Sashe 7
Hasashe Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Hajiya Talatu ta kira Ma u suka fita waje, ta Kalle ta tace, Allah ya sa aikin nan bai baci ba, dan Malam bai ce mana zai yi jinya ba. Ma u tace "Ki kirashi mana, shi malamin." Uwar tace sai dai in tafi gobe kinsan na Shuri baya son daga waya a tsakiyar wata sai farko ko karshe. Ma u tace "To Wai saboda me?" Uwar tace Aljanu sun hana, Ma u kin kuwa binne layun nan? Tace " Tun yaushe Mama nifa yanzu jiran sakamako nake yi zuwa gobe. Tace to Bari mugani in ta kama sai na koma Shurin gobe zance zani Rimin kebe ko Wudil sai kawai in koma Zariya in tafi shuri. Ki koma ki kwanta kar waccan anamimiyar yarinya ta farka.
Hafsi dake labe ta girgiza kai bayan taji komai domin lokacin da Uwar ta zo ta tashi yar Hafsi ba bacci take yi ba tana chatin ne a cikin bargo da saurayin ta.
Biyun dare su Anty da Dady suka dawo Bros Adamu aka kira ya kwana gurin sa. Hafsi tana jin shigo war mota ta fita da sauri ta fara tambayar iyayenta jikin uncle Halifa. Suka ce mata da sau ki Sannan ta ja Anty gefe ta rattafa mata komai game da abinda taji. Tace banyi mamaki ba, domin na san ruwa baya tsami banza, matar nan da shirin ta ta zo. Shike nan kici gaba da samun ido sosai a kan duk wani motsin su.
Tana shiga dakinta Hajiya Talatu ta baje tana bacci sai uban minshari ta ke saki, Anty ta harare ta ta ja tsaki Sannan ta wuce bandaki.
Asiya ta ji waya tana ringing ga zaton ta shine duk da taga an rubuta favorite ba Wai ta iya waya bane, ta san dai koren shine dagawa.
Ta daga da sallama cikin wata muryar da bata san tana da ita ba. Sai taji an katse ta da cewa "Ke wacece ke? Ta ce ni ce Asiya ki kira daya layin nasa. Bilkisu ta yi shiru ko zata tuna mai irin sunan a dangin su Halifa. Rashin tunawa ya sa ta danja tsaki tare da sake fadin " Ke yanzu me ya kawo wayarsa gurin ki.?" Asiya ta danyi jim tana tunanin ko yan gidansu ne. Bilkisu ta katse ta da fadin cewa "Ni matar sa ce ina miki magana kin min banza." Wani abu Asiya taji ya daki kirjinta matarsa kuma. Ta sauke ajiyar zuciya tace A iya sanina ni ce matar sa domin ya biya sadaki na, ko da yake ki kirashi ta daya layin kinga sai da safe. Asiya ta kashe cike da tashin hankali.
Cikin dare Halifa ya farka bayan ya yi wani mummunan mafarki, Bros Adam ya gani yana zaune kan kujera ya kifa kai a jikin gado. Jin motsin shi sai shima Bros din ya farka. Ya yi masa ya jiki, ya amsa da sauki. Yace jiya naji zuwan ka ashe baka tafi ba bacci ya dauke ni. Bros yace "Ni ai mamaki naji kai da baka fiye yin ko zazzabi ba. ". Halifa yace Aii gara a dan dinga taba mu muma abin ne ya zo ba zato Allah ya kara mana lafiya. Kai kwana biyu bamu hadu ba, tunda aka soma hatsaniyar bikin nan ban ganka ba. Bros Yace "Munyi sabani na zo Anty take min korafin abinda ya faru, to bance komai ba domin kun fi kusa." Halifa yace au Haka ma zaka ce? "To me kake so ince Uncle Halifa, nan ka goyi bayan Anty aka wai dole saina saki mata ta, ina sonta yaran mu biyu amma aka kasa min uzri." Halifa yace Bros kaga dai Anty Yayata ce kai ta haifa ba ni ba ko? To mace ko yar uban waye zan iya sakin ta matsawar ta zagi Anty kamar yadda aka ce matar ka ta yi.
