← Book details Labarinsu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 80

Sashe 6

Labarinsu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sannan ta juya kanta kaɗan, ba tare da ta kalli bayanta ba, idonta a kan matashin ta kira sunan na cikin motar.

“RAJA!”
A hankali mutumin cikin motar ya buɗe idonsa dake rufe, kafin ya sauƙe kansa, idonsa ya sauƙa a kan mutanen dake gaban motar tasu, ɗan guntun tsaki ya ja.

Sannan ya buɗe ƙofar motar ya fito.

Hannunsa kan ƙofar motar ya ci gaba da kallonsu.

Kafaɗarsa ta dama ya ɗaga, sannan ya kai hannu ya sodai tattoo ɗin kan zakin dake bayan wuyansa, ya fara takawa zuwa wajen da suke tsaye.A gaban matashin ya ja ya tsaya.

“Ka bamu kayan za mu juya”
Muryarsa me cike da kamala da kuma nutsuwa ta furta, idan ka ji muryarsa ba tare da ka ganshi ba sai ka rantse da Allah ba daga bakinsa ta futo ba, dan sam yanayinsa baya kama da yanayin muryar tasa.

“Sai kun bamu kuɗi tukkuna“
Raja ya kuma yin guntun tsaki, ya ɗaga kafaɗarsa ta dama.

“Kana ji ko bana san jayyaya, sannan nakan jima banyi fushi ba, ka bamu kawai mu juya”
Wannan karon muryar tasa cikin wani irin taushi ta fito.

“Ni ma ba na san jayyaya.....”
Bai ko gama rufe bakinsa ba, Raja ya ɗauke shi da mari, sannan ya ci kwalarsa da hannunsa na dama, tare da zaro bindigarsa da hannunsa na hagu, ya ɗorata a kan matashin.

Yaron dake tsaye a bayan matashin ya fiddo da tasa bindigar ya nuna Raja da ita, yayin da mutanen Rajan ma suka fiddo da tasu bingidar.

Matashin ya shiga ƙoƙarin motsa bakinsa cike da tsoro.

“Shhhhh!”
Rajan ya faɗi yana ɗauke bindigar daga kan matashin, tare da ɗora bindigar a bakinsa, alamun ya masa shiru.

“Ba na san jayyayya!......”
Ya ƙarshe yana maido da bindigar kan matashin, cike da tsoro matashin ya gyaɗa kansa, sannan ya yi wa mutuminsa alama da ya basu kayan.

Da sauri mutumin ya juya cikin motarsu ya buɗeta, sannan ya ɗuko wani brief case, ya danƙa a hannun macan nan, ita kuma macen ta miƙawa ɗaya daga cikun mazan dake tsaye a bayata.

Kuma har zuwa lokacin Raja na riƙe da kwalar matshin nan, sannan bindigar Rajan sete a gosbinsa.

Sai da mutumin su Rajan ya buɗe brief case ɗin, ya tabbatar musu da sahihancin abin da ke cikin brief case ɗin, sannan Raja ya saki matashin.

Kafaɗarsa ta dama ya ɗaga, sannan ya maida bindigar bayansa, yana kallon matashin da shanyyayun idanuwansa, hannunsa ya kai yana gyarawa matshin kwalar rigar jikinsa.

Da farko saida matshin ya razana, ya ɗauka cewar wuya zai shaƙe masa.

Kuma har lokacin cike da tsoro yake kallonsa.

“You are such a good boy, ka kyauta, da ka yi abinda na ce”
Kuma daga haka ya juya.

Da hannu ya yi wa yaransa alama da su shiga mota.

Har motar tasu ta bar wurin matashin na tsaye a wurin yana kallonsu, a ransa yake hasaso irin masifar da ogansa zai masa idan har yasan cewa ya basu kayan ba tare da sun bashi kuɗi ba.
*Unguwar Karkasara....*
*12:30am*
“Da kyau Raja!”
Cewar Garuje, wanda yake shugaba a wurin Rajan, yana faɗin hakan tare da bubbuga kafaɗar Rajan.

Bayan da ya duba kayan da ya aikasu su karɓo masa.

Raja ya yi murmushi yana ɗaga kafaɗarsa ta dama.

