Sashe 65
Matar Makaho Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri ta d'ago kanta jin yanda yayi maganar a matukar sanyaye, kamar wanda zai nemi Alfarma itafa halaliyar sace,amma ga yanda yake had'ata da Allah, yayi matukar kokari, yanzun ana neman kusan wata uku da auren su, koh ma fiye da haka, ba tare da ya taba tilasta ta akan hakkinsa, kullum ya bukace hakan, zata saka masa kuka, koma hakan koh baya so yake kyaleta. Jin batace kome ba yasa sa lalubar fuskar ta,In baki Ra'ayi kiyi hakuri sumayya,na hakura. Da sauri ta kamo nasa fuskar hawaye na cika mata ido, "yayan khadija hakkin kane fa?kaima da kanka ka fad'a, kaga kenan ni bani da damar hana ka, tunda naka ne, duk abinda zaka bukata a gareni mallakin kane, na amince kayi duk abinda kake so dani, ta karasa maganar da fashewa da kuka. Jin ta fara kuka yasa muhammad, da sauri yace, sumayya kiyi hakuri nama hakura, shikenan tashi kisa kayanki mu kwanta. "Ba kuka nake ba" Hannu yasa ya shafo kumatun ta, toh me kike, kuma menene a fuskar taki? "Kayi hakuri" Fuskar sa ya had'a da tata fuskar, baki min kome ba sumayya. "Toh insa kaya koh haka xamu kwanta" ? Shikam ba karamin dariya sumayya ta basa ba harya kasa hakuri, saida ya dara, hhh menene haka kuma sumayya? "Toh ba tambaya nayi ba, koh tambaya laifine"? Ah ah ba laifi bane, yace yana d'aura fuskarsa a kafadar ta, yana goga mata gemunsa. A hankali sumayya ta manne masa gam a jiki, hannu tasa ta kama gashin kansa, jin kamar zai zautar da ita, jin bakinsa akan wuyan ta. Ahhhh, yace yana kamota, d'agota yayi gabaki d'ayan ta, yana lalube harya hau gadon, kwantar da ita yayi ya hau kanta, bakinsa ya jona cikin nata, sosai yake tsotsar bakin ta, jikinsa sai rawa yake. Sosai sumayya ke tare da farga ba, don yanayin muhammad kawai yau zai tabbatar maka, da gaske yake son Angon cewa. Washhh Ashhhhh sumayya tace, lokacin da taji muhammad ya yaye mata towel in jikinta, shima tuni ya watsar da nasa daga ita harshe babu sutura a jikinsu....... Zafafan Romance Al'ameen yake wa sumayya, da zafi zafi don A lokacin bazaka taba tunanin koh baya gani ba, aikin dake gabansa kawai yake. Sumayya dake kwance rumtsa ido tayi, jin Al'ameen na ware mata kafa, bakinsa d'auke da Addu'an saduwa da iyali Kara ta kwala da karfi, tare da ware ido, jin wani Al'amari mai girma daya ratso rayuwarta, a karon farko hannunta dake free, ta d'aga a zabure ta cakumo gashin kansa. Da karfi ya fizgo Hannunta, daga gashinsa ware hannun yayi ya danne da jikin katifa, sosai ya kara bada himma akan abinda yake, bai taba d'aukar zaiji wani d'adi ba tunda Abbajon sa ya barsu, wahalar rayuwa bai barsa ya tuna akwai wani dadin da zai iyya d'and'ana wa, maka mancin wannan dadin ba, sai gashi yau sumayya ke shayar dashi. Sumayya kam gumi ta had'a sosai, duk da an fara yayyafi, Amma daga ita har muhammad zufane ya jikasu, sosai sumayya ke kuka tana goga kanta da jikin pillow, ba zafin da Al'ameen ke d'and'ana mata bane yafi ratsata, wani irin sarawa taji kanta nayi kamar wance ake fisgar gashin kanta da karfi, haka takeji a kanta kuka tasa, don abin ya hade mata biyu, ga azaban da Al'ameen ke gana mata sosai, kanta ke bugawa