Bros yace to ba komai ai gobe saurin zuwa gareta, baga dai auren zaka yi ba, Allah ya kade fitina. Yanzu bikin yana nan a lahadi din?" Halifa yace ameen. Yana nan insha Allah Wai kuwa ina wayata? Sai ya tuna ya ba Asiya sai karamar dake kusa da shi, yasan yanzu tana bacci ya dakko kirane Kala kala. Bros yace jiya har zan shigo kasuwar ku in duba wa Maman Nihal waya bakin kwastomomin mu na nijar ba su tafi da wuri ba. Halifa ya Kalle shi " Wai kai duk da kun Rabun da kyar Amma har hanzu kuna tare? Bros yace " Nifa na maida mata ta kuma tuni na kama mata haya yanzu ma cikin ta ya kai wata biyar."
Halifa ya tashi zaune har yana yarda karfen dake dauke da ruwan da ake kara masa, Nus ta shigo da sauri tana ta bayar lafiya? Ta taimaka masa yace ta cire ruwan haka ya isa tun jiya ake dura min ruwan nan. Tace ka yi hakuri ya karasa, kafin ta rufe baki ya tuge allurar karin ruwan ya rataye, jini ya biyo baya. Bros yace kalli to abinda ka yi Uncle. Ya dafe masa gurin da yatsa. Ta kawo auduga ya manna ya dafe. Bros yace "Kai Uncle dan Allah ka rage wannan dabi ar mana ace shi mutum komai sai yadda yake so harda lafiyar taka ma sai ka yi wasa?". Halifa yace Amma dai Anty bata San ka dawo da matar ka ba. Bros yace "Sai dai ko in kaine zaka fada mata yanzu. " Halifa yace ai da kasan zan fada din baza ka fada min ba, amma ina tausaya maka duk radda ta sani. Bros yace Matata fa bata zagi Anty ba kawai Anty ta raina arzikin sune kamar yadda na yi ta kokarin fahimtar da kai, kuma wai ita ce ta yi silar karayar arzikina wanda kasan I yan damfarane ba kuma ni ka sai suka cuta a kwariba har Anty tana tutiyar wai yanzu da muka rabu gashi komai nawa ya dawo, bata san muna tare ba. Ta amshe Nihal da Nur a gurinta.
Halifa yace Kabi a hankali mahaifiyar ka ce ka samu ku rabu lafiya. Amma ina jiye maka radda ta sani to yanzu ya maganar auren da take nema maka? Bros yace "Ni dai ba ina bita da to ba. " Halifa ya yi dariya shiyasa muka matsa ka dawo gida ka ki yarda?
Bros yace Kai Anty in ta sako mutum a gaba sai Allah, harfa zuwan bazata take tayi akai akai gidana kamar tana zargin zata samu Aisha a gidan lokacin ma ban samu gida ba muna Hotel ai wannan cikin a Hotel muka yi shi, gidansu fa basu da labarin wani saki, kai Bari ma dai in bude ka a mutum lokacin da Anty ta matsa ta tsaya gaba na ita da wannan shedaniyar kawar ta ta ta Zariya wai in rubuta takarda a take in bawa Aisha a jikin takarta na rubuta cewa taje ta jirani a can wani kebabben guri za muyi waya. Ina bata ta karanta sai ta hau kukan murna su kuma sun zata saki ne suka kwashe yara suka wuce. Tun a ranar naje na kama mana Hotel na kai mata kayan ta ni kuma sai da safe nake zuwa inyi shirin kasuwa lokacin ne take zuwa Wai ta duba ko ta dawo Shine kai kuma ka bullo da zance wai in koma gida. Na ce kaji Uncle zai ha wata fitina. Lokacin kam na kashe kudin abinci ma ka dai ba sauki. Da Anty ta matsa su zo su kwashe Kaya sai na kama gida muka bi dare muka kwashe. " Cike da mamaki Halifa ke Kallon Bros. Yace to wace Unguwar kuka koma? Bros yace Kuntau na samu wani gida mai kyau" . Halifa ya numfasa. To Allah ya kawo abin da sauki, ina jinjinawa ace Anty ta samu labarin nan.