“Ka ga yanzu nan muka gama waya da me gida, yana ta tambayata akan kayan....”
Garujen ya kuma faɗa.

Kuma yanzun ma Rajan bai ce masa komai ba, sai juyawa da ya yi ya kalli yaransa huɗu dake tsaye a bayansa,Rhoda, ta hannun damansa kenan, sai Zuzu, Alandi da kuma Jagwado.

Sannan ya juyo ya kalli Garuje, a hankali cikin nutsuwarsa wannan kamillaliyar muryar tasa tace.

“Kai ma ka sanni ai”
“Ai dole ne ma na sa me gida ya maka kyauta, sbd wannan ƙwazon da ka nuna”
Lumsassun idanuwansa na ci gaba da kallon Garuje, yayinda ya ɗaga kafaɗarsa ta dama.
*No. 213, Naf Belly Estate, Asokoro, Abuja*
KULIYA POV.

Har zuwa yanzu a idonsa yana ganin abinda ya faru a ɗazu, ɗazun da ya buɗe ƙofar kai tsaye wuta ya buɗe musu.

Bai ankara ba ashe wani daga cikinsu yana riƙe da bindiga, kuma shi ne ya yi yunƙurin harbinsa.

Sai de cikin ikon Allah sai ya bashi damar kaucewa, bullet ɗin ya samu bango.

Kuma bayan ya juya ta kalli bangon da bullet ɗi ya fasa, juyowa ya yi ya kalli yaron da hannunsa ke karkarwa, kuma bai jira komai ba, ya riƙe gaban rigar yaron, ya shiga dukansa da hannunsa, har saida yaransa suka shigo sannan suka raba shi da shi......

“Yau ma halin aka sake?....”
Muryar Wata dattijuwar mata ta dawo da shi zahiri.

Hannunsa na dama ya sauƙe daga kan bakinsa, kafin ya ɗaga kafaɗarsa ta dama.

Bai cewa matar komai ba, har ta samu wuri ta zauna kusa da shi, matar ta ci gaba da kallonsa tana nazarinsa.

Kamar kullum, kamar yanda ya taso a wurinta, kamar yadda ta rene shi, sanye yake cikin baƙaƙen kaya, wasu jogger set ne sanye a jikin nasa, ya rufe kansa da hular hoodie ɗin rigar.

Idonta ya sauƙa a kan hannunsa na dama, rauni ta gani, kuma da ma ɗazu tun da taga labarai, ta ji an sanar da cewa hukumar DSS sun yi kame a wani gida, har sun kashe mutum ɗaya, ta tabbatar da shi a cikin aikin.

Dan yanda tasan Kuliya, haka ta san yunwar cikinta, bata jin akwai wani da zai faɗa mafa halayensa.

Hannun nasa ya farfashe daga kan yatsunsa, alamun dai ya daki wani abun da shi.

Kanta ta girgiza sannan ta miƙe ta bar falon.

Jim kaɗan sai gata ta dawo, hannunta riƙe da plate ɗin abinci, sanna firstaid box.

A kan coffe table ta aje masa abincin, sannan ta ɗauki firstaid box ɗin ta ɗora akan cinyarta kafin ta buɗe.

Hannun nasa na dama ta kama sannan ta shiga shafa masa maganin zafi a wurin.

Kafaɗarsa ta dama ya ɗaga yana kallonta.

A duk sanda Anna zata nuna masa kulawa, idan ya kalleta sai ya ga fuskarta na rikiɗewa tana koma irin tata.

Mahaifiyarsa, mahaifiyarsa da a duk sanda zai tuna da ita sai ya tuna da mahaɗinsa, ɗan uwansa, abokin tagwaitakarsa, Zaid ɗinsa, Zaid ɗin da ya ƙara sunansa a gaban nasa sunan, sai dai kuma idan ya ci gaba da san zurfafa a cikin tunanin LABARINSU na baya zuciyarsa ƙuna take, wani abu ne ke maƙale masa a wuya, shi bai faɗa cikinsa ba shi bai fito daga bakinsa ba.

“Ga abinci ka ci”
Anna ta faɗi a sanda ta gama shafa masa maganin,tana miƙa masa plate ɗin.

