← Book details Ja Ya Fado Ja Ya Dauka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 77 OF 101

Sashe 77

Ja Ya Fado Ja Ya Dauka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Washegari barcin gajiya na kwanta yi don gaskiya akwai gajiya a jikin mu lokacin can cikin barcin nake jin muryan matar nan ta yaya Habib da yarta a dakina. Su din ne suna zaune a dakin suna hiran abinda ya faru da Aimana da kyar na samu na bude idona ina mika tare da sakar masu murmushi ina fadin anty har kun shigo ashe ? Mun shigo tun dazun shine nacewa mummy inane gidan ku tasa yaro ya kawoni yarta Amira nata faman ce main good morning. Muna magana da uwarta sai daga baya na fahinci me take fadi na jawota ina mikewa tare da amsawa kafin na samu nakai zaune na mike gaba daya saman gadon. Bakin mirro naje na dauki brush na matsa marclean na fita ban jima ba na dawo tana zaune da wani littafina a hannu tana karantawa nadawo. Zama nayi saman Stoll din bakin mirror din yarinyar still tazo ta hau saman jikina kai Amira aka take fa kamar mage da son jiki uwar ta fada. Nace ai haka yara suke a zuciyana kuma ina faman mamakin zuwansu gidan mune haka kafin Aimana data fita ta dawo da kwano a hannu ta zauna wait waina ta fita ta sayo wajen wani mutumi dake suya can dan nisa damu kadan. Ganin yadda yarinyar ta tsura mata ido itako ko kallonta batayi ba yasa na shafa kanta ina fadin Amira zakici waina din he bari Asmau ta sayo maku kuci da mummy ko ? Nan uwar ta dago kai tana fadin ayya kyaleta ba zataci ba yanzu tea din da mummy ta hada munama bata sha ba nan ta barshi muka fito. Zancen mu baisa Aimana ta kira yarinyar ta bata koda dayane ba taci gaba da cin abinta tana kallon wayanta kamar bata san me muke fada ba a lokacin . Fits nayi da yarinyar wajen Ammah na karbi kudi na tura Asmau ta sayo muna nayi mata bayanin yadda zata sayo din ta fita muka koma dakin tsike banyan kai na dauko na fara banyewa yarinyar kai batayi gardama ba muna hira jefi jefi da uwar har Asmau din ta dawo. Ta aje ta koma ta dauko plate biyo ta girke da gorunan kunnun zaki da zobo duk ta aje muna a gefe days zata fita nake fadin Asmau dauko Abu ki diba a raba wanan ai yayi muna yawa. Nayi mamakin yadda suka zauna sukaci sosai ita da yar bayan sun gama na kwashewa yar kai kalaba mai three in one nayi mata sun kwanta da kyau kafin naje nayi wanka na fito na shirya muka garzaya gidan bukin. Don ranace daurin sure kowa kuma daga ranan zai kama gabansa don kwasan gara ya kare ga mutane yadda aketa dora tukwane ake saukewa akuma ce abinci bai isa ba. Muna shiga kiran S matazun yana shigowa wayana dole na dauka da har yasa mukai dakin umma ina kan waya a lokacin . Tana zaune da yaranta maza da gani dai akwai zancen da sukeyi ko kuma sun gama yayin da a waya nake sauraron S matazun dake min mita akan yayi expecting din kirana ko don inji yaya ya tashi da kwana. Abin mamaki ya bani matuka amma a fili ce masa nayi bansan ana hakan ba ai da nayi sai naji ya kwashe da dariya. Yana fadin you are right tunda ni ba bakonki bane a yanzu kada ki damu with time zaki san hakan ai don da zaran kin zamo tawa ni kadai zaki soma. Uhmm kawai nace nan yake fada min yanzu ya tashi shima yana son ya shiga wanka sai ya karya before suzo daurin aure dama don yaji yaya na tashi ya samu natsuwa yasa ya neme ni a yanzu and yaji ya samu piece a zuciyarshi kuma. Zai neme no zuwa anjima idan yafito a hankali nace dashi naji na kuma gode da kulawan shi gareni mukai sallama na kashe wayar. A hankali na dago kai ina gaidasu da kwana yaya salis ne ya fara amsa min da fadin Aisha ashe yau ke aka kaiwa rigima naji matar yaya Habib na fadin D Aysha gaida ku fa ? Ya dan juyo yana fadin ta gama wayan natane tashigo tana muna soyayya a gaban mu haka dama sau kusan biyu muna hada ido dashi a lokacin ina kawarwa don kallon tsana da naga yana min a lokacin. Mikewa nayi ina fadin anty barin leka yan matan can in dawo ina fita take fadin babu ruwanta ga son mutane wallahi. Umma dake duke tana daukan abu a bayan kujeranta tace wai Aeesha ai haka take babu ruwanta don ma bukin nan ne ai inbashi ba bata shiga mutane sosai ita. Wallahi kan mummy tana da hankali sosai yarinyar wa yan nan tsofin suka haifeta kuma ta tambaya hakan yasa umma juyowa tana fadin a,a iyayyenta suna saudiya zaune. Haba nikan nace nayi mamaki wallahi very innocent girl bats da rigima ko kadan haka jiya zamu dawo wani soja ya tareta take fadin ina taga time dinshi ita da take karatu. Gaskiya ne