikice yana mata bayani yasa tayi murmushi tace
"Karkayi kuka na yarda ba da niyya kayi ba". Ahmad yayi dariya, Badar da Fatima suka fito suka gaisheta ta amsa da fara'a tana tambayarsa wacece Surukar tata a cikinsu.
"Ki zaɓa Mama" ya faɗa yana shafa kai, tace
"Kowaccece a ciki Allah ya tabbatar da Alkhairi, saura ɗan uwanka ya kamata shima ya bar ruwan ido haka ya fitarda mata" ta koma cikin gida bayan tace su jira tana zuwa. Hijabai ta ɗebo ta basu sukayita godiya. Badar data karɓi ledar bayan sun shiga mota kafin Ahmad ya shiga tacewa Fatima
"Ke Hijaban Ummu-Maheer (07061838488) ne, kinga ledarta".
"Ai sun zaga duk inda bakya zato Kyau iya kyau, kasha gayunka da kuɗi ƙalilan a ringa zaton tafiyayye kika saka dole ki ganshi a gurin manyan mata irinsu Hajiyar nan".
Suna yan hirarrakin Ahmad ya dawo suka kama hanya. Tilas seda sukaci abinci sukayi Azahar kafin Momynsu Badar ta barsu suka tafi. A hanya Ahmad nata mata santin kirkin Maman Badar. "Ai Momy badaga nan ba gurin kirki, ita Badar ta gado" amsar data bashi kenan ta kame baki ya gaji da jan maganar shima ya kunna musu karatun Alƙur'ani ƙasa ƙasa suka cigaba da tafiya.
Lokaci lokaci yake kallonta yana ganin yanda ta mayar da hankali kan wayarta kome takeyi se Allah idan ta nisa kuma taja tsaki ita kaÉ—ai tayi tagumi ta kalli window. Yana so ya tambayeta me yake damunta amma ya kanne, so yake ya fara jurewa yana danne sonta ko ze samu ta fara dubansa da kimar da yake so. Bukar ya gaya masa ya bata iska, bawai barta ba tunda yana sonta amma ya koyi kamewa shima ya dena nuna mata cewar idan babu ita baze iya rayuwa ba.
Wayarta tayi ƙara, yana ganin yanda ta zabura ta duba in beyi ƙarya ba har sautin ajiyar zuciyar da tayi ya jiyo. Suka haɗa ido sanda ta saci kallonsa kafin ta ɗaga wayar. Zuciyarsa ta harba, daga yanayinta da yanda take magana a wayar dukda bajin me take cewa yakeyi ba tsabar yanda tayi ƙasa da murya ya gane da Namiji take maganar. Kansa ya ɗauki zafi, har wani sara masa yakeyi idanuwansa sukayi jajir lokaci ɗaya saboda wutar kishin data tashi ta fara ci balbal a zuciyarsa. Be san ta gama wayar ba seda yaga tana Ƙoƙarin saka cajin wayar ta ajikin cajar motar. Murya a kausashe da irin sautin da bata taɓa jinsa dashi ba ya kira sunanta kafinyace
"Ni ba shashashan Namiji bane da kina zaune tareda ni wani ze kiraki a waya ki É—auka, this should be the last time da zaki kwatanta wani abu kamar haka. Wlh kika sake sena fasa wayar idan yaso naga da abinda zaki cimun fuska kiyi magana da wani Namiji".
Tsabar yanda maganarsa ta shigeta har karkarwa jikinta ya ɗauka, tunani takeyi daman Ahmad ya iya faɗa irin haka? Yanda ya juye mata lokaci ɗaya ya firgitata ga speed daya ƙarawa motar yanda kasan zasu tashi sama.
"Kayi haƙuri" ta faɗa bakinta na rawa. Har suka isa Kano kuma be sake ce mata komai ba, a bakin layinsu da suka isa ya faka be kulata ba ya fita ya samu yara ya buɗe booth suka kwashe mata kayanta. Be bata fuskar da zata sake masa wata magana ba, a wajen motar ma ya tsaya har seda ta sauka kafin yaja yayi tafiyarsa ya barta da bin bayansa da kallo.
A sanyaye ta isa gida kafin ta shiga dai tayi ƙoƙarin daidaita nutsuwarta saboda gudun tambayar meya sameta. Ta tarar da Anty Sauda da yaranta, ganinsu yasa ta sake sakin ranta musamman kuma da sahibul Ƙalbinta ya kirata ya mata fatan sa'a akan Jarabawar da suka gama yace zasuyi magana idan ta isa gida. Wannan birkicewar ta Ahmad ce ta jirkitata amma tana shiga gida ta manta da babinsa ta shiga sabogogi sedai lokaci lokaci yakan faɗo mata, yanda ya fututtuke se taji kamar Jay yana sababi, daman ance masu haƙuri basu iya fushi ba yau kuwa gashi ta tabbatar.