Bros yace kullum ina adduo'in Allah ya fahimtar da Anty gaskiya wannan kawayen nata su ke zugata. " Halifa yace jiya ai na kusa doke yarinyar kawarta ta Zariya din nan kawai ta fesa min wani abu wai murnar biki. Tun abine fa har yanzu bana gane kaina so sai wallahi Bros. Bros yace dama ka doke ta wallahi Allah ya sa ba wani mugun asirin na su bane suka fesa maka. " Halifa yace Sai sun jira, asiri su zai ci su da suka yarda da masu yin shi, ni ina tare da kariyar Allah ko da yau she bana wasa da azkar kaga kuwa sai dai wata kaddara. Sunata hira sai kiran salla suka ji.
Hafsi dake labe ta girgiza kai bayan taji komai domin lokacin da Uwar ta zo ta tashi yar Hafsi ba bacci take yi ba tana chatin ne a cikin bargo da saurayin ta.
Biyun dare su Anty da Dady suka dawo Bros Adamu aka kira ya kwana gurin sa. Hafsi tana jin shigo war mota ta fita da sauri ta fara tambayar iyayenta jikin uncle Halifa. Suka ce mata da sau ki Sannan ta ja Anty gefe ta rattafa mata komai game da abinda taji. Tace banyi mamaki ba, domin na san ruwa baya tsami banza, matar nan da shirin ta ta zo. Shike nan kici gaba da samun ido sosai a kan duk wani motsin su.
Tana shiga dakinta Hajiya Talatu ta baje tana bacci sai uban minshari ta ke saki, Anty ta harare ta ta ja tsaki Sannan ta wuce bandaki.
Asiya ta ji waya tana ringing ga zaton ta shine duk da taga an rubuta favorite ba Wai ta iya waya bane, ta san dai koren shine dagawa.
Ta daga da sallama cikin wata muryar da bata san tana da ita ba. Sai taji an katse ta da cewa "Ke wacece ke? Ta ce ni ce Asiya ki kira daya layin nasa. Bilkisu ta yi shiru ko zata tuna mai irin sunan a dangin su Halifa. Rashin tunawa ya sa ta danja tsaki tare da sake fadin " Ke yanzu me ya kawo wayarsa gurin ki.?" Asiya ta danyi jim tana tunanin ko yan gidansu ne. Bilkisu ta katse ta da fadin cewa "Ni matar sa ce ina miki magana kin min banza." Wani abu Asiya taji ya daki kirjinta matarsa kuma. Ta sauke ajiyar zuciya tace A iya sanina ni ce matar sa domin ya biya sadaki na, ko da yake ki kirashi ta daya layin kinga sai da safe. Asiya ta kashe cike da tashin hankali.
Cikin dare Halifa ya farka bayan ya yi wani mummunan mafarki, Bros Adam ya gani yana zaune kan kujera ya kifa kai a jikin gado. Jin motsin shi sai shima Bros din ya farka. Ya yi masa ya jiki, ya amsa da sauki. Yace jiya naji zuwan ka ashe baka tafi ba bacci ya dauke ni. Bros yace "Ni ai mamaki naji kai da baka fiye yin ko zazzabi ba. ". Halifa yace Aii gara a dan dinga taba mu muma abin ne ya zo ba zato Allah ya kara mana lafiya. Kai kwana biyu bamu hadu ba, tunda aka soma hatsaniyar bikin nan ban ganka ba. Bros Yace "Munyi sabani na zo Anty take min korafin abinda ya faru, to bance komai ba domin kun fi kusa." Halifa yace au Haka ma zaka ce? "To me kake so ince Uncle Halifa, nan ka goyi bayan Anty aka wai dole saina saki mata ta, ina sonta yaran mu biyu amma aka kasa min uzri." Halifa yace Bros kaga dai Anty Yayata ce kai ta haifa ba ni ba ko? To mace ko yar uban waye zan iya sakin ta matsawar ta zagi Anty kamar yadda aka ce matar ka ta yi.
Bros yace to ba komai ai gobe saurin zuwa gareta, baga dai auren zaka yi ba, Allah ya kade fitina. Yanzu bikin yana nan a lahadi din?" Halifa yace ameen. Yana nan insha Allah Wai kuwa ina wayata? Sai ya tuna ya ba Asiya sai karamar dake kusa da shi, yasan yanzu tana bacci ya dakko kirane Kala kala. Bros yace jiya har zan shigo kasuwar ku in duba wa Maman Nihal waya bakin kwastomomin mu na nijar ba su tafi da wuri ba. Halifa ya Kalle shi " Wai kai duk da kun Rabun da kyar Amma har hanzu kuna tare? Bros yace " Nifa na maida mata ta kuma tuni na kama mata haya yanzu ma cikin ta ya kai wata biyar."