wanan baki taba ganin ta tana hira yaya salis ya fada nan dai sukai ta sharhi akaina har uwar ta fita ta barsu a dakin. Yana zaune cikin mota yana jiran wani abokin aikinsa ya fito daga dogon benen daya shiga wani bincke hakan yasa ya zaro wayansa da rabon ya duba yau kwana biyu ke nan. Saboda wanan bincken mutumin kasan Lebanon din da suke nema ruwa a jallo a yanzu don case dinsa shima babbane don hakane baida lokacin komai. Yana kunna data ya shiga WhatsApp don a nan yafi samun sakon nan abokansa da yan gida wani lokaci tunda sun san bako yaushe yake available bashi. Ya tabbatar da Lukman Dabo dai bukinsa akayi a wanan satin don yadda yake ganin ana yayatawa a ko ina ga yan kanon. Husnan su ce yaga ta dora wasu photo yabi photunan nata da kallo duk da hakan ba dabi,ansa bane saidai yana shiga idonsa yayi arba da photon da ya bashi mamaki su hudune a hoton khairat husna summy kanwarsu sai Aeesha how comes haka ya faru a ina suka hadu sukai wanan photo yaya akayi tasan su husnah din ? A take zuciyarsa ta bashi amsa da khairat that means yanzu yariyar nan tana kawance da khairat ke nan kome ya tambayi kansa ? As how hakan ya faru why take appearing haka garesa yan kwanakin nan wacan a layin ummi yar salman ya gani wanan kuma gun Husnah dinsu . Sannu a hankali yake bin photonan da kallo a wajen buki sukai photon saida ya kusa kai karshe ya gane ai bukin su ummi din ne sukaje suma. A haka abokin aikin nasa Wanda baturene shi ya fito ya sameshi a wajen days barshi yana fada mai inda zasu nufa lokacin kai tsaye suka nufi can din a cikin sauri. Yadai samu yayi aikinsa ranan yadda ya kamata amma yana mai jin wani abu ya tsaya masa a zuciyarshi har lokacin daya kamo hanyar zuwa gidansa. Yana shiga gidan kai tsaye bedroom dinsa ya nufa ya fara cire tufafin jikinsa wanka ya shiga saida ya gurje jikinsa da kyau don wanan dabi,ansa ne dadewa a wajen wanka. Yana fitowa dan mai ya shafa kafin ya sauko zuwa kasa ya nufi wajen fridge din kitchen kai tsaya cimarsa na gwagwani ya dauko ya bude tare da juyewa cikin wani bowl ya tura a ovon tare da kunna ovon din na dan lokaci. Yana tsaye ya dafa table na dan lokaci tare da duo da kai kamar me tunane a wajen yana zafi ya bashi signal na yakai limits din da yake sonsa yakai. Ya juye ya dauko zuwa falo ya zauna yayi kamar spoons biyu ya aje cokalin don yau abincin ba dadi a bakinsa gefe ya mayar ya dora kafa saman table din yana dan kadawa a hankali cikin sarauta da yake jin ya motsa masa a lokacin abin a ji yake dams sai ya motsa. Kansa ya mayar baya kadan yana cigaba da girgiza kafa kafin ya lumshe idanuwansa yana dan tunane zakice barci ya soma a lokacin in badan kafansa da yake dan motsawa ba kadan zakice barci ya daukesa a hakan da yake. Yakai tsawon mintuna talatin a hakan zaune kafin ya dago yana furzo da iska daga bakinsa don t)unanen nasa na karshe da yazo mass a zuciyarsa. Dan guntun tsoki yaja yana dagowan ya dubi lokaci sha biyu da rabi na daren rana yasan yanzu a can Nageria din ma darene don haka ya sauke ajiyan zuciya don baida halin kiran kowa a lokacin. Haka ya samu ya mike zuwa dakin kwanansa da mai aikinsa ya gyara tsab kafin ya tafi bai kwanta kai tsaye ba saida yayi alwala yazo ya sauke nafila ya jima a zaune kamar yadda ya sabayi duk dare kafin ya kwanta. Dogone man bash karfafa saidai ba irin can din nan ba daidai musali ya dan surka don bai kwaso bakin kanawa haka ba andai bashi tsayi da karfin su wurin launin fata uwarsa ya dauko dukama yaran haka suke donshi din gaure biyune bafulatanin bauchi na usuli bakanon gidi na ainihi sai abin ya zame masa biyu. Gidan Rabakaya ya cika yau da jama aure yaya biyu mace dana miji Allah dai yaiwa aure albarka za ace ina daki kudun dune kamar amaryam danko tunda na koma dakin yan mata ban fito ba . Su maryam sunzo sun samemu a gidan nan muka hade dasu din Allah ya gani ba don saratun nan tayi min rashin mutunci ba dama dai hakana nake na tsani mai baki mara kunya a rayuwata irin fitsaran shashancin nan da ba,aso diya mace dashi haka wanan saratun mai zubin tsohon agwagwa take. Sai ta gama ta fita Anty fati zatace don Allah ku kyaleta ku daina biye mata wai yanzu kuma da wata kawar anty fatin take wa wanab zarin haka. Bata bar kowa ba kamar wace bataso zuwan kowa taron ba haka take bin kowa daya baya daya tana masu cin mutunci wai ita mai baki. Yanzu dai mun mun samu lafiya don tonon asirin su samira bata kulamu ko kuma anyi mata fada akan mune oho mata.
Chapter 77 · 0% Book details