Ahmad kuwa seda yayi dagaske kafin ya danne abinda ya ringa cin zuciyarsa, yana da kishi matuƙa musamman akan abinda yake so kamar Fatima. Koda yake binta yana lallaɓata dan yasan kawai ra'ayinsa ne batayi bawai wani saurayi ne da ita daban da yasa take ƙinsa saboda shi ba. Yasan bata double dating, shiyasa ya nace yake ta roƙon Allah yana kuma ƙara cusa kansa gurinta amma yanzu ya fahinci ta samu wani saurayin da take ra'ayi shiyasa harta iya ci masa fuska ta ringa waya dashi a gabansa shi ga sakarai wato bazeji komai a ransa ba.
Seda aka kwana biyu da ɗakkota da yayi be sake kiranta ba, dan ya yanke dole ya koyawa zuciyarsa haƙuri da ita tunda har ya fahimci da wani bayan shi yanzu komai yana iya faruwa kenan. Da safe ranar Asabar kwana biyu kenan da dawowar tata yana kwance a ɗakinsa se gashi ta kirashi. Ya ringa kallon wayar kamar wanda yayi loosing memory saboda ya kasa yarda Fatima ce take kiransa da karan kanta yau. Rejecting yayi kafin yabi bayan kiran duk da zuciyarsa nace masa karya amsa ya bar wayar tayi ringing ta gama harta sake kira dan ya tabbatar da gaske shi take kira ba tuntuɓen number tayi ba.
"Ina kwana?" Ta faÉ—a a sanyaye bayan da yayi mata sallama ta amsa. Ya amsa gaisuwar yana jin tamkar ya taka rawar murna, dahgaske kenan idan mutum yaja aji za'a mutuntashi tunda gashi fushin kwana biyu ya juyo masa da hankalin Fatima.
"Kayi haƙuri akan abinda ya faru ranar nan banyi da wata niyya ba" ta sake faɗa a sanyaye. Daɗi ya sake kamashi, har tasan ta kirashi kenan ta bashi haƙuri ai kuwa akwai haske a cikin tafiyar. Ya wani mula yace
"Babu komai kawai dai na gaya miki idan kika sake sena fasa wayar tunda bazan iya fasa miki baki ba"
"Ai dai nace kayi haƙuri" ta sake nanatawa yace
"Na haƙura na kuma yafe miki Alhakina da kika ɗauka kika sa nayi fushi dake".
"Uhm" kawai tace, suka ɗan taɓa hira kafin sukayi sallama bayan yace mata zeje da yamma tace tana gidan Anty Sauda ya sameta a can dan kwana zatayi.
"Toh ko kefa? Nifa harga Allah zancen wani Ɗan Ball be kwantamun a rai ba. Haka kawai zaki kwasarwa kanki abinda ze saka miki ciwon rai idan ya aureki ɗin ma kenan. A matsayinki nawa Afeeyah zakice zaki auri world class Celebrity? Ai ɗagen yayi yawa, irin waɗannan ai ba kowacce mace ba, kuma duk ma ba wannan ba na tabbatar wlh fuskarki ce kawai ta ruɗeshi, babu tabbacin idan yasan wacece ke ya yarda ya aureki a haka gara miki Ahmad ɗin. Mutumin nan ga Hankali, nutsuwa, mutunchi, karamchi uwa uba yana matuƙar sonki kuma ya sanki ciki da bai yasan Mahaifanki a hakan kuma yace yaji ya gani yana sonki ze aureki na rasa wace masifa ce tasa bakya son Bawan Allahn nan Afeeyah wlh in guje miki kiyi nadanar da ba zata amfana miki komai ba a gaba" Anty Sauda wadda ita ta tursasata kiran Ahmad bayan data shaida mata abinda ya faru tsakaninsu ta faɗa.
"Ni nace miki yau zan tafi?"
"Nima ai ba yau nayi niyyar tafiyar ba saboda ya rigada yazo yasa dole zan tafi, ki tashi dan Allah karmu tsayar dashi" Afeeyah ta gaya mata. Dole Suka kashi kaya dan shirin da basu ƙarasa ba kaɗan ne, Badar nata mitar batayi sallama da Sweetynta Nurain ba kuma sunyi yau ze kaita yawo yanzu tasakata tafiya gida ita dai ta toshe kunne har suka kama hanya.
Badar da Ahmad keta hirar su ba tareda sun damu da Afeeyah ba dan daman sun saba muddin tafiya ztacehaɗa irin haka shiru takeyi tabarsu idan ma daga shi se itane sedai ya gaji da magana ya kunna Radio. A gidan Hajiya Ummu Yayar Hajiya Binta ya karɓi saƙon Laces ne ya siyawa Momy, a mota ya barsu ya shiga shi kaɗai da ze fito Hajiya Ummu da itama zata fita daman shi take jira ta biyo shi suka fito tare.