Yanda yake kaiwa lomar abincin ne kawai ya shaida mata da kalar yunwar da yake ji, bisa ga dukkan alamu ko da aka yi buɗa baki bai ci abinci bw.

Masifar zurfin cikinsa da miskilancinsa da kuma taurin kansa shi ne ke haɗata faɗa da shi, dan da ace bata kawo masa abincin ba, haka zai ƙaraci zamansa a gidan, har ya tashi ya tafi ba tare da ya ce ta bashi abincin ba, alhalin shi ne wanda ya siyo kayan abincin.

Kuma bama iyaka kayan abinci ba, komai ma na gidan shi ne ya siya.

“Aliyu!”
Ta kira sunansa a hankali, shi ma kuma sai ya saki spoon ɗin hannunsa ya juyo ya kalleta.

“Dan Allah ka rage yawan fushin nan, ka rage wannan zafin zuciyar taka”
“Anna ba na iya controlling kai na, as far as zan ga ana aikata laifi bana iya hana kaina ɗaukar mataki!......”
A karo na biyu ya yi magana tun bayan zuwasan gidan, tun da ya gaisheta cikin jimla ɗaya bai sake cewa komai ba sai yanzu.

“Haka ne, amma ya kamata a ce kana ragewa, ka riƙa sanyaya zuciyarka, Aliyu babu macen da zata aureka da wannan halin naka”
Ransa ya soma ɓaci, ita Anna ana gabar tana yamma, shi ya faɗa mata cewa zai yi aure ?, shi fa sam babu aure a lissafinsa, bai shirya masa ba, kuma baya jin zai shirya masa ko a nan gaba.

Sai dai ban san abinda Allah ya ƙaddaro ba, bai san ƙaddara da zata kasance ƴan kwanaki ƙalilan ba, ƙaddarar da Allah ya hukunta zata faru a 'yan kwanaki masu zuwan.

Wata iriyar ƙaddara ce da zata tarwatsa komai, sannan ta zama silar shiryiwar wasu lamura.

“Ni na faɗa miki cewar aure nake san yi ?!”
Annan ta yi murmushi, jin muryar tasa na fita a zafafe, ko bai buɗe baki ya faɗa mata ba tasan cewa ransa ne ya ɓaci.

Kuma shi da ma haka yake, abu ɗan ƙalilan ne ke ɓata masa rai.

Kuliya ya ɗaga kafaɗarsa ta dama yana ƙoƙarin saita kansa, dan sai bayan muryar tasa ta fito ne ya fuskanci abinda ya yi.

“Sorry Anna, zancen auren ne bana so”
Har a lokacin Anna na iya tsintar sauran fishin da bai gama sauƙe shi ba, kuma da ma shi haka muryar tasa take, kullum cikin darari, ba'a iya maganar arziƙi da shi ta minti goma, kullum idanuwansa a waje kamar me zarewa mutane su.

“Aure shi ne cikar kamala Aliyu, duk wannan muƙamin naka, da dukiyar da ka tara, da wannan shekarun naka, ba zasu baka kimar da aure zai baka ba!....”
Bai ƙara kallonta ba, bare ya amsata, dan ya lura da yau so take suyi faɗa.

TALLAH!

Salma's Graphics:
•Muna haɗa book cover.
•Banner
•poster
Kuma duka a kan ₦ 300 kacal.

Domin neman ƙarin bayani: 08130172702.
#Labarinsu
#SalmaAhmadIsah
#TaurariWriters
°°°°°°°°°°°°°
*LABARINSU*
*© SALMA AHMAD ISAH*
*TAURARI WRITERS*
*03*
~~~
_-*If it doesn't set your soul feel free, then it isn't love...*-_
***
*No.234, Efab Estate, Gwarinfa, Abuja*
*07:30am*
“An ya kuwa kina ganin abun nan zai iyu ?, jiya fa ba kiga irin faɗan da muka yi da shi ba, wai ka wai dan na mata faɗa, sai ciwonta ya tashi, ko a ɗakina ma bai kwana ba.....”
Muryar Hajjara ta faɗi ta cikin wayar da take da ƙawarta Fati.

Tsaye take a jikin wardrobe, yayin da hannunta na dama ke riƙe da murfin wardrobe ɗin, na hagun kuma riƙe da wayar da take.
Chapter 6 · 0% Book details