Sashe 80
Labarinsu Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Can sai ga wani kyakkyawan yaro dake tsantsar kama da Kuliya ya sauƙo daga kan stairs hannunsa riƙe da Ipad.
Rabi ta bishi da kallo tana jinjina kai, wato yana jinta, amsawar ce ba zai iya ba, ita har mamakin lamarin Junior take, ko da ɗiso babu abun da ya baro a hallayar Kuliya.
“Papi na faɗi!”
Cewar Junior ɗin yana miƙawa Kuliya Ipad ɗin hannunsa.
Kuliya ya karɓa ya na kallon yaron.
Aliyu Zaid Aliyu kenan, a.k.a Junior, a.k.a Kuliya, a.k.a AZA, duka sunansa ne, ɗan auta a wurin kawunsa, kakarsa, mamansa, dadynsa, papinsa da kuma Nininsa.
Zaid ya ja kujera ya zauna yana faɗin.
“Wata ran sai na fasa ipad ɗin nan, in yabso na ga ta tsiyar...
In ba wulaƙanci irin na Junior ba, ya za ayi mamansa ta dawo daga training, ta kirashi amma ya wuce wurin Aliyu yana faɗin wai ya faɗi a game?”
Kuliya ya kalli Zaid yana zaunar da Junior a kan cinyarsa.
“Ka fasa, ni kuma sai na sai masa sabuwa, ina ruwanka da sha'aninmu?, mu babu ruwanmu da kowa ba ehe”
“Junior Mama fa?”
Rabi ta faɗi tana kallonsa.
Juyowa ya yi ya kalleta da gray eyes ɗinsa da shi kaɗai ne abu ɗaya da ya gado a wurin Zaid, amma hatta da buɗar idonsa irin ta Kuliya ce.
Sai kuma ya sauƙo daga kan cinyar Kuliya, ya tako zuwa wurin Rabi, ya ɗan mata wani gutun murmushi yana rungume ƙafafunta.
“Tafi ka bani wuri ba na so”
“Haka fa ni ma suka haɗe mun kai shi da Papi last week, wai dan suna kallon Film ɗin 'Tara Dunken' na zo na sauya, shi kenan suka dena min magan, sai jiya suka kulani”
Cewar Mishal tana aje cup ɗin hannunta.
“Ai ke na sati ɗaya suka miki ma, ni da suka fi sati biyu ba sa kulani fa in ce me?”
Cewar Anna cikin taɓe baki.
“Sorry Mama”
Cewar Junior kamar wanda aka yiwa dole.
Rabi ta dunguri kansa tana faɗin.
“Ka dena wannan miskilancin naka, idan ka ce irin halin Papi za ka ɗauko wahala za ka sha, don ma de shi Papi an yi nasarar samun Nini ta seta masa hanya, kai ko sai de ka ci jibga, don dukanka zan fara...”
Shi dai bai ce mata komai ba, sai ƙasan kimonohnta da ya riƙe.
“Nini?
Ashe ke kika seta ni?”
Kuliya ya tambaya yana kallon Mishal, ita ko tai masa banza, don ta san idan ta biyashi yanzu sai su zo suna cece ku ce, ita kuwa yanzu a duniyar Allahn nan magana ita ce abun da ke mata wuya, ba ta son yawan magana.
“Sai ku zo mu fara cin abin cin”
Cewar Anna.
“Bari na je na yi wanka tukunna”
Rabi ta faɗi tana ƙwace ƙasan kimonohnta daga hannun Junior.
Kafin ta haye sama.
Bayan ɗan wani lokaci Zaid ma ya miƙe ya bita.
Kuliya ya ci gaba da tsokanar Mishal, amma ko ci kanka ba ta ce masa ba, har sai da Anna ta masa magana kafin ya shafa mata lafiya.
“Ammatan Raj”
Zaid ya kira sunanta, yayin da take tsaye a jikin mirror tana shafa mai, juyowa ta yi ta kalleshi, shi ma kuma kallon nata yake, yayin da yake tsaye a bayanta.
“Kai wai baka san ka girma ba ne?”
Ta tambaya tana juyawa.
“Girman me?, ɗa ɗaya ne fa da mu kawai, ki bari sai mun tara kamar yara goma haka, sai ki ce na girma, amma ɗa ɗaya ai ya yi kaɗan ya sa na ga tsufana”
Rabi ta yi murmushi tana shafa mai a wuyanta.
“Saura kwana nawa ku tafi ne?”
Ya tambaya yana zuge mata zip ɗin rigarta da bata zuge ba.
Rabi na kallonsa ta cin madubin gabanta ta furta.
“One week”
“Mun gode Allah, dan nan da kwana uku visar mu na iya fitowa”
Sai ta gyaɗa masa kai tana juyowa.
“Mu je ko?”
Ya girgiza mata kai yana kama waist ɗinta.
Rabi ta ture shi tana faɗin.
“Su Anna na ƙasa suna jiranmu fa”
Ya ƙara kamota yana faɗin.
”To ina ruwana...”
“Dady!
Mama!”