ji take kamar kwakwalwarta zai fita, sai salati take tana murza kan da filo. Ta bangaren Al'ameen kam, yau ba'aji ba'a gani am amsa sunan MAKAHO yau, don koh kukan sumayya baji yake ba, hankali..sa na gefe, damuwar sa kawai yaji abinda yake gabansa. Sumayya jin wasu irin bugawa da kanta keyi akai akai jijiyoyin kanta takeji kamar zasu tsinke, koh gani bata iyyawa yanzun sosai, duk da a duhu suke Amma duhun da take kallo yanzun yafi karfin duhun d'akin. Sosai bakin ta ya bushe, sai shakuwa take, tana kiran ruwa da muryarta da baya fita sosai. Amma ina muhammad baisan tanayi ba abinda yasa agaba yake fama. Jan numfashi sumayya tayi da karfi jin wani irin wahalallen shakuwa, ya gudu da numfashin ta duka, sakewa tayi jagab ta koma jikin filo, Muhammad bai farga da halinda sumayya take ciki ba sai da ya gama samun nutsuwa, A hankali ya zare jikinsa a nata, aiji yayi kamar an watsa masa Allurai a idanun sa, soki yakeji a cikin kwayan idonsa, sunfi d'ari rumtsa idon yayi da karfi, yana kiran sunan Allah jin wani irin barkono da soki na cakansa, tunda yake bai tabajin azaba irin wannan ba, kansa ya had'a da jikin gado da karfi ya buga ji kake gauuuuu ...........ya sulale kan katifar baya motse. Har Asuba muhammad da sumayya suna sume, basu farfado ba, babu wanda yasan halinda suke ciki, sai mahallincin mu, A Hankali sumayya ta fara motse, a hankali take kokarin bude idanunta, sai kuma ta maida su ta rufe da sauri, jin wani irin nauyi daya mata, sai da tafi minutes 10 kafun ta sake bude idon, a hankali harta budesu duka, ware idon tayi tana kallo dishi dishi har idanunta suka sauka akan muhammad, dake yashe a gefe ga goshin sa a fashe. Cikin matukar razana ganin sa kamar wani matan ce, haftowa tayi da kuzari zata mike, kara ta sake tana Ambatan sunan Allah, ta koma ta kwanta jin wani irin rad'ad'i dake ratsata, ta kasa A hankali ta mike zaune, tana cije lebenta, ta fara rarrafawa zuwa garesa, matsowa tayi sosai ta tattabasa jin baya motse, yasata sake kara"innalillahi wa'inna'illahi raji'um nashiga uku, don Allah muhammad karka tafi ka barni wayyo nashiga uku, wayyo mijina na bonu,ganin kamar suma yayi, sai kuma ta rarrafa da sauri taja blanket in ta rufe masa jiki, da rarrafe ta sauka akan gadon, towel inta dake yashe a kasa ta d'auka ta d'aura. Firij ta wuce ta d'auki ruwa, haka ta rarrafa ta iso bakin gadon ta saitin da yake, hannu tasa ta bude bakin goran, ta tsiyaye ta wasa masa a fuska, Amma ina shuru muhammad bai tashi ba, kuka ta sake tana bulbula masa ruwan sanyin a fuska, Amma koh motse baiyi ba,"wayyo muhammad wayyo mijina, na shiga uku Allah ka taimake ni" A matukar gigice ta saka kunnen ta a kan kirjinsa, jin zuciyarsa na bugawa, yasa hankalin ta kwanciya don ta gane suma yayi. Tunawa tayi da number maimuna kanwar Ammar, a wayan ta koh ta kirata ne? ta had'ata da Ammar koh Zai taimaka mata mijinta ya tashi tunda itama, tana bukatn taimako, gashi bata san wazata kira ya tallafa musu ba. Da rarrafe ta isa kusa da wayan d'auka tayi jikinta sai bari yake, ta kira maimuna tanajin ta d'aga tace"Assalamu Alaikum" Wa'alaikumu salam Aunty sumayya ina kwana? "Lafiya maimuna don Allah Ammar