Halifa ya tashi zaune har yana yarda karfen dake dauke da ruwan da ake kara masa, Nus ta shigo da sauri tana ta bayar lafiya? Ta taimaka masa yace ta cire ruwan haka ya isa tun jiya ake dura min ruwan nan. Tace ka yi hakuri ya karasa, kafin ta rufe baki ya tuge allurar karin ruwan ya rataye, jini ya biyo baya. Bros yace kalli to abinda ka yi Uncle. Ya dafe masa gurin da yatsa. Ta kawo auduga ya manna ya dafe. Bros yace "Kai Uncle dan Allah ka rage wannan dabi ar mana ace shi mutum komai sai yadda yake so harda lafiyar taka ma sai ka yi wasa?". Halifa yace Amma dai Anty bata San ka dawo da matar ka ba. Bros yace "Sai dai ko in kaine zaka fada mata yanzu. " Halifa yace ai da kasan zan fada din baza ka fada min ba, amma ina tausaya maka duk radda ta sani. Bros yace Matata fa bata zagi Anty ba kawai Anty ta raina arzikin sune kamar yadda na yi ta kokarin fahimtar da kai, kuma wai ita ce ta yi silar karayar arzikina wanda kasan I yan damfarane ba kuma ni ka sai suka cuta a kwariba har Anty tana tutiyar wai yanzu da muka rabu gashi komai nawa ya dawo, bata san muna tare ba. Ta amshe Nihal da Nur a gurinta.
Halifa yace Kabi a hankali mahaifiyar ka ce ka samu ku rabu lafiya. Amma ina jiye maka radda ta sani to yanzu ya maganar auren da take nema maka? Bros yace "Ni dai ba ina bita da to ba. " Halifa ya yi dariya shiyasa muka matsa ka dawo gida ka ki yarda?
Bros yace Kai Anty in ta sako mutum a gaba sai Allah, harfa zuwan bazata take tayi akai akai gidana kamar tana zargin zata samu Aisha a gidan lokacin ma ban samu gida ba muna Hotel ai wannan cikin a Hotel muka yi shi, gidansu fa basu da labarin wani saki, kai Bari ma dai in bude ka a mutum lokacin da Anty ta matsa ta tsaya gaba na ita da wannan shedaniyar kawar ta ta ta Zariya wai in rubuta takarda a take in bawa Aisha a jikin takarta na rubuta cewa taje ta jirani a can wani kebabben guri za muyi waya. Ina bata ta karanta sai ta hau kukan murna su kuma sun zata saki ne suka kwashe yara suka wuce. Tun a ranar naje na kama mana Hotel na kai mata kayan ta ni kuma sai da safe nake zuwa inyi shirin kasuwa lokacin ne take zuwa Wai ta duba ko ta dawo Shine kai kuma ka bullo da zance wai in koma gida. Na ce kaji Uncle zai ha wata fitina. Lokacin kam na kashe kudin abinci ma ka dai ba sauki. Da Anty ta matsa su zo su kwashe Kaya sai na kama gida muka bi dare muka kwashe. " Cike da mamaki Halifa ke Kallon Bros. Yace to wace Unguwar kuka koma? Bros yace Kuntau na samu wani gida mai kyau" . Halifa ya numfasa. To Allah ya kawo abin da sauki, ina jinjinawa ace Anty ta samu labarin nan.
Bros yace kullum ina adduo'in Allah ya fahimtar da Anty gaskiya wannan kawayen nata su ke zugata. " Halifa yace jiya ai na kusa doke yarinyar kawarta ta Zariya din nan kawai ta fesa min wani abu wai murnar biki. Tun abine fa har yanzu bana gane kaina so sai wallahi Bros. Bros yace dama ka doke ta wallahi Allah ya sa ba wani mugun asirin na su bane suka fesa maka. " Halifa yace Sai sun jira, asiri su zai ci su da suka yarda da masu yin shi, ni ina tare da kariyar Allah ko da yau she bana wasa da azkar kaga kuwa sai dai wata kaddara. Sunata hira sai kiran salla suka ji.