Muryar Junior ta kira daga wajen ɗakin.
Rabi ta ƙara tureshi tana nufar ƙofar da sauri, sai ta ga Junior ɗin tsaye a waje yana kallonta.
“Me ya faru?”
“Anna tace wai ku yi sauri”
Rabi ta juyo ta kalli Zaid tana watsa masa hararar wasa, kafin ta juyo ta tsugunna ta ɗauki Junior ta sauƙa ƙasa, Zaid ya bi bayansu da kalli yana murmushi, kafin shi ma ya bi bayan nasu ya sauƙa aka fara cin abincin da shi.
Labarin rayuwar sabon gidan da suka gina cike da so ƙaunar juna da farin ciki kenan.
°°°°°°Alhamdullullah°°°°°°
••••••END••••••
-Assalamualaikum-
Barkan mu da wannan lokaci, ina so na yi amfani da wannan damar, wurin nuna muku irin godiyata gareku, kan so da ƙaunar da kuka nuna min, a har kullum ina ganin kamar ‘Na gode' ta yi kaɗan wurin nuna muku jin daɗi na game da yanda kuke support ɗina, my people i can't thank you enough.
Allah ya bar zumunci.
Sannan ina so na yi jan hankali gareku, game da darasin dake cikin wannan littafi.
Idan kuka tsaya kuka yi nazari, za ku ga cewar wannan littafin na ƙunshe da illollin fyaɗe, da kuma yanda rayuwar 'ya mace kan shiga garari yayin da iyayenta suka koreta daga gida, bacin da ƙaddara fyaɗe ta faɗa kanta.
Kun sani, kuma ni ma na sani, fyaɗe ita ce babbar annobar da ta damu yankin mu na arewa gaba ɗaya, shi ya sa nake so, mu tashe tsaye ni da ku, mu haɗa ƙarfi da ƙarfe, wurin ganin mun kawo ƙarshen wannan annoba, domin fyaɗe masifa ne, kuma bala'ine.
Ina kira ga duk wani wanda ya san Allah ya wadata shi da wata baiwa, da ya yi anfani da wannan baiwar tasa wurin ganin mun kawo ƙarshen fyaɗe a arewacin nigeria, idan zai iyu, a gaba ɗayan Nigeria ma.
Ni tawa baiwar ta rubutu ce, shi ya sa na yi amfani da shi, wurin ganin na yaƙi wannan annoba da ta damu sauran 'yan uwana mata.
Jama'a mu ƙyamaci fyaɗe.
*Say No to Rape❌*
#Labarinsu
#SalmaAhmadIsah
#TaurariWriters
Best regards
SALMA AHMAD ISAH
2024...
Rabi ta bishi da kallo tana jinjina kai, wato yana jinta, amsawar ce ba zai iya ba, ita har mamakin lamarin Junior take, ko da ɗiso babu abun da ya baro a hallayar Kuliya.
“Papi na faɗi!”
Cewar Junior ɗin yana miƙawa Kuliya Ipad ɗin hannunsa.
Kuliya ya karɓa ya na kallon yaron.
Aliyu Zaid Aliyu kenan, a.k.a Junior, a.k.a Kuliya, a.k.a AZA, duka sunansa ne, ɗan auta a wurin kawunsa, kakarsa, mamansa, dadynsa, papinsa da kuma Nininsa.
Zaid ya ja kujera ya zauna yana faɗin.
“Wata ran sai na fasa ipad ɗin nan, in yabso na ga ta tsiyar...
In ba wulaƙanci irin na Junior ba, ya za ayi mamansa ta dawo daga training, ta kirashi amma ya wuce wurin Aliyu yana faɗin wai ya faɗi a game?”
Kuliya ya kalli Zaid yana zaunar da Junior a kan cinyarsa.
“Ka fasa, ni kuma sai na sai masa sabuwa, ina ruwanka da sha'aninmu?, mu babu ruwanmu da kowa ba ehe”
“Junior Mama fa?”
Rabi ta faɗi tana kallonsa.
Juyowa ya yi ya kalleta da gray eyes ɗinsa da shi kaɗai ne abu ɗaya da ya gado a wurin Zaid, amma hatta da buɗar idonsa irin ta Kuliya ce.
Sai kuma ya sauƙo daga kan cinyar Kuliya, ya tako zuwa wurin Rabi, ya ɗan mata wani gutun murmushi yana rungume ƙafafunta.
“Tafi ka bani wuri ba na so”
“Haka fa ni ma suka haɗe mun kai shi da Papi last week, wai dan suna kallon Film ɗin 'Tara Dunken' na zo na sauya, shi kenan suka dena min magan, sai jiya suka kulani”
Cewar Mishal tana aje cup ɗin hannunta.
“Ai ke na sati ɗaya suka miki ma, ni da suka fi sati biyu ba sa kulani fa in ce me?”
Cewar Anna cikin taɓe baki.
“Sorry Mama”
Cewar Junior kamar wanda aka yiwa dole.
Rabi ta dunguri kansa tana faɗin.