"Au daman tare kake sa baƙi shine ka barsu a Mota Ahmad? Rowar yar tawa kakeyi mun ko kuma baka riƙeni uwa ba shiyasa ka hanasu shigowa?" Hajiya Ummu ta faɗa. Ahmad ya duburburce, sam be kawo zata fito ba kuma shi be ƙiyi musu tayin shiga ba sedan baya so su ɓata lokaci dan yasan Antyn Ummun cewa zatayi se sun zauna sunci abinci dan shi kansa daƙyar ta barshi ya fito shaf shaf ɗin gashi kuma yanzu yayi complicating abun.
"Wlh Mama ba haka bane, ita wannan gida zamu sauketa Fatima kuma mu wuce Kano tare. Naga rana tayine bana so mu ɓata lokaci amma kiyi haƙuri bari su shigo". Yanda duk ya rikice yana mata bayani yasa tayi murmushi tace
"Karkayi kuka na yarda ba da niyya kayi ba". Ahmad yayi dariya, Badar da Fatima suka fito suka gaisheta ta amsa da fara'a tana tambayarsa wacece Surukar tata a cikinsu.
"Ki zaɓa Mama" ya faɗa yana shafa kai, tace
"Kowaccece a ciki Allah ya tabbatar da Alkhairi, saura ɗan uwanka ya kamata shima ya bar ruwan ido haka ya fitarda mata" ta koma cikin gida bayan tace su jira tana zuwa. Hijabai ta ɗebo ta basu sukayita godiya. Badar data karɓi ledar bayan sun shiga mota kafin Ahmad ya shiga tacewa Fatima
"Ke Hijaban Ummu-Maheer (07061838488) ne, kinga ledarta".
"Ai sun zaga duk inda bakya zato Kyau iya kyau, kasha gayunka da kuɗi ƙalilan a ringa zaton tafiyayye kika saka dole ki ganshi a gurin manyan mata irinsu Hajiyar nan".
Suna yan hirarrakin Ahmad ya dawo suka kama hanya. Tilas seda sukaci abinci sukayi Azahar kafin Momynsu Badar ta barsu suka tafi. A hanya Ahmad nata mata santin kirkin Maman Badar. "Ai Momy badaga nan ba gurin kirki, ita Badar ta gado" amsar data bashi kenan ta kame baki ya gaji da jan maganar shima ya kunna musu karatun Alƙur'ani ƙasa ƙasa suka cigaba da tafiya.
Lokaci lokaci yake kallonta yana ganin yanda ta mayar da hankali kan wayarta kome takeyi se Allah idan ta nisa kuma taja tsaki ita kaÉ—ai tayi tagumi ta kalli window. Yana so ya tambayeta me yake damunta amma ya kanne, so yake ya fara jurewa yana danne sonta ko ze samu ta fara dubansa da kimar da yake so. Bukar ya gaya masa ya bata iska, bawai barta ba tunda yana sonta amma ya koyi kamewa shima ya dena nuna mata cewar idan babu ita baze iya rayuwa ba.
Wayarta tayi ƙara, yana ganin yanda ta zabura ta duba in beyi ƙarya ba har sautin ajiyar zuciyar da tayi ya jiyo. Suka haɗa ido sanda ta saci kallonsa kafin ta ɗaga wayar. Zuciyarsa ta harba, daga yanayinta da yanda take magana a wayar dukda bajin me take cewa yakeyi ba tsabar yanda tayi ƙasa da murya ya gane da Namiji take maganar. Kansa ya ɗauki zafi, har wani sara masa yakeyi idanuwansa sukayi jajir lokaci ɗaya saboda wutar kishin data tashi ta fara ci balbal a zuciyarsa. Be san ta gama wayar ba seda yaga tana Ƙoƙarin saka cajin wayar ta ajikin cajar motar. Murya a kausashe da irin sautin da bata taɓa jinsa dashi ba ya kira sunanta kafinyace
"Ni ba shashashan Namiji bane da kina zaune tareda ni wani ze kiraki a waya ki É—auka, this should be the last time da zaki kwatanta wani abu kamar haka. Wlh kika sake sena fasa wayar idan yaso naga da abinda zaki cimun fuska kiyi magana da wani Namiji".
Tsabar yanda maganarsa ta shigeta har karkarwa jikinta ya ɗauka, tunani takeyi daman Ahmad ya iya faɗa irin haka? Yanda ya juye mata lokaci ɗaya ya firgitata ga speed daya ƙarawa motar yanda kasan zasu tashi sama.