na gida"? Lafiya kam aunty sumayya, naji muryan ki a dishe? " nace miki Ammar na gida"? Ah ah wallahi yau yabar gari da asuba lfy? Kashe wayar in sumayya tayi, don bata da lokacin maimuna. Da sauri wani tunanin yazo kanta, ta rarrafa ta isa wajen kayan sa, budewa tayi tana ciro masa kaya, in yaso sai ta saka masa, ta fita ta kira keke su tafi asibiti, duk da ba lafiya bane da ita, koh da rarrafe zata fita ta taimake rayuwar mijinta. Kayan sa ta bude ta, dauko jallabiya tayi ta aje, tasa hannu zata d'auki gajeren wandon sa, taji hannunta ya taba wani abu mai karfi kamar gidan agogo, hannu tasa ta zaro abin, haka kawai taji hankalin ta bai kwanta da wannan karamin akwatin ba, hannu tasa ta bude. Da sauri ta rufe Idanun ta ganin wani irin haske daya kashe mata ido,A hankali ta sake bude ido ta kurawa sarkan ido, yayi haske yasa ke mutuwa farine sosai, mai kyau sai zanen zaki dake tsakiyar gaban sarka, sosai sarkan ke sheki yana komawa normal. Jiki na bari ta rike sarkan, indai bata manta ma Al'ameen yace baban shi ya basa sarka, koh dai wannan ne sarkan? menene dalilinsa na cirewa? a wuyansa, rarrafe tayi ta isa garesa, sarkan ta d'auka ta d'aura masa a wuya. Ai sarkan nan na shiga wuyan Al'ameen, ya wani irin haske sosai sai kuma ya koma normal bai sake hasken ba. Da rarrafe sumayya ta fita a kofar dikin"subhanallah"tace ganin har rana ya fitoh don lokacin ana neman, kusan karfe 8:00 na safe koh sallan asuba basuyi ba,da rarrafe ta shiga kitchen kittle ta jona a soket, tana zaune a wajen ya tafasa juyewa tayi a boket, ta sake saka wani saida ta juye kittle uku,sannan ta fara kokarin mikewa,don d'aukar boket in ta juye a band'aki, Amma ta kasa, kuka kawai ta sake, ta koma ta zauna. Muhammad kam tunda sumayya ta fita a d'akin ya farka, sosai idanunsa ke masa zoge kamar an kwakule masa su,tun d'azun yana kwance don duk jikinsa a sake yake. Da sauri ya mike zaune jin kukan sumayya ta window, sai yanzun tunanin abinda ya faru ya fado masa,take yaji tsikar jikinsa ya miki, hasbinallahu wani'imal wakin, yace yana mikewa zaune, dafa kansa yayi da karfi jin wani irin rad'adi a inda ya buge, a haka dai ya lallaba ya mike zaune, jin baida sutura a jiki yasa sa fara laluben gadon, ji kawai yayi hannun sa ya taba wani abu damshe damshe, ga karnin jini. Da sauri ya mike, sauka yayi ya d'auki wando a cikin kayansa ya saka, yana dafe da kansa har lokacin idanunsa a rufe suke. Sumayya!!!sumayya!! Menene?yace yana karaso wa kusa da ita. Ai barin kukan sumayya tayi, ta zare ido ganin Al'ameen akan kafafunsa, hannu tasa ta kamo nasa hannun"na kasa tashine, ga rana yayi bamuyi wanka ba, gashi ina son kai ruwa band'aki na kasa, gashi ka suma hankali na ya tashi"tana maganar tana kuka. Rungumar ta muhammad yai da karfin gaske, A hankali ya bude baki daker, kamar yanajin tsoron magana, sumayya ina sonki, sumayya ina tsananin kaunar ki, bazan taba mantawa da daren jiya a rayuwa ta ba, har abada kece cikon farin cikina, ina fatan har in koma ga Allah, karna miki butulci matata. Kara rungumar sa tayi sosai, taji wani sanyi a ranta da tausayin mijinta"nima babu abinda zance maka sai dai na mana fatan gamawa da duniya