“Ka dena wannan miskilancin naka, idan ka ce irin halin Papi za ka ɗauko wahala za ka sha, don ma de shi Papi an yi nasarar samun Nini ta seta masa hanya, kai ko sai de ka ci jibga, don dukanka zan fara...”
Shi dai bai ce mata komai ba, sai ƙasan kimonohnta da ya riƙe.
“Nini?
Ashe ke kika seta ni?”
Kuliya ya tambaya yana kallon Mishal, ita ko tai masa banza, don ta san idan ta biyashi yanzu sai su zo suna cece ku ce, ita kuwa yanzu a duniyar Allahn nan magana ita ce abun da ke mata wuya, ba ta son yawan magana.
“Sai ku zo mu fara cin abin cin”
Cewar Anna.
“Bari na je na yi wanka tukunna”
Rabi ta faɗi tana ƙwace ƙasan kimonohnta daga hannun Junior.
Kafin ta haye sama.
Bayan ɗan wani lokaci Zaid ma ya miƙe ya bita.
Kuliya ya ci gaba da tsokanar Mishal, amma ko ci kanka ba ta ce masa ba, har sai da Anna ta masa magana kafin ya shafa mata lafiya.
“Ammatan Raj”
Zaid ya kira sunanta, yayin da take tsaye a jikin mirror tana shafa mai, juyowa ta yi ta kalleshi, shi ma kuma kallon nata yake, yayin da yake tsaye a bayanta.
“Kai wai baka san ka girma ba ne?”
Ta tambaya tana juyawa.
“Girman me?, ɗa ɗaya ne fa da mu kawai, ki bari sai mun tara kamar yara goma haka, sai ki ce na girma, amma ɗa ɗaya ai ya yi kaɗan ya sa na ga tsufana”
Rabi ta yi murmushi tana shafa mai a wuyanta.
“Saura kwana nawa ku tafi ne?”
Ya tambaya yana zuge mata zip ɗin rigarta da bata zuge ba.
Rabi na kallonsa ta cin madubin gabanta ta furta.
“One week”
“Mun gode Allah, dan nan da kwana uku visar mu na iya fitowa”
Sai ta gyaɗa masa kai tana juyowa.
“Mu je ko?”
Ya girgiza mata kai yana kama waist ɗinta.
Rabi ta ture shi tana faɗin.
“Su Anna na ƙasa suna jiranmu fa”
Ya ƙara kamota yana faɗin.
”To ina ruwana...”
“Dady!
Mama!”
Muryar Junior ta kira daga wajen ɗakin.
Rabi ta ƙara tureshi tana nufar ƙofar da sauri, sai ta ga Junior ɗin tsaye a waje yana kallonta.
“Me ya faru?”
“Anna tace wai ku yi sauri”
Rabi ta juyo ta kalli Zaid tana watsa masa hararar wasa, kafin ta juyo ta tsugunna ta ɗauki Junior ta sauƙa ƙasa, Zaid ya bi bayansu da kalli yana murmushi, kafin shi ma ya bi bayan nasu ya sauƙa aka fara cin abincin da shi.
Labarin rayuwar sabon gidan da suka gina cike da so ƙaunar juna da farin ciki kenan.
°°°°°°Alhamdullullah°°°°°°
••••••END••••••
-Assalamualaikum-
Barkan mu da wannan lokaci, ina so na yi amfani da wannan damar, wurin nuna muku irin godiyata gareku, kan so da ƙaunar da kuka nuna min, a har kullum ina ganin kamar ‘Na gode' ta yi kaɗan wurin nuna muku jin daɗi na game da yanda kuke support ɗina, my people i can't thank you enough.
Allah ya bar zumunci.
Sannan ina so na yi jan hankali gareku, game da darasin dake cikin wannan littafi.
Idan kuka tsaya kuka yi nazari, za ku ga cewar wannan littafin na ƙunshe da illollin fyaɗe, da kuma yanda rayuwar 'ya mace kan shiga garari yayin da iyayenta suka koreta daga gida, bacin da ƙaddara fyaɗe ta faɗa kanta.
Kun sani, kuma ni ma na sani, fyaɗe ita ce babbar annobar da ta damu yankin mu na arewa gaba ɗaya, shi ya sa nake so, mu tashe tsaye ni da ku, mu haɗa ƙarfi da ƙarfe, wurin ganin mun kawo ƙarshen wannan annoba, domin fyaɗe masifa ne, kuma bala'ine.
Ina kira ga duk wani wanda ya san Allah ya wadata shi da wata baiwa, da ya yi anfani da wannan baiwar tasa wurin ganin mun kawo ƙarshen fyaɗe a arewacin nigeria, idan zai iyu, a gaba ɗayan Nigeria ma.
Ni tawa baiwar ta rubutu ce, shi ya sa na yi amfani da shi, wurin ganin na yaƙi wannan annoba da ta damu sauran 'yan uwana mata.
Jama'a mu ƙyamaci fyaɗe.
*Say No to Rape❌*
#Labarinsu
#SalmaAhmadIsah
#TaurariWriters
Best regards
SALMA AHMAD ISAH
2024...