"Kayi haƙuri" ta faɗa bakinta na rawa. Har suka isa Kano kuma be sake ce mata komai ba, a bakin layinsu da suka isa ya faka be kulata ba ya fita ya samu yara ya buɗe booth suka kwashe mata kayanta. Be bata fuskar da zata sake masa wata magana ba, a wajen motar ma ya tsaya har seda ta sauka kafin yaja yayi tafiyarsa ya barta da bin bayansa da kallo.
A sanyaye ta isa gida kafin ta shiga dai tayi ƙoƙarin daidaita nutsuwarta saboda gudun tambayar meya sameta. Ta tarar da Anty Sauda da yaranta, ganinsu yasa ta sake sakin ranta musamman kuma da sahibul Ƙalbinta ya kirata ya mata fatan sa'a akan Jarabawar da suka gama yace zasuyi magana idan ta isa gida. Wannan birkicewar ta Ahmad ce ta jirkitata amma tana shiga gida ta manta da babinsa ta shiga sabogogi sedai lokaci lokaci yakan faɗo mata, yanda ya fututtuke se taji kamar Jay yana sababi, daman ance masu haƙuri basu iya fushi ba yau kuwa gashi ta tabbatar.
Ahmad kuwa seda yayi dagaske kafin ya danne abinda ya ringa cin zuciyarsa, yana da kishi matuƙa musamman akan abinda yake so kamar Fatima. Koda yake binta yana lallaɓata dan yasan kawai ra'ayinsa ne batayi bawai wani saurayi ne da ita daban da yasa take ƙinsa saboda shi ba. Yasan bata double dating, shiyasa ya nace yake ta roƙon Allah yana kuma ƙara cusa kansa gurinta amma yanzu ya fahinci ta samu wani saurayin da take ra'ayi shiyasa harta iya ci masa fuska ta ringa waya dashi a gabansa shi ga sakarai wato bazeji komai a ransa ba.
Seda aka kwana biyu da ɗakkota da yayi be sake kiranta ba, dan ya yanke dole ya koyawa zuciyarsa haƙuri da ita tunda har ya fahimci da wani bayan shi yanzu komai yana iya faruwa kenan. Da safe ranar Asabar kwana biyu kenan da dawowar tata yana kwance a ɗakinsa se gashi ta kirashi. Ya ringa kallon wayar kamar wanda yayi loosing memory saboda ya kasa yarda Fatima ce take kiransa da karan kanta yau. Rejecting yayi kafin yabi bayan kiran duk da zuciyarsa nace masa karya amsa ya bar wayar tayi ringing ta gama harta sake kira dan ya tabbatar da gaske shi take kira ba tuntuɓen number tayi ba.
"Ina kwana?" Ta faÉ—a a sanyaye bayan da yayi mata sallama ta amsa. Ya amsa gaisuwar yana jin tamkar ya taka rawar murna, dahgaske kenan idan mutum yaja aji za'a mutuntashi tunda gashi fushin kwana biyu ya juyo masa da hankalin Fatima.
"Kayi haƙuri akan abinda ya faru ranar nan banyi da wata niyya ba" ta sake faɗa a sanyaye. Daɗi ya sake kamashi, har tasan ta kirashi kenan ta bashi haƙuri ai kuwa akwai haske a cikin tafiyar. Ya wani mula yace
"Babu komai kawai dai na gaya miki idan kika sake sena fasa wayar tunda bazan iya fasa miki baki ba"
"Ai dai nace kayi haƙuri" ta sake nanatawa yace
"Na haƙura na kuma yafe miki Alhakina da kika ɗauka kika sa nayi fushi dake".
"Uhm" kawai tace, suka ɗan taɓa hira kafin sukayi sallama bayan yace mata zeje da yamma tace tana gidan Anty Sauda ya sameta a can dan kwana zatayi.
"Toh ko kefa? Nifa harga Allah zancen wani Ɗan Ball be kwantamun a rai ba. Haka kawai zaki kwasarwa kanki abinda ze saka miki ciwon rai idan ya aureki ɗin ma kenan. A matsayinki nawa Afeeyah zakice zaki auri world class Celebrity? Ai ɗagen yayi yawa, irin waɗannan ai ba kowacce mace ba, kuma duk ma ba wannan ba na tabbatar wlh fuskarki ce kawai ta ruɗeshi, babu tabbacin idan yasan wacece ke ya yarda ya aureki a haka gara miki Ahmad ɗin. Mutumin nan ga Hankali, nutsuwa, mutunchi, karamchi uwa uba yana matuƙar sonki kuma ya sanki ciki da bai yasan Mahaifanki a hakan kuma yace yaji ya gani yana sonki ze aureki na rasa wace masifa ce tasa bakya son Bawan Allahn nan Afeeyah wlh in guje miki kiyi nadanar da ba zata amfana miki komai ba a gaba" Anty Sauda wadda ita ta tursasata kiran Ahmad bayan data shaida mata abinda ya faru tsakaninsu ta faɗa.